< حزقیال 38 >

و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت: ۱ 1
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
«ای پسر انسان نظر خود را بر جوج که از زمین ماجوج و رئیس روش و ماشک و توبال است بدار و بر او نبوت نما. ۲ 2
“Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
و بگو خداوند یهوه چنین می‌فرماید: اینک من‌ای جوج رئیس روش و ماشک و توبال به ضد تو هستم. ۳ 3
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
و تو را برگردانیده، قلاب خود را به چانه ات می‌گذارم و تورا با تمامی لشکرت بیرون می‌آورم. اسبان وسواران که جمیع ایشان با اسلحه تمام آراسته، جمعیت عظیمی با سپرها و مجنها و همگی ایشان شمشیرها به‌دست گرفته، ۴ 4
Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
فارس و کوش و فوط با ایشان و جمیع ایشان با سپر و خود، ۵ 5
Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
جومر و تمامی افواجش و خاندان توجرمه ازاطراف شمال با تمامی افواجش و قوم های بسیارهمراه تو. ۶ 6
haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
پس مستعد شو و تو و تمامی جمعیتت که نزد تو جمع شده‌اند، خویشتن رامهیا سازید و تو مستحفظ ایشان باش. ۷ 7
“‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
بعد ازروزهای بسیار از تو تفقد خواهد شد. و درسالهای آخر به زمینی که از شمشیر استرداد شده است، خواهی آمد که آن از میان قوم های بسیار برکوههای اسرائیل که به خرابه دایمی تسلیم شده بود، جمع شده است و آن از میان قوم‌ها بیرون آورده شده و تمامی اهلش به امنیت ساکن می‌باشند. ۸ 8
Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
اما تو بر آن خواهی برآمد و مثل بادشدید داخل آن خواهی شد و مانند ابرها زمین راخواهی پوشانید. تو و جمیع افواجت و قوم های بسیار که همراه تو می‌باشند.» ۹ 9
Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
خداوند یهوه چنین می‌فرماید: «در آن روزچیزها در دل تو خطور خواهد کرد و تدبیری زشت خواهی نمود. ۱۰ 10
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
و خواهی گفت: به زمین بی‌حصار برمی آیم. بر کسانی که به اطمینان وامنیت ساکنند می‌آیم که جمیع ایشان بی‌حصارندو پشت بندها و دروازه‌ها ندارند. ۱۱ 11
Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
تا تاراج نمایی و غنیمت را ببری و دست خود را به خرابه هایی که معمور شده است و به قومی که ازمیان امت‌ها جمع شده‌اند، بگردانی که ایشان مواشی و اموال اندوخته‌اند و در وسط جهان ساکنند. ۱۲ 12
Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
شبا و ددان و تجار ترشیش و جمیع شیران ژیان ایشان تو را خواهند گفت: آیا به جهت گرفتن غارت آمده‌ای؟ و آیا به جهت بردن غنیمت جمعیت خود را جمع کرده‌ای تا نقره وطلا برداری و مواشی و اموال را بربایی و غارت عظیمی ببری؟ ۱۳ 13
Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
«بنابراین‌ای پسر انسان نبوت نموده، جوج را بگو که خداوند یهوه چنین می‌فرماید: در آن روز حینی که قوم من اسرائیل به امنیت ساکن باشند آیا تو نخواهی فهمید؟ ۱۴ 14
“Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
و از مکان خویش از اطراف شمال خواهی آمد تو وقوم های بسیار همراه تو که جمیع ایشان اسب‌سوار و جمعیتی عظیم و لشکری کثیر می‌باشند، ۱۵ 15
Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
و بر قوم من اسرائیل مثل ابری که زمین راپوشاند خواهی برآمد. در ایام بازپسین این به وقوع خواهد پیوست که تو را به زمین خودخواهم آورد تا آنکه امت‌ها حینی که من خویشتن را در تو‌ای جوج به نظر ایشان تقدیس کرده باشم مرا بشناسند.» ۱۶ 16
Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
خداوند یهوه چنین می‌گوید: «آیا توآنکس نیستی که در ایام سلف به واسطه بندگانم انبیای اسرائیل که در آن ایام درباره سالهای بسیارنبوت نمودند در خصوص تو گفتم که تو را برایشان خواهم آورد؟ ۱۷ 17
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
خداوند یهوه می‌گوید: در آن روز یعنی در روزی که جوج به زمین اسرائیل برمی آید، همانا حدت خشم من به بینی‌ام خواهد برآمد. ۱۸ 18
Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
زیرا در غیرت و آتش خشم خود گفته‌ام که هرآینه در آن روز تزلزل عظیمی در زمین اسرائیل خواهد شد. ۱۹ 19
Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
و ماهیان دریا و مرغان هوا و حیوانات صحرا و همه حشراتی که بر زمین می‌خزند و همه مردمانی که بر روی جهانند به حضور من خواهند لرزید وکوهها سرنگون خواهد شد و صخره‌ها خواهدافتاد و جمیع حصارهای زمین منهدم خواهدگردید. ۲۰ 20
Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
و خداوند یهوه می‌گوید: من شمشیری بر جمیع کوههای خود به ضد او خواهم خواند وشمشیر هر کس بر برادرش خواهد بود. ۲۱ 21
Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
و با وباو خون بر او عقوبت خواهم رسانید. و باران سیال و تگرگ سخت و آتش و گوگرد بر او و برافواجش و بر قوم های بسیاری که با وی می‌باشندخواهم بارانید. ۲۲ 22
Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
و خویشتن را در نظر امت های بسیار معظم و قدوس و معروف خواهم نمود وخواهند دانست که من یهوه هستم. ۲۳ 23
Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’

< حزقیال 38 >