< Matteus 3 >
1 I de dager stod døperen Johannes frem og forkynte i Judeas ørken
A waɗancan kwanaki, Yohanna Mai Baftisma ya zo, yana wa’azi a Hamadan Yahudiya
2 og sa: Omvend eder; for himlenes rike er kommet nær!
yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”
3 For det er ham profeten Esaias taler om når han sier: Det er en røst av en som roper i ørkenen: Rydd Herrens vei, gjør hans stier jevne!
Wannan shi ne wanda aka yi maganarsa ta wurin annabi Ishaya cewa, “Ga murya mai kira a hamada tana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.’”
4 Men Johannes hadde klædebon av kamelhår og lærbelte om sin lend, og hans mat var gresshopper og vill honning.
Tufafin Yohanna kuwa an yi su da gashin raƙumi ne, yana kuma daure da ɗamara ta fata. Abincinsa kuwa fāri ne da zumar jeji.
5 Da drog Jerusalem og hele Judea og hele landet om Jordan ut til ham,
Mutane suka zo wurinsa daga Urushalima da dukan Yahudiya da kuma dukan yankin Urdun.
6 og de blev døpt av ham i elven Jordan, idet de bekjente sine synder.
Suna furta zunubansu, ya kuma yi musu baftisma a Kogin Urdun.
7 Men da han så mange av fariseerne og sadduseerne komme til hans dåp, sa han til dem: Ormeyngel! hvem lærte eder å fly for den kommende vrede?
Amma da Yohanna ya ga Farisiyawa da Sadukiyawa da yawa suna zuwa inda yake yin baftisma, sai ya ce musu, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku ku guje wa fushin nan mai zuwa?
8 Bær derfor frukt som er omvendelsen verdig,
Ku yi ayyukan da suka dace da tuba.
9 og tro ikke at I kan si ved eder selv: Vi har Abraham til far! for jeg sier eder at Gud kan opvekke Abraham barn av disse stener.
Kada ma ku yi tunani a ranku cewa, ‘Ai, Ibrahim ne mahaifinmu.’ Ina gaya muku cewa Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim daga cikin duwatsun nan.
10 Øksen ligger allerede ved roten av trærne; derfor blir hvert tre som ikke bærer god frukt, hugget ned og kastet på ilden.
An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.
11 Jeg døper eder med vann til omvendelse; men han som kommer efter mig, er sterkere enn jeg, han hvis sko jeg ikke er verdig til å bære; han skal døpe eder med den Hellige Ånd og ild;
“Ina muku baftisma da ruwa domin tuba. Amma wani yana zuwa a bayana wanda ya fi ni iko, wanda ko takalmansa ma ban isa in ɗauka ba. Zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da kuma wuta.
12 han har sin kasteskovl i sin hånd, og han skal rense sin låve og samle sin hvete i laden, men agnene skal han brenne op med uslukkelig ild.
Yana riƙe da matankaɗinsa, zai tankaɗe hatsinsa, yă kuma tattara alkamarsa a cikin rumbu, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
13 Da kom Jesus fra Galilea til Jordan til Johannes for å bli døpt av ham.
Sai Yesu ya zo daga Galili, ya je Urdun don Yohanna yă yi masa baftisma.
14 Men han nektet ham det og sa: Jeg trenger til å bli døpt av dig, og du kommer til mig?
Amma Yohanna ya so yă hana shi, yana cewa, “Ina bukata ka yi mini baftisma, yaya kake zuwa wurina?”
15 Men Jesus svarte og sa til ham: La det nu skje! for således sømmer det sig for oss å fullbyrde all rettferdighet. Da lot han det skje.
Yesu ya amsa ya ce, “Bari yă zama haka yanzu; ya dace mu yi haka don mu cika dukan adalci.” Sa’an nan Yohanna ya yarda.
16 Men da Jesus var døpt, steg han straks op av vannet, og se, himmelen åpnet sig for ham, og han så Guds Ånd fare ned som en due og komme over ham.
Nan da nan da aka yi wa Yesu baftisma, sai ya fito daga ruwa. A wannan lokaci sama ya buɗe, sai ya ga Ruhun Allah yana saukowa kamar kurciya ya kuwa sauka a kansa.
17 Og se, det kom en røst fra himmelen, som sa: Dette er min Sønn, den elskede, i hvem jeg har velbehag.
Sai murya daga sama ta ce, “Wannan shi ne Ɗana wanda nake ƙauna; wanda kuma nake jin daɗinsa ƙwarai.”