< Matteus 4 >

1 Da blev Jesus av Ånden ført ut i ørkenen for å fristes av djevelen.
Sa’an nan Ruhu ya kai Yesu cikin hamada don Iblis yă gwada shi.
2 Og da han hadde fastet firti dager og firti netter, blev han til sist hungrig.
Bayan ya yi azumi yini arba’in da kuma dare arba’in, sai ya ji yunwa.
3 Og fristeren kom til ham og sa: Er du Guds Sønn, da si at disse stener skal bli til brød!
Sai mai gwajin ya zo wurinsa ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka ce wa duwatsun nan su zama burodi.”
4 Men han svarte og sa: Det er skrevet: Mennesket lever ikke av brød alene, men av hvert ord som går ut av Guds munn.
Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, sai dai da kowace kalmar da take fitowa daga bakin Allah.’”
5 Da tok djevelen ham med sig til den hellige stad og stilte ham på templets tinde, og sa til ham:
Sai Iblis ya kai shi birni mai tsarki, ya kai shi can wuri mafi tsayi duka na haikali.
6 Er du Guds Sønn, da kast dig ned! for det er skrevet: Han skal gi sine engler befaling om dig, og de skal bære dig på hendene, forat du ikke skal støte din fot på nogen sten.
Ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, yi tsalle ka sauka ƙasa. Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
7 Jesus sa til ham: Det er atter skrevet: Du skal ikke friste Herren din Gud.
Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake kuma cewa, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
8 Atter tok djevelen ham med op på et meget høit fjell og viste ham alle verdens riker og deres herlighet og sa til ham:
Har wa yau, Iblis ya kai shi bisa wani dutse mai tsawo sosai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
9 Alt dette vil jeg gi dig hvis du vil falle ned og tilbede mig.
Ya ce, “Zan ba ka dukan wannan, in za ka durƙusa ka yi mini sujada.”
10 Da sa Jesus til ham: Bort fra mig, Satan! for det er skrevet: Herren din Gud skal du tilbede, og ham alene skal du tjene.
Sai Yesu ya ce masa, “Rabu da ni, Shaiɗan! Gama a rubuce yake, ‘Yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai kuma za ka bauta wa.’”
11 Da forlot djevelen ham, og se, engler kom til ham og tjente ham.
Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.
12 Men da han fikk høre at Johannes var kastet i fengsel, drog han bort til Galilea.
Da Yesu ya ji labari cewa an kulle Yohanna a kurkuku, sai ya koma zuwa Galili.
13 Og han forlot Nasaret og kom og tok bolig i Kapernaum ved sjøen, i Sebulons og Naftalis landemerker,
Ya bar Nazaret, ya je ya zauna a Kafarnahum, wadda take a bakin tafki wajen Zebulun da Naftali
14 forat det skulde opfylles som er talt ved profeten Esaias, som sier:
don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,
15 Sebulons land og Naftalis land ved sjøen, landet på hin side Jordan, hedningenes Galilea,
“Ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali, da kuke a hanyar zuwa tekun Galili, a ƙetaren Urdun, wannan yankin Galili ta Al’ummai,
16 det folk som satt i mørke, har sett et stort lys, og for dem som satt i dødens land og skygge, for dem er et lys oprunnet.
mutanen da suke zama cikin duhu sun ga babban haske; haske kuma ya haskaka a kan waɗanda suke zama a inuwar mutuwa.”
17 Fra den tid begynte Jesus å forkynne og si: Omvend eder; for himlenes rike er kommet nær!
Tun daga wannan lokaci, Yesu ya fara wa’azi yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
18 Men da han vandret ved den Galileiske Sjø, så han to brødre, Simon, som kalles Peter, og hans bror Andreas, i ferd med å kaste garn i sjøen; for de var fiskere;
Da Yesu yana kan tafiya a bakin Tekun Galili, sai ya ga waɗansu’yan’uwa guda biyu, Siman wanda ake kira Bitrus da ɗan’uwansa Andarawus. Suna jefa abin kamun kifi a tafki, gama su masunta ne.
19 og han sa til dem: Følg mig, så vil jeg gjøre eder til menneskefiskere!
Sai Yesu ya ce, “Zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masu jan mutane zuwa wurina.”
20 Og de forlot straks sine garn og fulgte ham.
Nan da nan suka bar abin kamun kifinsu suka bi shi.
21 Og da han gikk videre frem, så han to andre brødre, Jakob, Sebedeus' sønn, og hans bror Johannes, sitte i båten med sin far Sebedeus, i ferd med å bøte sine garn, og han kalte dem.
Da ya ci gaba daga nan, sai ya ga waɗansu’yan’uwa guda biyu, Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna. Suna cikin jirgin ruwa tare da mahaifinsu Zebedi, suna shirya abin kamun kifinsu. Yesu ya kira su,
22 Og de forlot straks båten og sin far og fulgte ham.
nan take suka bar jirgin ruwan da mahaifinsu suka kuwa bi Yesu.
23 Og Jesus gikk omkring i hele Galilea og lærte folket i deres synagoger og forkynte evangeliet om riket og helbredet all sykdom og all skrøpelighet blandt folket,
Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane.
24 og ryktet om ham kom ut over hele Syria, og de førte til ham alle dem som hadde ondt og led av alle slags sykdommer og plager, både besatte og månesyke og verkbrudne, og han helbredet dem.
Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su.
25 Og meget folk fulgte ham fra Galilea og Dekapolis og Jerusalem og Judea og landet hinsides Jordan.
Taron mutane mai yawa daga Galili, Dekafolis, Urushalima, Yahudiya da kuma yankin hayin Urdun suka bi shi.

< Matteus 4 >