< دوم پادشاهان 22 >

یوشیا هشت ساله بود که پادشاه شد ودر اورشلیم سی و یک سال سلطنت نمود. و اسم مادرش یدیده، دختر عدایه، ازبصقت بود. ۱ 1
Yosiya yana da shekara takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Yedida’yar Adahiya; mutuniyar Bozkat.
و آنچه را که در نظر خداوند پسندبود، به عمل آورد، و به تمامی طریق پدر خود، داود سلوک نموده، به طرف راست یا چپ انحراف نورزید. ۲ 2
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma bi dukan gurbin kakansa Dawuda, bai bauɗe hagu ko dama ba.
و در سال هجدهم یوشیا پادشاه واقع شد که پادشاه، شافان بن اصلیا بن مشلام کاتب را به خانه خداوند فرستاده، گفت: ۳ 3
A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, Sarki Yosiya ya aiki Shafan ɗan Azaliya, ɗan Meshullam, magatakarda, zuwa haikalin Ubangiji. Ya ce,
«نزد حلقیا رئیس کهنه برو و او نقره‌ای را که به خانه خداوند آورده می‌شود و مستحفظان در، آن را از قوم جمع می‌کنند، بشمارد. ۴ 4
“Ka haura zuwa wurin Hilkiya babban firist ka sa yă shirya kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tara daga mutane.
و آن را به‌دست سرکارانی که بر خانه خداوند گماشته شده‌اند، بسپارند تا ایشان آن را به کسانی که در خانه خداوند کار می‌کنند، به جهت تعمیر خرابیهای خانه بدهند، ۵ 5
Ka sa su danƙa su a hannun waɗanda aka zaɓa don biyan ma’aikatan da suka yi gyara a haikalin Ubangiji,
یعنی به نجاران و بنایان و معماران، و تا چوبها و سنگهای تراشیده به جهت تعمیر خانه بخرند.» ۶ 6
wato, kafintoci, da magina, da masu tsara gini. Ka kuma sa su sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu don a gyara haikalin.
امانقره‌ای را که به‌دست ایشان سپردند، حساب نکردند زیرا که به امانت رفتار نمودند. ۷ 7
Amma ba sa bukata su ba da bayanin kuɗin da aka danƙa musu domin suna aikinsu da aminci.”
و حلقیا، رئیس کهنه، به شافان کاتب گفت: «کتاب تورات را در خانه خداوند یافته‌ام.» وحلقیا آن کتاب را به شافان داد که آن را خواند. ۸ 8
Hilkiya babban firist ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan, shi kuma ya karanta.
وشافان کاتب نزد پادشاه برگشت و به پادشاه خبرداده، گفت: «بندگانت، نقره‌ای را که در خانه خداوند یافت شد، بیرون آوردند و آن را به‌دست سرکارانی که بر خانه خداوند گماشته بودند، سپردند.» ۹ 9
Sa’an nan Shafan ya koma wurin sarki ya ce masa, “Hafsoshinka sun kwashe kuɗin da suke a haikalin Ubangiji, suka ba wa masu aiki da masu lura da haikalin.”
و شافان کاتب، پادشاه را خبر داده، گفت: «حلقیا، کاهن، کتابی به من داده است.» پس شافان آن را به حضور پادشاه خواند. ۱۰ 10
Sa’an nan Shafan magatakarda ya ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta shi a gaban sarki.
پس چون پادشاه سخنان سفر تورات راشنید، لباس خود را درید. ۱۱ 11
Da sarki ya ji kalmomin Littafin Doka, sai ya kece tufafinsa.
و پادشاه، حلقیای کاهن و اخیقام بن شافان و عکبور بن میکایا وشافان کاتب و عسایا، خادم پادشاه را امر فرموده، گفت: ۱۲ 12
Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikahiya, da Shafan magatakarda, da kuma Asahiya mai hidimar sarki, ya ce,
«بروید و از خداوند برای من و برای قوم و برای تمامی یهودا درباره سخنانی که در این کتاب یافت می‌شود، مسالت نمایید، زیرا غضب خداوند که بر ما افروخته شده است، عظیم می‌باشد، از این جهت که پدران ما به سخنان این کتاب گوش ندادند تا موافق هرآنچه درباره مامکتوب است، عمل نمایند.» ۱۳ 13
“Ku je, ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da saboda jama’a da kuma saboda dukan Yahuda game da abin da wannan littafi da aka samo ya ƙunsa. Fushin Ubangiji mai girma ne a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye kalmomin littafin nan ba; ba su aikata bisa ga abin da yake a rubuce game da mu ba.”
پس حلقیای کاهن و اخیقام و عکبور وشافان و عسایا نزد حلده نبیه، زن شلام بن تقوه بن حرحس لباس دار، رفتند و او در محله دوم اورشلیم ساکن بود. و با وی سخن‌گفتند. ۱۴ 14
Sai Hilkiya firist, da Ahikam, Akbor, da Shafan, da kuma Asahiya suka je don su yi magana da annabiya Hulda, matan Shallum ɗan Tikba, ɗan Harhas, mai ajiyar tufafi. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
و او به ایشان گفت: «یهوه، خدای اسرائیل چنین می‌گوید: به کسی‌که شما را نزد من فرستاده است، بگویید: ۱۵ 15
Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ku faɗa wa mutumin da ya aike ku wurina,
خداوند چنین می‌گوید: اینک من بلایی بر این مکان و ساکنانش خواهم رسانید، یعنی تمامی سخنان کتاب را که پادشاه یهوداخوانده است، ۱۶ 16
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, zan kawo masifa wa wannan wuri da kuma wa kan mutanen wurin, bisa ga dukan abubuwan da suke a rubuce a cikin littafin da sarkin Yahuda ya karanta.
چونکه مرا ترک کرده، برای خدایان دیگر بخور‌سوزانیدند تا به تمامی اعمال دستهای خود، خشم مرا به هیجان بیاورند. پس غضب من بر این مکان مشتعل شده، خاموش نخواهد شد. ۱۷ 17
Domin sun yashe ni suka ƙona turare wa waɗansu alloli, suka tozarta ni da dukan gumakan da hannuwansu suka sassaƙa, fushina zai yi ƙuna a kan wannan wuri, ba kuwa zai huce ba.’
لیکن به پادشاه یهودا که شما را به جهت مسالت نمودن از خداوند فرستاده است، چنین بگویید: یهوه، خدای اسرائیل چنین می‌فرماید: درباره سخنانی که شنیده‌ای ۱۸ 18
Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da kalmomin da ka ji.
چونکه دل تو نرم بود و هنگامی که کلام مرادرباره این مکان و ساکنانش شنیدی که ویران ومورد لعنت خواهند شد، به حضور خداوندمتواضع شده، لباس خود را دریدی، و به حضورمن گریستی، بنابراین خداوند می‌گوید: من نیز تورا اجابت فرمودم. ۱۹ 19
Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Ubangiji sa’ad da ka ji abin da na faɗa game da wannan wuri da mutanen wurin, cewa za su zama la’antattu da kuma kango, domin kuma ka kece tufafinka, ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
لهذا اینک من، تو را نزدپدرانت جمع خواهم کرد و در قبر خود به سلامتی گذارده خواهی شد و تمامی بلا را که من بر این مکان می‌رسانم، چشمانت نخواهد دید.» پس ایشان نزد پادشاه جواب آوردند. ۲۰ 20
Saboda haka zan haɗa ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka kuma ba za su ga dukan wannan masifan da zan jawo wa wurin nan ba.’” Sai suka kai wa sarki abin da ta faɗa.

< دوم پادشاهان 22 >