< اشعیا 55 >

«ای جمیع تشنگان نزد آبها بیایید وهمه شما که نقره ندارید بیایید بخرید وبخورید. بیایید و شراب و شیر را بی‌نقره وبی قیمت بخرید. ۱ 1
“Ku zo, dukanku masu jin ƙishi, ku zo wurin ruwaye; ku kuma da ba ku da kuɗi, ku zo, ku saya ku kuma ci! Ku zo, ku saya ruwan inabi da madara ba tare da kuɗi ba ba za ku kuma biya kome ba.
چرا نقره را برای آنچه نان نیست و مشقت خویش را برای آنچه سیرنمی کند صرف می‌کنید. گوش داده، از من بشنویدو چیزهای نیکو را بخورید تا جان شما از فربهی متلذذ شود. ۲ 2
Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba, ku kuma yi wahala a kan abin da ba za ku ƙoshi ba? Ku saurara, ku saurare ni, ku kuma ci abin da yake da kyau, ranku kuma zai ji daɗin abinci mafi kyau.
گوش خود را فرا داشته، نزد من بیایید و تا جان شما زنده گردد بشنوید و من باشما عهد جاودانی یعنی رحمت های امین داود راخواهم بست. ۳ 3
Ku kasa kunne ku kuma zo gare ni; ku saurare ni, don ranku ya rayu. Zan yi madawwamin alkawari da ku, zan nuna muku ƙaunata marar ƙarewa da na yi wa Dawuda alkawari.
اینک من او را برای طوایف شاهدگردانیدم. رئیس و حاکم طوایف. ۴ 4
Duba, na mai da shi shaida ga mutane, shugaba da kuma jagorar mutane.
هان امتی را که نشناخته بودی دعوت خواهی نمود. و امتی که تورا نشناخته بودند نزد تو خواهند دوید. به‌خاطریهوه که خدای تو است و قدوس اسرائیل که تو راتمجید نموده است.» ۵ 5
Tabbatacce za ku kira al’umman da ba ku sani ba, kuma al’umman da ba ku sani ba za su sheƙo a guje zuwa wurinku, saboda Ubangiji Allahnku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya darjanta ku.”
خداوند را مادامی که یافت می‌شود بطلبید ومادامی که نزدیک است او را بخوانید. ۶ 6
Ku nemi Ubangiji tun yana samuwa; ku yi kira gare shi tun yana kusa.
شریر راه خود را و گناه کار افکار خویش را ترک نماید وبسوی خداوند بازگشت کند و بر وی رحمت خواهد نمود و بسوی خدای ما که مغفرت عظیم خواهد کرد. ۷ 7
Bari mugu ya bar irin halinsa mugu kuma ya sāke irin tunaninsa. Bari yă juyo ga Ubangiji, zai kuwa ji tausayinsa, ya juyo ga Allahnmu kuma, gama shi mai gafartawa ne a sauƙaƙe.
زیرا خداوند می‌گوید که افکار من افکار شما نیست و طریق های شما طریق های من نی. ۸ 8
“Gama tunanina ba tunaninku ba ne, yadda kuke yin abubuwa ba yadda nake yin abubuwa ba ne,” in ji Ubangiji.
زیرا چنانکه آسمان از زمین بلندتر است همچنان طریق های من از طریق های شما و افکارمن از افکار شما بلندتر می‌باشد. ۹ 9
“Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, haka yadda nake yin abubuwa suke dabam da yadda kuke yin abubuwa tunanina kuma dabam da naku.
و چنانکه باران و برف از آسمان می‌بارد و به آنجابرنمی گردد بلکه زمین را سیراب کرده، آن را بارورو برومند می‌سازد و برزگر را تخم و خورنده رانان می‌بخشد، ۱۰ 10
Kamar yadda ruwan sama da dusar ƙanƙara suke saukowa daga sama, ba sa komowa ba tare da sun jiƙe duniya sun kuma sa su yi’ya’ya su kuma yi toho, don su ba da iri ga mai shuki da kuma abinci ga mai ci,
همچنان کلام من که از دهانم صادر گردد خواهد بود. نزد من بی‌ثمر نخواهدبرگشت بلکه آنچه را که خواستم بجا خواهدآورد و برای آنچه آن را فرستادم کامران خواهدگردید. ۱۱ 11
haka maganata da take fitowa daga bakina. Ba za tă koma gare ni wofi ba, amma za tă cika abin da nake so ta kuma cika abin da na aike ta tă yi.
زیرا که شما با شادمانی بیرون خواهیدرفت و با سلامتی هدایت خواهید شد. کوهها وتلها در حضور شما به شادی ترنم خواهند نمود وجمیع درختان صحرا دستک خواهند زد. ۱۲ 12
Za ku fita da farin ciki a kuma bi da ku da salama; duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa a gabanku, dukan itatuwan jeji kuma za su tafa hannuwansu.
به‌جای درخت خار صنوبر و به‌جای خس آس خواهد رویید و برای خداوند اسم و آیت جاودانی که منقطع نشود خواهد بود. ۱۳ 13
A maimakon sarƙaƙƙiya, itacen fir ne zai tsiro, a maimakon ƙayayyuwa kuma, itacen ci-zaƙi ne zai tsiro. Wannan zai zama matuni na abin da Ni Ubangiji na yi, madawwamiyar alama ce, wadda ba za a datse ba.”

< اشعیا 55 >