< 2 Peters 1 >
1 Simeon Peter, Jesu Kristi tjener og apostel - til dem som har fått samme dyre tro som vi ved vår Gud og frelser Jesu Kristi rettferdighet:
Siman Bitrus, bawa da kuma manzon Yesu Kiristi, Zuwa ga waɗanda ta wurin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi sun sami bangaskiya mai daraja irin tamu.
2 Nåde og fred bli eder mangfoldig til del, idet I kjenner Gud og Jesus, vår Herre!
Alheri da salama su zama naku a yalwace ta wurin sanin Allah da Yesu Ubangijinmu.
3 Eftersom hans guddommelige makt har gitt oss alt som tjener til liv og gudsfrykt, ved kunnskapen om ham som kalte oss ved sin egen herlighet og kraft
Ikonsa na Allahntaka ya ba mu kome da muke bukata don rayuwa da kuma tsoron Allah ta wurin sanin wanda ya kira mu ta wurin ɗaukakarsa da nagartarsa.
4 og derved har gitt oss de største og dyreste løfter, forat I ved dem skulde få del i guddommelig natur, idet I flyr bort fra fordervelsen i verden, som kommer av lysten,
Ta wurin waɗannan ya ba mu alkawaransa masu girma da kuma masu daraja, domin ta wurinsu ku iya yin tarayya cikin Allahntakarsa, ku kuma kuɓuta daga lalatar da take cikin duniya wadda mugayen sha’awace-sha’awace suke jawowa.
5 så legg og just derfor all vinn på i eders tro å vise dyd, og i dyden skjønnsomhet,
Saboda haka, ku yi iyakar ƙoƙari ku ƙara wa bangaskiyarku nagarta; ga nagarta kuwa, ku ƙara mata sani;
6 og i skjønnsomheten avhold, og i avholdet tålmod, og i tålmodet gudsfrykt,
ga sani kuma ku ƙara masa kamunkai; ga kamunkai kuma ku ƙara da daurewa; ga daurewa kuwa ku ƙara da tsoron Allah;
7 og i gudsfrykten broderkjærlighet, og i broderkjærligheten kjærlighet til alle.
ga tsoron Allah kuma ku ƙara da nuna alheri ga’yan’uwa; ga nuna alheri ga’yan’uwa kuma ku ƙara da ƙauna.
8 For når disse ting finnes hos eder og får vokse, da viser de at I ikke er uvirksomme eller ufruktbare i kunnskapen om vår Herre Jesus Kristus;
Domin in kuna ƙaruwa a waɗannan halaye, za su kāre ku daga rashin tasiri da rayuwa na rashin amfani cikin saninku na Ubangijinmu Yesu Kiristi.
9 for den som ikke har disse ting, han er blind, nærsynt, idet han har glemt renselsen fra sine fordums synder.
Amma in wani ba shi da su, ba shi da hangen nesa ke nan kuma makaho ne, ya kuma manta cewa an tsarkake shi daga zunubansa na dā.
10 Derfor, brødre, legg enn mere vinn på å gjøre eders kall og utvelgelse fast! for når I gjør disse ting, da skal I ingensinne snuble;
Saboda haka’yan’uwana, ku ƙara aniya wajen tabbatar da kiranku da zaɓenku da aka yi. Gama in kuka yi waɗannan abubuwa, ba za ku taɓa fāɗuwa ba,
11 for på denne måte skal det rikelig gis eder inngang i vår Herre og frelser Jesu Kristi evige rike. (aiōnios )
za ku sami kyakkyawar marabta cikin madawwamin mulkin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. (aiōnios )
12 Derfor vil jeg alltid komme til å minne eder om dette, enda I vet det og er grunnfestet i sannheten, som er hos eder;
Saboda haka kullum zan tuna muku da waɗannan, ko da yake kun sansu kun kuma kahu ƙwarai cikin gaskiyar da kuke da ita yanzu.
13 allikevel akter jeg det for riktig, så lenge jeg er i denne hytte, å vekke eder ved påminnelse,
A ganina ya dace in tunashe ku muddin ina raye cikin tentin wannan jiki,
14 for jeg vet at nedleggelsen av min hytte kommer brått, som og vår Herre Jesus Kristus varslet mig.
domin na sani na kusa in ajiye shi a gefe, yadda Ubangijinmu Yesu Kiristi ya nuna mini a sarari.
15 Men jeg vil og gjøre mig flid for at I til enhver tid efter min bortgang skal kunne minnes dette.
Zan kuwa yi iyakacin ƙoƙari in ga cewa bayan rabuwata kullum za ku iya tuna da waɗannan abubuwa.
16 For ikke var det kløktig uttenkte eventyr vi fulgte da vi kunngjorde eder vår Herre Jesu Kristi makt og gjenkomst, men vi hadde vært øienvidner til hans storhet.
Ba mu bi tatsuniyoyin da aka ƙaga da wayo sa’ad da muka gaya muku game da ikon Ubangijinmu Yesu Kiristi da zuwansa ba, sai dai mu shaidu ne na ɗaukakarsa mai girma da muka gani da ido.
17 For han fikk ære og herlighet av Gud Fader, idet en sådan røst kom til ham fra den ophøiede herlighet: Dette er min Sønn, den elskede, i hvem jeg har velbehag,
Gama ya sami girma da ɗaukaka daga Allah Uba sa’ad da murya ta zo masa daga Mafificiyar Ɗaukaka cewa, “Wannan Ɗana ne, wanda nake ƙauna; da shi nake jin daɗi ƙwarai.”
18 og denne røst hørte vi komme fra himmelen da vi var sammen med ham på det hellige berg.
Mu kanmu mun ji wannan muryar da ta zo daga sama sa’ad da muke tare da shi a kan dutse mai tsarki.
19 Og dess fastere har vi det profetiske ord, som I gjør vel i å akte på som på et lys som skinner på et mørkt sted, inntil dagen lyser frem og morgenstjernen går op i eders hjerter,
Muna kuwa da maganar annabawa da aka ƙara tabbatar mana, zai fi kyau in kuka lura da ita, kamar hasken da yake haskakawa a wuri mai duhu, har yă zuwa wayewar gari da kuma haskakawar tauraron asubahi a zukatanku.
20 idet I først og fremst vet dette at intet profetord i Skriften er gitt til egen tydning;
Gaba da kome dai, dole ku gane cewa babu annabcin Nassin da ya fito daga fassarar annabi da kansa.
21 for aldri er noget profetord fremkommet ved et menneskes vilje, men de hellige Guds menn talte drevet av den Hellige Ånd.
Gama annabci bai taɓa samo tushensa daga nufin mutum ba, sai dai mutane sun yi magana daga Allah yayinda Ruhu Mai Tsarki ya bishe su.