< حزقیال 39 >

«پس تو‌ای پسر انسان درباره جوج نبوت کرده، بگو خداوند یهوه چنین می‌فرماید که اینک‌ای جوج رئیس روش وماشک و توبال من به ضد تو هستم. ۱ 1
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
و تو رابرمی گردانم و رهبری می‌نمایم و تو را از اطراف شمال برآورده، بر کوههای اسرائیل خواهم آورد. ۲ 2
Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
و کمان تو را از دست چپت انداخته، تیرهای تو را از دست راستت خواهم افکند. ۳ 3
Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
وتو و همه افواجت و قوم هایی که همراه تو هستندبر کوههای اسرائیل خواهید افتاد و تو را به هرجنس مرغان شکاری و به حیوانات صحرا به جهت خوراک خواهم داد. ۴ 4
A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
خداوند یهوه می‌گوید که به روی صحرا خواهی افتاد زیرا که من تکلم نموده‌ام. ۵ 5
Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
و آتشی بر ماجوج و بر کسانی که در جزایر به امنیت ساکنند خواهم فرستاد تابدانند که من یهوه هستم. ۶ 6
Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
و نام قدوس خود را درمیان قوم خویش اسرائیل، معروف خواهم ساخت و دیگر نمی گذارم که اسم قدوس من بی‌حرمت شود تا امت‌ها بدانند که من یهوه قدوس اسرائیل می‌باشم. ۷ 7
“‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
اینک خداوند یهوه می‌گوید: آن می‌آید و به وقوع خواهد پیوست. واین همان روز است که درباره‌اش تکلم نموده‌ام. ۸ 8
Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
و ساکنان شهرهای اسرائیل بیرون خواهند آمدو اسلحه یعنی مجن و سپر و کمان و تیرها وچوب دستی و نیزه‌ها را آتش زده، خواهندسوزانید. و مدت هفت سال آتش را به آنها زنده نگاه خواهند داشت. ۹ 9
“‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
و هیزم از صحرا نخواهندآورد و چوب از جنگلها نخواهند برید زیرا که اسلحه‌ها را به آتش خواهند سوزانید. و خداوندیهوه می‌گوید که غارت کنندگان خود را غارت خواهند کرد و تاراج کنندگان خویش را تاراج خواهند نمود. ۱۰ 10
Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
و در آن روز موضعی برای قبردر اسرائیل یعنی وادی عابریم را بطرف مشرق دریا به جوج خواهم داد. و راه عبور کنندگان رامسدود خواهد ساخت. و در آنجا جوج و تمامی جمعیت، او را دفن خواهند کرد و آن را وادی هامون جوج خواهند نامید. ۱۱ 11
“‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
و خاندان اسرائیل مدت هفت ماه ایشان را دفن خواهند کرد تا زمین را طاهر سازند. ۱۲ 12
“‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
و تمامی اهل زمین ایشان رادفن خواهند کرد. و خداوند یهوه می‌گوید: روزتمجید من نیکنامی ایشان خواهد بود. ۱۳ 13
Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
وکسانی را معین خواهند کرد که پیوسته در زمین گردش نمایند. و همراه عبورکنندگان آنانی را که بر روی زمین باقی‌مانده باشند دفن کرده، آن راطاهر سازند. بعد از انقضای هفت ماه آنها راخواهند طلبید. ۱۴ 14
“‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
و عبورکنندگان در زمین گردش خواهند کرد. و اگر کسی استخوان آدمی بیند نشانی نزد آن برپا کند تا دفن کنندگان آن را دروادی هامون جوج مدفون سازند. ۱۵ 15
Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
و اسم شهرنیز هامونه خواهد بود. پس زمین را طاهر خواهندساخت. ۱۶ 16
Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
«و اما تو‌ای پسر انسان! خداوند یهوه چنین می‌فرماید که بهر جنس مرغان و به همه حیوانات صحرا بگو: جمع شوید و بیایید و نزد قربانی من که آن را برای شما ذبح می‌نمایم، فراهم آیید. قربانی عظیمی بر کوههای اسرائیل تا گوشت بخورید و خون بنوشید. ۱۷ 17
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
گوشت جباران راخواهید خورد و خون روسای جهان را خواهیدنوشید. از قوچها و بره‌ها و بزها و گاوها که همه آنها از پرواریهای باشان می‌باشند. ۱۸ 18
Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
و از قربانی من که برای شما ذبح می‌نمایم، پیه خواهید خوردتا سیر شوید و خون خواهید نوشید تا مست شوید. ۱۹ 19
A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
و خداوند یهوه می‌گوید که بر سفره من از اسبان و سواران و جباران و همه مردان جنگی سیر خواهید شد. ۲۰ 20
A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
و من جلال خود را در میان امت‌ها قرار خواهم داد و جمیع امت‌ها داوری مرا که آن را اجرا خواهم داشت و دست مرا که برایشان فرود خواهم آورد، مشاهده خواهند نمود. ۲۱ 21
“Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
و خاندان اسرائیل از آن روز و بعد خواهنددانست که یهوه خدای ایشان من هستم. ۲۲ 22
Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
وامت‌ها خواهند دانست که خاندان اسرائیل به‌سبب گناه خودشان جلای وطن گردیدند. زیراچونکه به من خیانت ورزیدند، من روی خود را ازایشان پوشانیدم و ایشان را به‌دست ستم کاران ایشان تسلیم نمودم که جمیع ایشان به شمشیرافتادند. ۲۳ 23
Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
برحسب نجاسات و تقصیرات ایشان به ایشان عمل نموده، روی خود را از ایشان پوشانیدم.» ۲۴ 24
Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
بنابراین خداوند یهوه چنین می‌گوید: «الان اسیران یعقوب را باز آورده، بر تمامی خاندان اسرائیل رحمت خواهم فرمود و بر اسم قدوس خود غیرت خواهم نمود. ۲۵ 25
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
و حینی که ایشان درزمین خود به امنیت ساکن شوند و ترساننده‌ای نباشد، آنگاه خجالت خود را و خیانتی را که به من ورزیده‌اند متحمل خواهند شد. ۲۶ 26
Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
و چون ایشان را از میان امت‌ها برگردانم و ایشان را از زمین دشمنانشان جمع نمایم، آنگاه در نظر امت های بسیار در ایشان تقدیس خواهم شد. ۲۷ 27
Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
و خواهنددانست که من یهوه خدای ایشان هستم، از آن روکه من ایشان را در میان امت‌ها جلای وطن ساختم و ایشان را به زمین خودشان جمع کردم و بار دیگرکسی را از ایشان در آنجا باقی نخواهم گذاشت. ۲۸ 28
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
و خداوند یهوه می‌گوید که من بار دیگرروی خود را از ایشان نخواهم پوشانید زیراکه روح خویش را بر خاندان اسرائیل خواهم ریخت.» ۲۹ 29
Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< حزقیال 39 >