< دانیال 6 >

و داریوش مصلحت دانست که صد و بیست والی بر مملکت نصب نماید تا بر تمامی مملکت باشند. ۱ 1
Ya gamshi Dariyus ya naɗa muƙaddasai 120 su yi shugabanci a duk fāɗin masarautar,
و بر آنهاسه وزیر که یکی از ایشان دانیال بود تا آن والیان به ایشان حساب دهند و هیچ ضرری به پادشاه نرسد. ۲ 2
ya naɗa mutum uku a bisa waɗannan muƙaddasan, Daniyel yana ɗaya daga cikin mutum ukun nan. Sai aka sa muƙaddasan nan a ƙarƙashin waɗannan uku ɗin domin kada sarki ya yi hasarar kome.
پس این دانیال بر سایر وزراء و والیان تفوق جست زیرا که روح فاضل دراو بود وپادشاه اراده داشت که او را بر تمامی مملکت نصب نماید. ۳ 3
To, Daniyel dai ya yi ficce a cikin shugabannin nan uku har da muƙaddasan ma, saboda waɗansu halaye nagari da yake da su, wanda ya sa sarki ya yi shiri ya ɗora shi a kan dukan mulkinsa.
پس وزیران و والیان بهانه می‌جستند تا شکایتی در امور سلطنت بر دانیال بیاورند اما نتوانستند که هیچ علتی یا تقصیری بیابند، چونکه او امین بود و خطایی یا تقصیری دراو هرگز یافت نشد. ۴ 4
A kan haka, shugabannin nan uku da muƙaddasan nan suka yi ƙoƙari su sami wani laifi a kan Daniyel a yadda yake tafiyar da aikin shugabancinsa, amma ba su samu ba. Ba su same shi da wani laifin cin hanci ba, domin shi amintacce ne kuma babu wani aibi a kansa ko rashin kula.
پس آن اشخاص گفتند که «در این دانیال هیچ علتی پیدا نخواهیم کرد مگراینکه آن را درباره شریعت خدایش در او بیابیم.» ۵ 5
A ƙarshe waɗannan mutane suka ce; “Ba za mu taɓa samun wani laifin da za mu kama Daniyel da shi ba, sai dai ko abin ya shafi dokar Allahnsa.”
آنگاه این وزراء و والیان نزد پادشاه جمع شدند و او را چنین گفتند: «ای داریوش پادشاه تابه ابد زنده باش. ۶ 6
Saboda haka shugabannin nan suka haɗu da muƙaddasan nan suka tafi wurin sarki a ƙungiyance suka ce, “Ya Sarki Dariyus, ranka yă daɗe!
جمیع وزرای مملکت و روسا و والیان و مشیران و حاکمان با هم مشورت کرده‌اند که پادشاه حکمی استوار کند و قدغن بلیغی نماید که هر کسی‌که تا سی روز از خدایی یا انسانی سوای تو‌ای پادشاه مسالتی نماید درچاه شیران افکنده شود. ۷ 7
Shugabannin masarauta, da masu mulki, da muƙaddasai, da mashawarta da gwamnoni duk sun amince cewa sarki yă kafa doka yă kuma yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu’a ga wani allah ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, jefa shi cikin kogon zakoki.
پس‌ای پادشاه فرمان رااستوار کن و نوشته را امضا فرما تا موافق شریعت مادیان و فارسیان که منسوخ نمی شود تبدیل نگردد.» ۸ 8
Yanzu, ya sarki, sai ka yi umarni ka kuma yi shi a rubuce saboda kada a canja shi, bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
بنابراین داریوش پادشاه نوشته وفرمان را امضا نمود. ۹ 9
Sai Sarki Dariyus ya ba da umarnin a rubuce.
اما چون دانیال دانست که نوشته امضا شده است به خانه خود درآمد و پنجره های بالاخانه خود را به سمت اورشلیم باز نموده، هر روز سه مرتبه زانو می‌زد و دعا می‌نمود و چنانکه قبل ازآن عادت می‌داشت نزد خدای خویش دعامی کرد و تسبیح می‌خواند. ۱۰ 10
To, da Daniyel ya ji labarin cewa an fitar da doka, sai ya tafi gidansa a ɗakinsa na sama inda tagogin ɗakin suke duban wajen Urushalima. Sau uku yakan durƙusa yă yi addu’a yana yin godiya ga Allahnsa, kamar yadda ya saba yi.
پس آن اشخاص جمع شده، دانیال را یافتند که نزد خدای خودمسالت و تضرع می‌نماید. ۱۱ 11
Sai waɗannan mutane suka tafi a ƙungiyance suka kuma iske Daniyel yana addu’a yana roƙon Allah yă taimake shi.
آنگاه به حضور پادشاه نزدیک شده، درباره فرمان پادشاه عرض کردند که «ای پادشاه آیافرمانی امضا ننمودی که هر‌که تا سی روز نزدخدایی یا انسانی سوای تو‌ای پادشاه مسالتی نماید در چاه شیران افکنده شود؟» پادشاه درجواب گفت: «این امر موافق شریعت مادیان وفارسیان که منسوخ نمی شود صحیح است.» ۱۲ 12
Sai suka tafi wurin sarki suka yi masa magana game da dokar mulkinsa, suka ce, “Ashe, ba ka yi doka cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda aka tarar yana addu’a ga wani allah ko mutum in ba kai ba, ya sarki, za ka jefa shi a cikin ramin zakoki ba?” Sarki ya amsa ya ce, “Dokar tana nan daram bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
پس ایشان در حضور پادشاه جواب دادند وگفتند که «این دانیال که از اسیران یهودا می‌باشد به تو‌ای پادشاه و به فرمانی که امضا نموده‌ای اعتنانمی نماید، بلکه هر روز سه مرتبه مسالت خود رامی نماید.» ۱۳ 13
Sai suka ce wa sarki, “Daniyel ɗin nan, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda aka kwaso daga Yahuda, bai kula da kai ba, ya sarki, balle fa dokar da ka yi. Har yanzu yana addu’a sau uku a rana.”
آنگاه پادشاه چون این سخن راشنید بر خویشتن بسیار خشمگین گردید و دل خود را به رهانیدن دانیال مشغول ساخت و تاغروب آفتاب برای استخلاص او سعی می‌نمود. ۱۴ 14
Da sarki ya ji haka, sai ya damu sosai, ya ƙudura yă ceci Daniyel, ya yi ta fama har fāɗuwar rana yadda zai yi yă kuɓutar da shi.
آنگاه آن اشخاص نزد پادشاه جمع شدند و به پادشاه عرض کردند که «ای پادشاه بدان که قانون مادیان و فارسیان این است که هیچ فرمان یاحکمی که پادشاه آن را استوار نماید تبدیل نشود.» ۱۵ 15
Sai mutanen nan suka je wurin sarki a ƙungiyance suka ce masa, “Ka tuna, ya sarki; cewa bisa ga dokar Medes da Farisa, babu umarni ko dokar da sarki ya yi da za a iya sokewa.”
پس پادشاه امر فرمود تا دانیال را بیاورند واو را در چاه شیران بیندازند و پادشاه دانیال راخطاب کرده، گفت: «خدای تو که او را پیوسته عبادت می‌نمایی تو را رهایی خواهد داد.» ۱۶ 16
Saboda haka sai sarki ya ba da umarni suka kuma kawo Daniyel suka jefa shi cikin ramin zakoki. Sarki ya ce wa Daniyel, “Bari Allahn nan wanda kake bauta masa kullum, yă cece ka!”
وسنگی آورده، آن را بر دهنه چاه نهادند و پادشاه آن را به مهر خود و مهر امرای خویش مختوم ساخت تا امر درباره دانیال تبدیل نشود. ۱۷ 17
Aka kawo dutsen aka rufe bakin ramin, sa’an nan sarki ya hatimce shi da zobensa da kuma zoban manyan mutanensa, don kada wani yă canja yanayin Daniyel.
آنگاه پادشاه به قصر خویش رفته، شب را به روزه بسربرد و به حضور وی اسباب عیش او را نیاوردند وخوابش از او رفت. ۱۸ 18
Sa’an nan sarki ya koma fadarsa ya kwana bai ci ba, kuma babu wata liyafar da aka kawo masa. Ya kuma kāsa barci.
پس پادشاه صبح زود وقت طلوع فجر برخاست و به تعجیل به چاه شیران رفت. ۱۹ 19
Gari yana wayewa, sai sarki ya tashi ya hanzarta zuwa ramin zakoki.
و چون نزد چاه شیران رسید به آوازحزین دانیال را صدا زد و پادشاه دانیال را خطاب کرده، گفت: «ای دانیال بنده خدای حی آیاخدایت که او را پیوسته عبادت می‌نمایی به رهانیدنت از شیران قادر بوده است؟» ۲۰ 20
Da ya yi kusa da ramin zakokin, sai ya kira Daniyel da muryar mai cike da damuwa ya ce, “Daniyel bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta wa kullum, ya iya cetonka daga zakoki?”
آنگاه دانیال به پادشاه جواب داد که «ای پادشاه تا به ابد زنده باش! ۲۱ 21
Sai Daniyel ya amsa ya ce, “Ran sarki, yă daɗe!
خدای من فرشته خود را فرستاده، دهان شیران را بست تا به من ضرری نرسانند چونکه به حضور وی در من گناهی یافت نشد و هم درحضور تو‌ای پادشاه تقصیری نورزیده بودم.» ۲۲ 22
Allahna ya aiko da mala’ikansa, ya kuwa rufe bakunan zakoki. Ba su yi mini rauni ba, gama an same ni marar laifi ne a gabansa. Ban kuwa taɓa yin wani abu marar kyau a gabanka ba, ya sarki.”
آنگاه پادشاه بی‌نهایت شادمان شده، امر فرمود که دانیال را از چاه برآورند و دانیال را از چاه برآوردند و از آن جهت که بر خدای خود توکل نموده بود در اوهیچ ضرری یافت نشد. ۲۳ 23
Sai sarki ya cika da murna ƙwarai, ya kuma yi umarni a ciro Daniyel daga ramin zakoki. Kuma da aka fito da Daniyel daga ramin, ba a sami wani rauni a jikinsa ba, domin ya dogara ga Allahnsa.
و پادشاه امر فرمود تاآن اشخاص را که بر دانیال شکایت آورده بودندحاضر ساختند و ایشان را با پسران و زنان ایشان در چاه شیران انداختند و هنوز به ته چاه نرسیده بودند که شیران بر ایشان حمله آورده، همه استخوانهای ایشان را خرد کردند. ۲۴ 24
Sai sarki ya umarta, a kawo mutanen nan da suka yi wa Daniyel maƙarƙashiya, a tura su, da’ya’yansu, da matansu cikin ramin zakoki. Kafin ma su kai ƙurewar ramin, sai zakoki suka hallaka su suka yayyage su, suka yi kaca-kaca da su.
بعد از آن داریوش پادشاه به جمیع قومها و امت‌ها وزبانهایی که در تمامی جهان ساکن بودند نوشت که «سلامتی شما افزون باد! ۲۵ 25
Sa’an nan Sarki Dariyus ya rubuta wa dukan mutane, da al’ummai da kuma mutanen dukan harsunan a duk fāɗin ƙasar. “Bari yă yi nasara sosai!
از حضور من فرمانی صادر شده است که در هر سلطنتی ازممالک من (مردمان ) به حضور خدای دانیال لرزان و ترسان باشند زیرا که او خدای حی و تاابدالاباد قیوم است. و ملکوت او بی‌زوال وسلطنت او غیرمتناهی است. ۲۶ 26
“Na fitar da doka cewa a cikin dukan iyakar ƙasar mulkina, dole mutane su ji tsoro su kuma girmama Allah na Daniyel.
او است که نجات می‌دهد و می‌رهاند و آیات و عجایب را درآسمان و در زمین ظاهر می‌سازد و اوست که دانیال را از چنگ شیران رهایی داده است.» ۲۷ 27
Yakan kuɓutar ya kuma ceci;
پس این دانیال در سلطنت داریوش و درسلطنت کورش فارسی فیروز می‌بود. ۲۸ 28
Daniyel kuwa ya bunkasa a lokacin mulkin Dariyus da kuma mulkin Sairus na Farisa.

< دانیال 6 >