< 1 Johannes 2 >
1 Mine barn! dette skriver jeg til eder forat I ikke skal synde; og om nogen synder, da har vi en talsmann hos Faderen, Jesus Kristus, den rettferdige,
’Ya’yana ƙaunatattu, ina rubuta muku wannan ne don kada ku yi zunubi. Amma in wani ya yi zunubi, muna da wani wanda yake magana da Uba don taimakonmu, wato, Yesu Kiristi, Mai Adalci.
2 og han er en soning for våre synder, dog ikke bare for våre, men og for hele verdens.
Shi ne hadayar kafara saboda zunubanmu, kuma ba don namu kaɗai ba amma har ma da zunuban duniya duka.
3 Og derav vet vi at vi kjenner ham: om vi holder hans bud.
Ta haka za mu tabbata cewa mun san shi in muna yin biyayya da umarnansa.
4 Den som sier: Jeg kjenner ham, og ikke holder hans bud, han er en løgner, og i ham er ikke sannheten;
Mutumin da ya ce, “Na san shi,” amma ba ya yin abin da ya umarta, maƙaryaci ne, gaskiya kuwa ba ta cikinsa.
5 men den som holder hans ord, i ham er sannelig kjærligheten til Gud blitt fullkommen. På dette kjenner vi at vi er i ham.
Amma in wani ya yi biyayya da maganarsa, ƙaunar Allah ta zama cikakkiya ke nan a cikinsa. Ta haka muka san cewa muna cikinsa.
6 Den som sier at han blir i ham, han er og skyldig å vandre således som han vandret.
Duk wanda ya ce yana rayuwa a cikinsa dole yă yi tafiya kamar yadda Yesu ya yi.
7 I elskede! det er ikke et nytt bud jeg skriver til eder, men et gammelt bud, som I hadde fra begynnelsen; det gamle bud er det ord som I har hørt.
Abokaina ƙaunatattu, ba sabon umarni nake rubuta muku ba, a’a, daɗaɗɗen umarnin nan ne, wanda kuke da shi tun farko. Wannan tsohon umarni shi ne saƙon da kuka riga kuka ji.
8 Og dog er det et nytt bud jeg skriver til eder, og det er sant i ham og i eder; for mørket viker bort, og det sanne lys skinner allerede.
Duk da haka ina rubuta muku sabon umarni; ana ganin gaskiyar umarnin a cikinsa da kuma cikinku, gama duhu yana shuɗewa, haske na gaskiya kuwa yana haskakawa.
9 Den som sier at han er i lyset, og som hater sin bror, han er ennu i mørket.
Duk wanda ya ce yana cikin haske yana kuma ƙin ɗan’uwansa, ashe a duhu yake har yanzu.
10 Den som elsker sin bror, han blir i lyset, og det er ikke anstøt i ham.
Duk wanda yake ƙaunar ɗan’uwansa, a cikin hasken yake rayuwa ke nan, kuma babu wani abin da yake cikinsa da zai sa yă yi tuntuɓe.
11 Men den som hater sin bror, han er i mørket og vandrer i mørket, og han vet ikke hvor han går hen, fordi mørket har blindet hans øine.
Amma duk wanda yake ƙin ɗan’uwansa, cikin duhu yake, yana kuma tafiya cikin duhu ke nan; bai ma san inda za shi ba, domin duhun ya makanta shi.
12 Jeg skriver til eder, mine barn, fordi eders synder er eder forlatt for hans navns skyld;
Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa.
13 jeg skriver til eder, I fedre, fordi I kjenner ham som er fra begynnelsen; jeg skriver til eder, I unge, fordi I har seiret over den onde. Jeg har skrevet til eder, mine barn, fordi I kjenner Faderen;
Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kun ci nasara a kan mugun nan.
14 jeg har skrevet til eder, I fedre, fordi I kjenner ham som er fra begynnelsen; jeg har skrevet til eder, I unge, fordi I er sterke, og Guds ord blir i eder, og I har seiret over den onde.
Ina rubuta muku,’ya’yana ƙaunatattu, domin kun san Uba. Ina rubuta muku, ubanni, domin kun san shi wanda yake tun farko. Ina rubuta muku, samari, domin kuna da ƙarfi, maganar Allah kuwa tana zaune a cikinku, kun kuma ci nasara a kan mugun nan.
15 Elsk ikke verden, heller ikke de ting som er i verden! Om nogen elsker verden, da er kjærligheten til Faderen ikke i ham;
Kada ku ƙaunaci duniya, ko wani abin da yake cikinta. In wani yana ƙaunar duniya, ƙaunar Uba ba ta cikinsa.
16 for alt det som er i verden, kjødets lyst og øinenes lyst og storaktighet i levnet, er ikke av Faderen, men av verden.
Gama duk abin da yake na duniya, kamar sha’awace-sha’awacen mutuntaka, sha’awar idanunsa, da kuma taƙama da abin da yake da shi, yake kuma yi, ba daga wurin Uba suke fitowa ba sai dai daga duniya.
17 Og verden forgår og dens lyst; men den som gjør Guds vilje, blir til evig tid. (aiōn )
Duniya da sha’awace-sha’awacenta suna shuɗewa, amma mutumin da yake aikata nufin Allah, zai rayu har abada. (aiōn )
18 Mine barn! det er den siste time; og som I har hørt at Antikristen kommer, så er det og nu kommet mange antikrister; derav skjønner vi at det er den siste time.
’Ya’yana ƙaunatattu, waɗannan su ne kwanakin ƙarshe; kuma kamar yadda kuka ji cewa magabcin Kiristi yana zuwa, ko yanzu ma abokan gāban Kiristi da yawa sun zo. Ta haka muka san cewa kwanakin ƙarshe sun iso.
19 De er gått ut fra oss, men de var ikke av oss: for hadde de vært av oss, så var de blitt hos oss; men det skulde bli åpenbart at ikke alle er av oss.
Waɗannan masu gāba da Kiristi suna cikinmu a dā, amma sun bar mu, don tun dā ma su ba namu ba ne. Ai, da su namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun bar mu, wannan ya nuna a fili cewa su ba namu ba ne.
20 Og I har salvelse av den Hellige og vet alt.
Amma ku kam, kuna da shafewa daga wurin Mai Tsarkin nan, kuma dukanku kun san gaskiya.
21 Jeg skriver ikke til eder fordi I ikke kjenner sannheten, men fordi I kjenner den og vet at ingen løgn er av sannheten.
Ina rubuta muku ba domin ba ku san gaskiya ba ne, a’a, sai dai domin kun santa, kun kuma san cewa babu yadda ƙarya za tă fito daga gaskiya.
22 Hvem er løgneren uten den som nekter at Jesus er Kristus? Dette er Antikristen, den som nekter Faderen og Sønnen.
Wane ne maƙaryaci? Ai, shi ne mutumin da yake mūsun cewa Yesu shi ne Kiristi. Irin wannan mutum shi ne magabcin Kiristi, ya yi mūsun Uban da kuma Ɗan.
23 Hver den som nekter Sønnen, har heller ikke Faderen; den som bekjenner Sønnen, har og Faderen.
Ba wanda yake mūsun Ɗan, sa’an nan yă ce yana da Uban; duk wanda ya yarda da Ɗan, yana da Uban a cikinsa ke nan.
24 La det bli i eder som I hørte fra begynnelsen! Dersom det I hørte fra begynnelsen, blir i eder, skal og I bli i Sønnen og i Faderen.
Ku lura fa cewa abin da kuka ji daga farko, bari yă ci gaba da kasance a cikinku. In kuwa ya ci gaba da zama a cikinku, za ku kasance a cikin Ɗan, da kuma a cikin Uban.
25 Og dette er det løfte han lovte oss: det evige liv. (aiōnios )
Wannan shi ne abin da ya yi mana alkawari, wato, rai madawwami. (aiōnios )
26 Dette skriver jeg til eder om dem som forfører eder.
Ina rubuta muku waɗannan abubuwa ne game da waɗanda suke ƙoƙari su sa ku kauce.
27 Og I - den salvelse som I fikk av ham, den blir i eder, og I trenger ikke til at nogen skal lære eder; men som hans salvelse lærer eder alt, så er det og sannhet og ikke løgn; og bli i ham, således som den lærte eder!
Game da ku kuwa, shafan nan da kuka karɓa daga gare shi tana nan a cikinku, ba kwa kuma bukata wani yă koyar da ku. Amma kamar yadda shafan nan tasa tana koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa.
28 Og nu, mine barn, bli i ham, forat vi, når han åpenbares, kan ha frimodighet og ikke bli til skamme for ham ved hans komme!
Yanzu fa, ya ku’ya’yana ƙaunatattu, sai ku ci gaba a cikinsa, domin sa’ad da ya bayyana, mu iya tsaya gabagadi babu kunya a dawowarsa.
29 Dersom I vet at han er rettferdig, så skjønner I at hver den som gjør rettferdighet, er født av ham.
In kun san cewa shi mai adalci ne, to, kun dai san cewa duk mai aikata abin da yake daidai haifaffensa ne.