< دوم پادشاهان 23 >

و پادشاه فرستاد که تمامی مشایخ یهودا و اورشلیم را نزد وی جمع کردند. ۱ 1
Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
و پادشاه و تمامی مردان یهودا و جمیع سکنه اورشلیم با وی و کاهنان و انبیا و تمامی قوم، چه کوچک و چه بزرگ، به خانه خداوندبرآمدند. و او تمامی سخنان کتاب عهدی را که درخانه خداوند یافت شد، در گوش ایشان خواند. ۲ 2
Sai ya haura zuwa cikin haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, da na Urushalima, da firistoci, da annabawa, dukan mutane, manya da ƙanana. Ya karanta musu duk kalmomin Littafin Alkawari, wanda aka samu a haikalin Ubangiji.
و پادشاه نزد ستون ایستاد و به حضور خداوندعهد بست که خداوند را پیروی نموده، اوامر وشهادات و فرایض او را به تمامی دل و تمامی جان نگاه دارند و سخنان این عهد را که در این کتاب مکتوب است، استوار نمایند. پس تمامی قوم این عهد را برپا داشتند. ۳ 3
Sarki ya tsaya dab da ginshiƙi ya kuma sabunta alkawarin a gaban Ubangiji, ya ce zai bi Ubangiji, yă kiyaye dokokinsa, da ƙa’idodinsa, da farillansa, da dukan zuciyarsa da dukan ransa, ta haka ya tabbatar da kalmomin alkawarin da yake a rubuce a cikin littafin nan. Sa’an nan dukan mutane ma suka yi alkawari yin haka.
و پادشاه، حلقیا، رئیس کهنه و کاهنان دسته دوم و مستحفظان در را امر فرمود که تمامی ظروف را که برای بعل و اشیره و تمامی لشکرآسمان ساخته شده بود، از هیکل خداوند بیرون آورند. و آنها را در بیرون اورشلیم در مزرعه های قدرون سوزانید و خاکستر آنها را به بیت ئیل برد. ۴ 4
Sai Yosiya ya umarci Hilkiya babban firist, tare da firistocin da suke taimakonsa, da masu tsaron ƙofa su kawar da dukan abubuwan da aka yi domin Ba’al, da domin Ashera, da kuma domin dukan rundunar taurari, daga haikalin Ubangiji. Ya ƙone su a bayan Urushalima a filayen Kwarin Kidron, ya kwashe tokan zuwa Betel.
و کاهنان بتها را که پادشاهان یهودا تعیین نموده بودند تا در مکان های بلند شهرهای یهودا ونواحی اورشلیم بخور بسوزانند، و آنانی را که برای بعل و آفتاب و ماه و بروج و تمامی لشکرآسمان بخور می‌سوزانیدند، معزول کرد. ۵ 5
Ya kawar da firistocin gumakan da sarakunan Yahuda suka naɗa don su ƙona turare a masujadan kan tuddai na garuruwan Yahuda, da kuma waɗanda suke kewaye da Urushalima, masu ƙona turare wa Ba’al, rana da wata, ga rukunin taurari, da kuma ga dukan rundunan taurari.
واشیره را از خانه خداوند، بیرون از اورشلیم به وادی قدرون برد و آن را به کنار نهر قدرون سوزانید، و آن را مثل غبار، نرم ساخت و گرد آن را بر قبرهای عوام الناس پاشید. ۶ 6
Ya ɗauke ginshiƙin Ashera daga haikalin Ubangiji zuwa Kwarin Kidron can bayan Urushalima, ya ƙone shi a can. Ya niƙa shi sai da ya zama toka, sai ya watsar da ƙurar a filin kabarin talakawa.
و خانه های لواط را که نزد خانه خداوند بود که زنان در آنهاخیمه‌ها به جهت اشیره می‌بافتند، خراب کرد. ۷ 7
Ya kuma rurrushe mazaunan karuwai mazan haikali waɗanda suke a haikalin Ubangiji, da kuma inda mata suke yi wa Ashera saƙa.
وتمامی کاهنان را از شهرهای یهودا آورد ومکانهای بلند را که کاهنان در آنها بخورمی سوزانیدند، از جبع تا بئرشبع نجس ساخت، ومکان های بلند دروازه‌ها را که نزد دهنه دروازه یهوشع، رئیس شهر، و به طرف چپ دروازه شهربود، منهدم ساخت. ۸ 8
Yosiya ya kawo dukan firistoci daga garuruwan Yahuda, ya kuma lalatar da masujadan kan tuddai daga Geba har zuwa Beyersheba, inda firistoci suke ƙona turare. Ya rurrushe matsafai a ƙofofi shigan gari na mashigi zuwa Ƙofar Yoshuwa, gwamnan birnin, wanda yake a hagu da ƙofar birnin.
لیکن کاهنان، مکانهای بلند، به مذبح خداوند در اورشلیم برنیامدند اما نان فطیر در میان برادران خود خوردند. ۹ 9
Ko da yake firistocin masujadan kan tuddai ba su yi hidima a bagaden Ubangiji a Urushalima ba, sun ci burodi marar yisti tare da sauran firistoci.
و توفت راکه در وادی بنی هنوم بود، نجس ساخت تا کسی پسر یا دختر خود را برای مولک از آتش نگذراند. ۱۰ 10
Ya lalatar da Tofet, wanda yake a Kwarin Ben Hinnom, don kada kowa yă iya yin amfani da wurin don yă miƙa hadayar ɗansa, ko’yarsa a wuta ga Molek.
و اسبهایی را که پادشاهان یهودا به آفتاب داده بودند که نزد حجره نتنملک خواجه‌سرا درپیرامون خانه بودند، از مدخل خانه خداوند دورکرد و ارابه های آفتاب را به آتش سوزانید. ۱۱ 11
Ya kawar da dawakan nan da sarakunan Yahuda suka keɓe wa gumakan nan na rana daga mashigin haikalin Ubangiji. Waɗannan dawakan suna kusa da ɗakin Natan Melek, ɗaya daga cikin dattawan sarki. Yosiya ya kuma ƙone kekunan yaƙi a yin sujada ga gumakan nan rana.
ومذبح هایی را که بر پشت بام بالاخانه آحاز بود وپادشاهان یهودا آنها را ساخته بودند، ومذبح هایی را که منسی در دو صحن خانه خداوندساخته بود، پادشاه منهدم ساخت و از آنجاخراب کرده، گرد آنها را در نهر قدرون پاشید. ۱۲ 12
Ya rushe bagadan da sarakunan Yahuda suka kafa a kan ɗakin sama kusa da ɗakin sama na Ahaz, da kuma bagadai biyu da Manasse ya gina a filaye biyu na haikalin Ubangiji. Ya kawar da su daga can, ya farfashe su, ya zubar da tarkacen a Kwarin Kidron.
و مکانهای بلند را که مقابل اورشلیم به طرف راست کوه فساد بود و سلیمان، پادشاه اسرائیل، آنها را برای اشتورت، رجاست صیدونیان و برای کموش، رجاست موآبیان، و برای ملکوم، رجاست بنی عمون، ساخته بود، پادشاه، آنها رانجس ساخت. ۱۳ 13
Sarkin kuma ya lalatar da masujadan kan tuddan da suke gabas da Urushalima, kudu da Tudun Hallaka, waɗanda Solomon sarkin Isra’ila ya gina don Ashtarot, ƙazantacciyar alliyar Sidoniyawa, da Kemosh ƙazantaccen allah na Mowab, da kuma Molek allahn banƙyama na mutanen Ammon.
و تماثیل را خرد کرد و اشیریم را قطع نمود و جایهای آنها را از استخوانهای مردم پر ساخت. ۱۴ 14
Yosiya ya farfashe keɓaɓɓun duwatsu, ya rurrushe ginshiƙan Asheransu, ya baza ƙasusuwan mutane a can.
و نیز مذبحی که در بیت ئیل بود و مکان بلندی که یربعام بن نباط که اسرائیل را مرتکب گناه ساخته، آن را بنا نموده بود، هم مذبح و هم مکان بلند را منهدم ساخت و مکان بلند راسوزانیده، آن را مثل غبار، نرم کرد و اشیره راسوزانید. ۱۵ 15
Har ma da bagaden Betel, masujadan kan tudun da Yerobowam ɗan Nebat ya yi, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi. Wannan bagade da masujadan kan tudun ma ya kawar, ya ƙone masujadan kan tudun, ya niƙa su, ya kuma ƙone ginshiƙin Ashera.
و یوشیا ملتفت شده، قبرها را که آنجا در کوه بود، دید. پس فرستاده، استخوانها رااز آن قبرها برداشت و آنها را بر آن مذبح سوزانیده، آن را نجس ساخت، به موجب کلام خداوند که آن مرد خدایی که از این امور اخبارنموده بود، به آن ندا درداد. ۱۶ 16
Da Yosiya ya dubi kewaye da shi, ya ga kaburburan da suke can a gefen tudu, sai ya sa aka kwaso ƙasusuwan da suke cikinsu aka ƙone a kan bagade don yă lalatar da shi bisa ga maganar Ubangiji ta bakin mutumin Allah, wanda ya yi annabcin waɗannan abubuwa.
و پرسید: «این مجسمه‌ای که می‌بینم، چیست؟» مردان شهر وی را گفتند: «قبر مرد خدایی است که از یهودا آمده، به این کارهایی که تو بر مذبح بیت ئیل کرده‌ای، نداکرده بود.» ۱۷ 17
Sarkin ya yi tambaya, ya ce, “Wane kabari ke nan nake gani?” Mutanen birnin suka ce, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuda, shi ne ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.”
او گفت: «آن را واگذارید و کسی استخوانهای او را حرکت ندهد.» پس استخوانهای او را با استخوانهای آن نبی که ازسامره آمده بود، واگذاشتند. ۱۸ 18
Sai ya ce, “Ku rabu da shi, kada wani yă dami ƙasusuwansa.” Saboda haka suka bar kasusuwansa, da na annabin da ya fito Samariya.
و یوشیا تمامی خانه های مکان های بلند را نیز که در شهرهای سامره بود و پادشاهان اسرائیل آنها را ساخته، خشم (خداوند) را به هیجان آورده بودند، برداشت و با آنها موافق تمامی کارهایی که به بیت ئیل کرده بود، عمل نمود. ۱۹ 19
Kamar yadda ya yi a Betel, Yosiya ya kawar da dukan ɗakunan gumaka a kan tuddan da sarakunan Isra’ila suka gina a garuruwan Samariya, waɗanda suka tozarta Ubangiji.
و جمیع کاهنان مکان های بلند را که در آنجا بودند، بر مذبح هاکشت و استخوانهای مردم را بر آنها سوزانیده، به اورشلیم مراجعت کرد. ۲۰ 20
Yosiya ya yayyanka dukan firistoci na waɗannan masujadan kan tuddai, ya kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kansu. Sa’an nan ya koma Urushalima.
و پادشاه تمامی قوم را امر فرموده، گفت که «عید فصح را به نحوی که در این کتاب عهدمکتوب است، برای خدای خود نگاه دارید.» ۲۱ 21
Sarkin ya ba da umarnin nan ga dukan mutane, cewa, “Ku yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, yadda aka rubuta a Littafin Alkawari.”
به تحقیق فصحی مثل این فصح از ایام داورانی که بر اسرائیل داوری نمودند و در تمامی ایام پادشاهان اسرائیل و پادشاهان یهودا نگاه داشته نشد. ۲۲ 22
Ba a taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa haka ba, tun zamanin da masu shari’a suke aiki a matsayin sarakuna, ko a kwanakin sarakunan Isra’ila, ko na Yahuda.
اما در سال هجدهم، یوشیا پادشاه، این فصح را برای خداوند در اورشلیم نگاه داشتند. ۲۳ 23
Amma a shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yosiya, aka yi Bikin Ƙetarewan nan ga Ubangiji a Urushalima.
و نیز یوشیا اصحاب اجنه و جادوگران وترافیم و بتها و تمام رجاسات را که در زمین یهوداو در اورشلیم پیدا شد، نابود ساخت تا سخنان تورات را که در کتابی که حلقیای کاهن در خانه خداوند یافته بود، به‌جا آورد. ۲۴ 24
Ban da haka, Yosiya ya kawar da masu duba, da masu maita, da allolin gidaje, da gumaka, da duk wani abin banƙyaman da ya gani a Yahuda da Urushalima. Ya yi wannan domin yă cika wa’adodin shari’a yadda suke a littafin da Hilkiya firist ya samu a haikalin Ubangiji.
و قبل از اوپادشاهی نبود که به تمامی دل و تمامی جان وتمامی قوت خود موافق تمامی تورات موسی به خداوند رجوع نماید، و بعد از او نیز مثل او ظاهر نشد. ۲۵ 25
Babu wani sarki kafin Yosiya, ko kuma a bayansa, wanda ya juya ga Ubangiji da dukan zuciyarsa, da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa bisa ga shari’ar Musa, kamar yadda ya yi.
اما خداوند از حدت خشم عظیم خودبرنگشت زیرا که غضب او به‌سبب همه کارهایی که منسی خشم او را از آنها به هیجان آورده بود، بر یهودا مشتعل شد. ۲۶ 26
Duk da haka, Ubangiji bai huce daga zafin fushinsa wanda ya ƙuna game da Yahuda saboda abin da Manasse ya aikata don yă tozarta shi ba.
و خداوند گفت: «یهودارا نیز از نظر خود دور خواهم کرد چنانکه اسرائیل را دور کردم و این شهر اورشلیم را که برگزیدم و خانه‌ای را که گفتم اسم من در آنجاخواهد بود، ترک خواهم نمود.» ۲۷ 27
Saboda haka Ubangiji ya ce, “Zan shafe Yahuda ma kamar yadda na shafe Isra’ila, daga gabana, zan ƙi Urushalima birnin da na zaɓa, da wannan haikali wanda na ce, ‘A can Sunana zai kasance.’”
و بقیه وقایع یوشیا و هرچه کرد، آیا درکتاب تواریخ ایام پادشاهان یهودا مکتوب نیست؟ ۲۸ 28
Game da sauran ayyukan mulkin Yosiya, da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
و در ایام او، فرعون نکوه، پادشاه مصر، بر پادشاه آشور به نهر فرات برآمد و یوشیای پادشاه به مقابل او برآمد و چون (فرعون ) او رادید، وی را در مجدو کشت. ۲۹ 29
Yayinda Yosiya yake sarki, Fir’auna Neko, sarkin Masar ya haura zuwa Kogin Yuferites don yă taimaki sarkin Assuriya da yaƙi. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa’ad da Fir’auna Neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Megiddo.
و خادمانش او رادر ارابه نهاده، از مجدو به اورشلیم، مرده آوردندو او را در قبرش دفن کردند و اهل زمین، یهوآحازبن یوشیا را گرفتند و او را مسح نموده، به‌جای پدرش به پادشاهی نصب کردند. ۳۰ 30
Bayin Yosiya suka ɗauko gawarsa daga Megiddo suka kai Urushalima, suka binne shi a kabarinsa. Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa.
و یهوآحاز بیست و سه ساله بود که پادشاه شد و سه ماه در اورشلیم سلطنت نمود و اسم مادرش حموطل، دختر ارمیا از لبنه بود. ۳۱ 31
Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki. Ya yi mulki na wata uku a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Hamutal’yar Irmiya; mutuniyar Libna.
و اوآنچه را که در نظر خداوند ناپسند بود، موافق هرآنچه پدرانش کرده بودند، به عمل آورد. ۳۲ 32
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yadda kakanninsa suka yi.
وفرعون نکوه، او را در ربله، در زمین حمات، دربند نهاد تا در اورشلیم سلطنت ننماید و صد وزنه نقره و یک وزنه طلا بر زمین گذارد. ۳۳ 33
Fir’auna Neko ya sa shi a sarƙa a Ribla a ƙasar Hamat don kada yă yi mulki a Urushalima, sa’an nan ya sa wa Yahuda harajin talenti ɗari na azurfa, da talenti ɗaya na zinariya.
و فرعون نکوه، الیاقیم بن یوشیا را به‌جای پدرش، یوشیا، به پادشاهی نصب کرد و اسمش را به یهویاقیم تبدیل نمود و یهوآحاز را گرفته، به مصر آمد. و اودر آنجا مرد. ۳۴ 34
Fir’auna Neko ya naɗa Eliyakim ɗan Yosiya sarki a maimakon mahaifinsa, ya kuma canja masa suna zuwa Yehohiyakim. Ya ɗauki Yehoyahaz ya kai Masar, a can ya mutu.
و یهویاقیم، آن نقره و طلا را به فرعون داد اما زمین را تقویم کرد تا آن مبلغ راموافق فرمان فرعون بدهند و آن نقره و طلا را ازاهل زمین، از هرکس موافق تقویم او به زور گرفت تا آن را به فرعون نکوه بدهد. ۳۵ 35
Yehohiyakim ya riƙa biyan Fir’auna Neko azurfa da zinariyar da ya umarta. Don yă yi haka sai ya riƙa karɓar azurfa da zinariya daga mutanen ƙasar, kowa bisa ga ƙarfinsa.
یهویاقیم بیست و پنج ساله بود که پادشاه شد و یازده سال در اورشلیم سلطنت کرد و اسم مادرش زبیده، دختر فدایه، از رومه بود. ۳۶ 36
Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Zebuda’yar Fedahiya, mutuniyar Ruma.
وآنچه را که در نظر خداوند ناپسند بود موافق هرآنچه پدرانش کرده بودند، به عمل آورد. ۳۷ 37
Ya kuma aika mugunta a gaban Ubangiji yadda kakanninsa suka yi.

< دوم پادشاهان 23 >