< دانیال 7 >

در سال اول بلشصر پادشاه بابل، دانیال دربسترش خوابی و رویاهای سرش را دید. پس خواب را نوشت و کلیه مطالب را بیان نمود. ۱ 1
A shekara ta fari ta mulkin Belshazar sarkin Babilon, Daniyel ya yi mafarki, wahayoyi kuma suka ratsa tunaninsa a sa’ad da yake a kwance a gadonsa. Sai ya rubuta abin da mafarkin ya ƙunsa.
پس دانیال متکلم شده، گفت: «شبگاهان در عالم رویا شده، دیدم که ناگاه چهار باد آسمان بر روی دریای عظیم تاختند. ۲ 2
Daniyel ya ce, “A cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga kusurwoyi huɗu na sama suna gurɓata babban teku.
و چهار وحش بزرگ که مخالف یکدیگر بودند از دریا بیرون آمدند. ۳ 3
Sai ga dabbobi huɗu, kowannensu ya yi dabam da sauran, suna fitowa daga teku.
اول آنها مثل شیر بود و بالهای عقاب داشت و من نظرکردم تا بالهایش کنده گردید و او از زمین برداشته شده، بر پایهای خود مثل انسان قرار داده گشت ودل انسان به او داده شد. ۴ 4
“Na farkon ya yi kamar zaki kuma yana da fikafikai kamar gaggafa. Ina kallo, sai aka fizge fikafikanta, aka ɗaga ta sama, aka sa ta tsaya a kan ƙafafu biyu kamar mutum, aka ba ta tunani irin na mutum.
و اینک وحش دوم دیگر مثل خرس بود و بر یک طرف خود بلند شدو در دهانش در میان دندانهایش سه دنده بود ووی را چنین گفتند: برخیز و گوشت بسیار بخور. ۵ 5
“A gabana kuma ga dabba ta biyu, wadda ta yi kamar beyar. Aka ɗaga ta a gefenta guda, tana kuwa da haƙarƙarai uku a bakinta a tsakanin haƙoranta. Aka faɗa mata, ‘Tashi ki cika cikinki da ɗanyen nama!’
بعد از آن نگریستم و اینک دیگری مثل پلنگ بود که بر پشتش چهار بال مرغ داشت و این وحش چهار سر داشت و سلطنت به او داده شد. ۶ 6
“Bayan haka, na duba, a gabana kuwa ga wata dabba wadda ta yi kamar Damisa, a bayanta kuma tana da fikafikai huɗu irin na tsuntsu. Wannan dabbar tana da kawuna huɗu, aka kuma ba ta iko tă yi mulki.
بعد ازآن در رویاهای شب نظر کردم و اینک وحش چهارم که هولناک و مهیب و بسیار زورآور بود ودندانهای بزرگ آهنین داشت و باقی‌مانده رامی خورد و پاره پاره می‌کرد و به پایهای خویش پایمال می‌نمود و مخالف همه وحوشی که قبل ازاو بودند بود و ده شاخ داشت. ۷ 7
“Bayan haka, a cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga dabba ta huɗu, wadda take da bantsoro da banrazana da kuma iko ƙwarai. Tana da manyan haƙoran ƙarfe; ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta. Ta bambanta da dukan sauran dabbobin da suka riga ta, tana kuma da ƙahoni goma.
پس در این شاخهاتامل می‌نمودم که اینک از میان آنها شاخ کوچک دیگری برآمد و پیش رویش سه شاخ از آن شاخهای اول از ریشه‌کنده شد و اینک این شاخ چشمانی مانند چشم انسان و دهانی که به سخنان تکبرآمیز متکلم بود داشت. ۸ 8
“Yayinda nake cikin tunani game da ƙahonin nan, a gabana kuwa ga wani ƙaho, ɗan ƙanƙani, wanda ya fito daga cikinsu; kuma an tumɓuke uku daga cikin ƙahonin farko kafin wannan. Wannan ƙaho yana da idanu kamar na mutum da kuma bakin da yake maganganun fariya.
«و نظر می‌کردم تا کرسیها برقرار شد وقدیم الایام جلوس فرمود و لباس او مثل برف سفید و موی سرش مثل پشم پاک و عرش اوشعله های آتش و چرخهای آن آتش ملتهب بود. ۹ 9
“Ina cikin dubawa, “sai aka ajiye kursiyoyi, sai ga wani wanda yake tun fil azal ya zauna a mazauninsa. Rigarsa ta yi fari fat kamar ƙanƙara; gashin kansa sun yi fari kamar ulu. Kursiyinsa kuma harshen wuta, dukan ƙafafun kursiyin masu kama da keken yaƙin, wuta ne.
نهری از آتش جاری شده، از پیش روی اوبیرون آمد. هزاران هزار او را خدمت می‌کردند وکرورها کرور به حضور وی ایستاده بودند. دیوان برپا شد و دفترها گشوده گردید. ۱۰ 10
Kogin wuta yana gudu, yana fitowa daga gabansa. Dubun dubbai sun yi masa hidima; dubu goma sau dubu goma sun tsaya a gabansa. Aka zauna don shari’a, aka kuma buɗe littattafai.
آنگاه نظر کردم به‌سبب سخنان تکبرآمیزی که آن شاخ می‌گفت. پس نگریستم تا آن وحش کشته شد وجسد او هلاک گردیده، به آتش مشتعل تسلیم شد. ۱۱ 11
“Sa’an nan na ci gaba da kallo saboda kalmomin fariyar da wannan ƙaho yake furtawa. Na yi ta kallo har sai da aka yanke dabbar, aka kuma hallaka jikinta a cikin wuta.
اما سایر وحوش سلطنت را از ایشان گرفتند، لکن درازی عمر تا زمانی و وقتی به ایشان داده شد. ۱۲ 12
(An tuɓe sauran dabbobin daga mulkinsu, amma aka bar su su rayu na wani lokaci.)
و در رویای شب نگریستم و اینک مثل پسر انسان با ابرهای آسمان آمد و نزدقدیم الایام رسید و او را به حضور وی آوردند. ۱۳ 13
“A wahayina na dare, na ga a gabana wani kamar ɗan mutum yana saukowa tare da gizagizan sama. Ya kusaci Wannan wanda yake Tun fil azal aka kuma kai shi gabansa.
و سلطنت و جلال و ملکوت به او داده شد تاجمیع قوم‌ها و امت‌ها و زبانها او را خدمت نمایند. سلطنت او سلطنت جاودانی و بی‌زوال است و ملکوت او زایل نخواهد شد. ۱۴ 14
Aka ba shi mulki, daraja da kuma mafificin iko; dukan mutane, da al’ummai, da mutane daga kowane harshe suka yi masa sujada. Mulkinsa kuwa dawwammamen mulki ne da ba zai ƙare ba, sarautarsa kuma ba ta taɓa lalacewa.
«اما روح من دانیال در جسدم مدهوش شدو رویاهای سرم مرا مضطرب ساخت. ۱۵ 15
“Ni, Daniyel, ruhuna ya damu ƙwarai, kuma wahayin da ya ratsa tunanina ya dame ni.
و به یکی از حاضرین نزدیک شده، حقیقت این همه امور را از وی پرسیدم و او به من تکلم نموده، تفسیر امور را برای من بیان کرد، ۱۶ 16
Sai na matsa kusa da ɗaya daga cikin waɗanda suke tsaye a can, na tambaye shi gaskiya ma’anar waɗannan al’amura. “Don haka sai ya faɗa mini, ya kuma ba ni fassarar waɗannan al’amura.
که این وحوش عظیمی که (عدد) ایشان چهار است چهار پادشاه می‌باشند که از زمین خواهند برخاست. ۱۷ 17
‘Waɗannan manyan dabbobi huɗu, Masarautai ne huɗu waɗanda za su taso a duniya.
امامقدسان حضرت اعلی سلطنت را خواهند یافت و مملکت را تا به ابد و تا ابدالاباد متصرف خواهند بود. ۱۸ 18
Amma tsarkaka na Mafi Ɗaukaka za su karɓi wannan sarauta, za su kuwa mallake ta har abada, I, har abada abadin.’
آنگاه آرزو داشتم که حقیقت امررا درباره وحش چهارم که مخالف همه دیگران وبسیار هولناک بود و دندانهای آهنین و چنگالهای برنجین داشت و سایرین را می‌خورد و پاره پاره می‌کرد و به پایهای خود پایمال می‌نمود بدانم. ۱۹ 19
“Sa’an nan kuma sai na so in san ma’anar wannan dabba ta huɗu, wadda ta yi dabam da sauran dabbobin da suke da matuƙar bantsoro, da take da haƙoran ƙarfe da kuma farcen tagulla, dabbar ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta.
و کیفیت ده شاخ را که بر سر او بود و آن دیگری را که برآمد و پیش روی او سه شاخ افتادیعنی آن شاخی که چشمان و دهانی را که سخنان تکبرآمیز می‌گفت داشت و نمایش او از رفقایش سختتر بود. ۲۰ 20
Na kuma so in gane game da ƙahonin nan guda goma da suke a kanta da kuma game da ƙahon nan da ya fito, wanda aka tumɓuke ƙahoni uku a gabansa, ƙahon nan da yake da idanu da bakin da yake furta manyan maganganun fariya, wanda ya yi kamar ya fi sauran girma.
پس ملاحظه کردم و این شاخ بامقدسان جنگ کرده، بر ایشان استیلا یافت. ۲۱ 21
Ina cikin dubawa, sai ga wannan ƙaho yana yaƙi da tsarkaka yana kuma cin nasara a kansu,
تاحینی که قدیم الایام آمد و داوری به مقدسان حضرت اعلی تسلیم شد و زمانی رسید که مقدسان ملکوت را به تصرف آوردند. ۲۲ 22
sai da Wannan wanda yake tun fil azal ya zo ya furta hukunci, aka kuma ba tsarkaka na Mafi Ɗaukaka gaskiya, lokaci kuwa ya cika sai suka karɓi mulki.
پس اوچنین گفت: وحش چهارم سلطنت چهارمین برزمین خواهد بود و مخالف همه سلطنتها خواهدبود و تمامی جهان را خواهد خورد و آن راپایمال نموده، پاره پاره خواهد کرد. ۲۳ 23
“Sai ya ba ni wannan bayani, ‘Dabbar nan ta huɗu, ita ce mulki na huɗu da zai bayyana a duniya. Zai bambanta da dukan sauran mulkoki, zai kuma cinye dukan duniya, yă tattake ta, yă kuma ragargaje ta.
و ده شاخ از این مملکت، ده پادشاه می‌باشند که خواهندبرخاست و دیگری بعد از ایشان خواهدبرخاست و او مخالف اولین خواهد بود و سه پادشاه را به زیر خواهد افکند. ۲۴ 24
Ƙahonin nan goma, sarakuna ne goma waɗanda za su taso daga wannan mulki. Bayansu kuma, wani sarki zai taso, wanda ya sha dabam da waɗanda suka riga shi. Zai rinjayi sarakunan nan uku.
و سخنان به ضدحضرت اعلی خواهد گفت و مقدسان حضرت اعلی را ذلیل خواهد ساخت و قصد تبدیل نمودن زمانها و شرایع خواهد نمود و ایشان تا زمانی ودو زمان و نصف زمان به‌دست او تسلیم خواهندشد. ۲۵ 25
Zai yi maganar saɓo a kan Mafi Ɗaukaka, zai kuma tsananta wa tsarkaka yă kuma yi ƙoƙarin sāke lokuta da shari’u. Za a miƙa tsarkaka a hannunsa na wani lokaci, lokuta da kuma rabin lokaci.
پس دیوان برپا خواهد شد و سلطنت او رااز او گرفته، آن را تا به انتها تباه و تلف خواهندنمود. ۲۶ 26
“‘Amma majalisa za tă yi zama, za a karɓe ikonsa, a kuma hallaka shi gaba ɗaya har abada.
و ملکوت و سلطنت و حشمت مملکتی که زیر تمامی آسمانهاست به قوم مقدسان حضرت اعلی داده خواهد شد که ملکوت اوملکوت جاودانی است و جمیع ممالک او راعبادت و اطاعت خواهند نمود. ۲۷ 27
Sa’an nan za a ba da mulki, iko da girma na mulkokin da suke a ƙarƙashin dukan sammai ga tsarkaka, mutane na Mafi Ɗaukaka. Mulkinsa kuwa mulki ne marar matuƙa, kuma dukan masu mulki za su yabe shi, su kuma yi masa biyayya.’
انتهای امر تابه اینجا است. فکرهای من دانیال مرا بسیارمضطرب نمود و هیئتم در من متغیر گشت، لیکن این امر را در دل خود نگاه داشتم.» ۲۸ 28
“Wannan shi ne ƙarshen batun. Ni, Daniyel na damu ƙwarai da irin tunanina, kuma fuskata ta rikice, amma na riƙe batun a zuciyata.”

< دانیال 7 >