< 2 USamuyeli 19 >

1 Kwasekubikwa kuJowabi kwathiwa: Khangela, inkosi uDavida iyakhala inyembezi, ililela uAbisalomu.
Aka faɗa wa Yowab cewa, “Sarki yana kuka, yana kuma makoki saboda Absalom.”
2 Ukunqoba ngalolosuku kwasekusiba yisililo ebantwini bonke, ngoba abantu bezwa ngalolosuku kuthiwa: Inkosi idabukile ngenxa yendodana yayo.
Saboda haka sai nasarar da aka yi a ranar ta zama makoki ga dukan sojoji, gama a ranar, rundunoni sun ji an ce, “Sarki yana baƙin ciki domin ɗansa.”
3 Abantu basebengena ngokunyenya emzini ngalolosuku njengabantu benyenya belenhloni bebaleka empini.
Mutane fa suka shiga birni shiru, sai ka ce waɗanda sukan sace jiki don kunya sa’ad da suka gudo daga yaƙi.
4 Kodwa inkosi yagubuzela ubuso bayo, inkosi yakhala ngelizwi elikhulu yathi: Ndodana yami Abisalomu, Abisalomu, ndodana yami, ndodana yami!
Sarki ya rufe fuskarsa ya yi kuka da ƙarfi yana cewa, “Ya ɗana Absalom! Ya Absalom ɗana, ɗana!”
5 UJowabi wasengena endlini enkosini wathi: Lamuhla uyangisile ubuso benceku zakho zonke ezisindise impilo yakho lamuhla lempilo yamadodana akho leyamadodakazi akho lempilo yabomkakho lempilo yabafazi bakho abancane.
Sai Yowab ya shiga gidan sarki ya ce, “Yau ka kunyatar da dukan mutanenka, waɗanda ba da daɗewa ba sun ceci ranka, da rayukan’ya’yanka maza, da na’ya’yanka mata, da na matanka da kuma na ƙwarƙwaranka.
6 Uyabathanda abakuzondayo, uzonde abakuthandayo. Ngoba ukuveze obala lamuhla ukuthi izinduna lezinceku kazisilutho kuwe; ngoba ngiyananzelela lamuhla ukuthi uba uAbisalomu ubephila, njalo thina sonke besifile lamuhla, ukuthi bekungabe kulungile emehlweni akho.
Kana ƙaunar maƙiyinka, kana ƙin waɗanda suke ƙaunarka. Ka bayyana a fili cewa komandodi da sojojinsu ba kome ba ne a gare ka. Na ga cewa da za ka yi farin ciki, da a ce Absalom yana da rai a yau, dukanmu kuma mun mutu.
7 Ngakho-ke sukuma, uphume uyekhuluma enhliziyweni yezinceku zakho; ngoba ngifunga ngeNkosi, uba ungaphumi, sibili kakulamuntu ozahlala lawe ngalobubusuku. Lalokhu kuzakuba kubi kuwe kulakho konke okubi okukwehlele kusukela ebutsheni bakho kuze kube khathesi.
Yanzu ka fita ka ƙarfafa mutanenka. Na rantse da Ubangiji, in ba ka fita ba, babu mutum guda da za a bari tare da kai a daren nan. Wannan zai fi maka muni fiye da kowace irin masifar da ta auko maka tun ƙuruciyarka har zuwa yanzu.”
8 Inkosi yasisukuma, yahlala esangweni. Batshela bonke abantu bathi: Khangela, inkosi ihlezi esangweni; basebesiza abantu bonke phambi kwenkosi. UIsrayeli wayebaleke-ke, ngulowo lalowo waya emathenteni akhe.
Saboda haka sarki ya tashi, ya zauna a bakin hanyar shiga. Da aka faɗa wa mutane cewa, “Sarki yana zaune a bakin hanyar shiga,” sai duk suka zo gabansa. Ana cikin haka, Isra’ilawa dai sun riga sun tsere zuwa gidajensu.
9 Njalo abantu bonke babephikisana ezizweni zonke zakoIsrayeli besithi: Inkosi yasikhulula esandleni sezitha zethu, njalo yona yasophula esandleni samaFilisti; kodwa khathesi isibalekile elizweni ngenxa kaAbisalomu.
Mutane ko’ina a kabilan Isra’ila, suka yi ta gardama da juna, suna cewa, “Sarki ne ya cece mu daga hannun abokan gābanmu, shi ne kuma ya kuɓutar da mu daga hannun Filistiyawa. Amma ga shi ya tsere daga ƙasar saboda Absalom;
10 Kodwa uAbisalomu esamgcoba ukuthi abe phezu kwethu ufele empini. Pho-ke, lithuleleni ngokubuyisa inkosi?
kuma shi Absalom, da muka naɗa yă yi mulkinmu, ya mutu a yaƙi. Saboda haka don me ba kwa ce wani abu game da dawo da sarki?”
11 Inkosi uDavida yasithuma kuZadoki lakuAbhiyatha abapristi, isithi: Khulumani labadala bakoJuda lithi: Kungani lingabokucina ukubuyisela inkosi endlini yayo? (Ngoba inkulumo kaIsrayeli wonke ifike enkosini endlini yayo.)
Sai Sarki Dawuda ya aika da saƙo zuwa wurin Zadok da Abiyatar, firistoci, ya ce, “Ku tambayi dattawan Yahuda, ‘Me ya sa ku ne za ku zama na ƙarshe a yin tunanin komar da sarki zuwa fada, da yake abin da ake faɗi ko’ina a Isra’ila ya kai kunnen sarki a mazauninsa?
12 Lingabafowethu, lilithambo lami lenyama yami; ngakho kungani lingabokucina ukubuyisa inkosi?
Ku’yan’uwana ne, jikina, jinina kuma. To, don me za ku zama na ƙarshe na yarda a dawo da sarki zuwa fada?’
13 Lithi-ke kuAmasa: Angithi ulithambo lami lenyama yami? UNkulunkulu kenze njalo kimi engezelele ngokunjalo, uba ungayikuba yinduna yebutho phambi kwami zonke izinsuku esikhundleni sikaJowabi.
Ku kuma ce wa Amasa, ‘Ashe, kai ba jikina ba ne da jinina? Allah yă hukunta ni, da hukunci mai tsanani, idan daga yanzu ba ka zama komandan sojojina a maimakon Yowab ba.’”
14 Wasethobisa inhliziyo yabantu bonke bakoJuda, njengamuntu munye; basebethuma enkosini besithi: Buyela wena lazo zonke inceku zakho.
Ta haka ya rinjayi zukatan dukan mutane Yahuda, kamar mutum ɗaya. Suka aika da saƙo wurin sarki suka ce, “Ka dawo, kai da dukan mutanenka.”
15 Inkosi yasibuyela yafika eJordani; uJuda wasesiza eGiligali ukuyahlangabeza inkosi, ukuchaphisa inkosi iJordani.
Sa’an nan sarki ya dawo, ya kuma tafi har zuwa Urdun. To, mutanen Yahuda suka zo Gilgal don su fita su taryi sarki, su kuma kawo shi ƙetaren Urdun.
16 UShimeyi indodana kaGera umBhenjamini, owaseBahurimi, wasephangisa wehla labantu bakoJuda ukuhlangabeza inkosi uDavida,
Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim ya gaggauta, ya gangara tare da mutanen Yahuda don su taryi Sarki Dawuda.
17 labantu abayinkulungwane bakoBhenjamini belaye, loZiba inceku yendlu kaSawuli, lamadodana akhe alitshumi lanhlanu, lenceku zakhe ezingamatshumi amabili belaye. Basebephangisa baya eJordani phambi kwenkosi.
Tare da shi akwai kabilar Benyamin mutum dubu, tare da Ziba, mai hidimar gidan Shawulu, da’ya’yansa maza goma sha biyar, da bayi ashirin. Suka ruga zuwa Urdun, inda sarki yake.
18 Kwasekuchapha isikepe sokuchapha ukuchaphisa abendlu yenkosi lokwenza okulungileyo emehlweni ayo. UShimeyi indodana kaGera wasewela phansi phambi kwenkosi ekuchapheni kwayo iJordani.
Suka haye a mashigin don su ƙetaro da iyalin sarki, su kuma yi duk abin da yake so. Sa’ad da Shimeyi ɗan Gera ya haye Urdun, sai ya fāɗi rubda ciki a gaban sarki
19 Wasesithi enkosini: Inkosi yami ingangibaleli isiphambeko, futhi ungakhumbuli lokho inceku yakho eyaphambeka ngakho mhla inkosi yami, inkosi, iphuma eJerusalema, ukuthi inkosi ikubeke enhliziyweni yayo.
ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka riƙe laifina a zuciya. Kada ka tuna da laifin da na yi maka ranka yă daɗe, ranan nan da kake gudu daga Urushalima. Kada ka tuna da shi ko kaɗan.
20 Ngoba inceku yakho iyazi ukuthi mina ngonile; khangela-ke, ngifikile lamuhla ngingowokuqala wendlu yonke kaJosefa ukwehla ukuhlangabeza inkosi yami, inkosi.
Na sani ni bawanka na yi maka laifi. Shi ya sa na zama na farko daga dukan Gidan Yusuf, da mutanen Isra’ila wanda ya fito don yă tarye ka yau, ranka yă daɗe, sarki.”
21 Kodwa uAbishayi indodana kaZeruya waphendula wathi: UShimeyi kayikubulawa yini ngalokhu, ngoba wathuka ogcotshiweyo weNkosi?
Sai Abishai ɗan Zeruhiya ya ce, “Bai kamata a kashe Shimeyi saboda wannan ba? Ya la’anci shafaffe na Ubangiji.”
22 UDavida wasesithi: Ngilani lani, madodana kaZeruya, ukuthi libe yisitha kimi lamuhla? Kuzabulawa umuntu lamuhla koIsrayeli yini? Ngoba kangazi yini ukuthi lamuhla ngiyinkosi phezu kukaIsrayeli?
Dawuda ya ce, “Me ya haɗa ni da ku, ku’ya’yan Zeruhiya? Yau ɗin nan kun zama maƙiyana! Ya kamata a kashe wani a Isra’ila a yau? Ban san cewa yau ni sarki ne a bisa Isra’ila ba?”
23 Inkosi yasisithi kuShimeyi: Kawuyikufa. Inkosi yasifunga kuye.
Saboda haka sarki ya ce wa Shimeyi, “Ba za ka mutu ba.” Sarki kuwa ya yi alkawari har da rantsuwa.
24 UMefiboshethi indodana kaSawuli wasesehla ukuhlangabeza inkosi. Wayengalungisanga inyawo zakhe, engalungisanga lendevu zakhe, engawatshanga lezigqoko zakhe, kusukela mhla inkosi ihamba kwaze kwaba mhla ibuya ngokuthula.
Mefiboshet, jikan Shawulu, shi ma ya gangara don yă taryi sarki. Tun daga ranar da sarki ya gudu har ran da ya komo lafiya, Mefiboshet bai lura da ƙafafunsa, ko yă aske gemunsa, ko yă wanke tufafinsa ba.
25 Kwasekusithi esefikile eJerusalema ukuhlangabeza inkosi, inkosi yathi kuye: Kungani ungahambanga lami, Mefiboshethi?
Sa’ad da ya zo daga Urushalima don yă taryi sarki, sai sarki ya ce masa, “Me ya sa ba ka tafi tare da ni ba Mefiboshet?”
26 Wasesithi: Nkosi yami, nkosi, inceku yami yangikhohlisa; ngoba inceku yakho yathi: Ngizazibophelela isihlalo kubabhemi ukuze ngimgade, ngihambe lenkosi, ngoba inceku yakho iyaqhula.
Sai ya ce, “Ranka yă daɗe sarki, da yake bawanka gurgu ne, na ce, ‘A sa mini sirdi a kan jakina don in hau in tafi tare da sarki.’ Amma Ziba bawana ya bashe ni.
27 Njalo iyihlebile inceku yakho enkosini yami, inkosi; kodwa inkosi yami, inkosi, injengengilosi kaNkulunkulu; ngakho yenza okulungileyo emehlweni akho.
Ya kuwa ɓata suna bawanka a gaban ranka yă daɗe, sarki. Ranka yă daɗe, sarki yana kama da mala’ikan Allah, ka yi abin da ka ga ya fi maka kyau.
28 Ngoba yonke indlu kababa ibingesilutho ngaphandle kokuba ngabantu bokufa phambi kwenkosi yami, inkosi; loba kunjalo wayibeka inceku yakho phakathi kwabadla etafuleni lakho. Pho, ngiselalungelo bani ukuthi ngibuye ngikhale enkosini?
Duk zuriyar kakana ba su cancanci kome ba sai mutuwa daga ranka yă daɗe, amma ka ba wa bawanka wuri cikin mutanen da suke ci a teburinka. Saboda haka, wanda’yanci nake da shi da zan yi wani ƙarin roƙo a wurin sarki?”
29 Inkosi yasisithi kuye: Usakhulumelani ngendaba zakho? Ngithe: Wena loZiba lizakwehlukaniselana insimu.
Sarki ya ce masa, “Me ya sa kake zancen nan? Ai, na riga na umarta, da kai, da Ziba ku raba filayen.”
30 UMefiboshethi wasesithi enkosini: Yebo, kayithathe yonke, lokhu inkosi yami, inkosi, isibuyile endlini yayo ngokuthula.
Mefiboshet ya ce wa sarki, “Bari yă ɗauki kome, yanzu da ranka yă daɗe, sarki ya dawo gida lafiya.”
31 UBarizilayi umGileyadi wasesehla evela eRogelimi, wachapha iJordani kanye lenkosi ukuyiphelekezela phetsheya kweJordani.
Barzillai mutumin Gileyad shi ma ya zo daga Rogelim don yă ƙetare Urdun tare da sarki, yă kuma sallame shi daga can.
32 UBarizilayi wayesemdala kakhulu, eleminyaka engamatshumi ayisificaminwembili; yena wayisekela inkosi ekuhlaleni kwayo eMahanayimi, ngoba wayengumuntu omkhulu kakhulu.
To, Barzillai fa tsoho ne, mai shekara tamanin. Ya tanada wa sarki a lokaci da yake Mahanayim, gama shi attajiri ne.
33 Inkosi yasisithi kuBarizilayi: Chapha kanye lami wena, ngizakusekela lami eJerusalema.
Sarki ya ce wa Barzillai, “Ka ƙetaro tare da ni ka zauna tare da ni a Urushalima, zan kuwa tanada maka.”
34 Kodwa uBarizilayi wasesithi enkosini: Zingaki insuku zeminyaka yempilo yami ukuthi ngenyukele eJerusalema lenkosi?
Amma Barzillai ya ce wa sarki, “Shekara nawa ya rage mini har da zan tafi Urushalima da sarki?
35 Lamuhla ngileminyaka engamatshumi ayisificaminwembili; ngingehlukanisa phakathi kokuhle lokubi yini? Inceku yakho inganambitha engikudlayo lengikunathayo yini? Ngingabe ngisawezwa yini amazwi amadoda ahlabelayo lawabesifazana abahlabelayo? Kungani-ke inceku yakho isizakuba ngumthwalo enkosini yami, inkosi?
Yanzu ina da shekara tamanin. Zan iya bambanta abu mai daɗi da marar daɗi kuma ne? Bawanka zai iya jin ɗanɗano abin da yake ci, ko yake sha ne? Har yanzu zan iya jin muryoyin mawaƙan maza da mata? Don me bawanka zai zama ƙari kaya ga ranka yă daɗe?
36 Inceku yakho izake ichaphe iJordani ingcosana nje kanye lenkosi; kungani-ke inkosi izangenanisa ngomvuzo ongaka?
Bawanka zai ƙetare Urdun tare da sarki, yă ɗan yi maka rakiya kaɗan. Me ya sa ranka yă daɗe zai ba ni irin wannan lada.
37 Ngiyakuncenga, yekela inceku yakho ibuyele, ukuze ngifele emzini wami eduze lengcwaba likababa lelikamama. Kodwa khangela, inceku yakho uKhimihamu, kayichaphe lenkosi yami, inkosi, uyenzele okulungileyo emehlweni akho.
Ka bar bawanka yă koma, don in mutu a garina, kusa da kabarin mahaifina da mahaifiyata. Amma ga bawanka Kimham. Bari yă ƙetare tare da ranka yă daɗe, sarki. Ka yi abin da ka ga dama da shi.”
38 Inkosi yasisithi: UKhimihamu uzachapha lami; njalo mina ngizamenzela okulungileyo emehlweni ami, lakho konke okufunayo kimi ngizakwenzela khona.
Sarki ya ce, “Kimham zai ƙetare tare da ni, zan kuwa yi masa abin da ya gamshe ka. Kuma duk abin da kake bukata a wurina, zan yi maka.”
39 Bonke abantu basebechapha iJordani, lenkosi yachapha, inkosi yamanga uBarizilayi, yambusisa, wasebuyela endaweni yakhe.
Saboda haka dukan mutane suka ƙetare Urdun, sa’an nan kuma sarki ma ya ƙetare. Sarki ya yi wa Barzillai sumba ya albarkace shi, sa’an nan Barzillai ya koma gidansa.
40 Inkosi yasisedlulela eGiligali, loKhimihamu wedlula layo; labo bonke abantu bakoJuda bayidlulisela phambili inkosi, futhi lengxenye yesizwe sakoIsrayeli.
Sa’ad da sarki ya ƙetare zuwa Gilgal, Kimham ma ya ƙetare tare da shi. Dukan sojojin Yahuda da rabin sojojin Isra’ila suka ƙetare da sarki.
41 Khangela-ke, bonke abantu bakoIsrayeli beza enkosini bathi enkosini: Abafowethu, abantu bakoJuda, bakuntshontsheleni, bachaphisa inkosi lendlu yayo iJordani labo bonke abantu bakaDavida belaye?
Nan take sai ga mutane Isra’ila suna zuwa wurin sarki, suna cewa, “Don me’yan’uwanmu, mutanen Yahuda, suka saci sarki, suka kawo shi da iyalinsa a ƙetaren Urdun, tare da dukan mutanensa?”
42 Bonke abantu bakoJuda basebephendula amadoda akoIsrayeli bathi: Ngoba inkosi iyisihlobo sethu; pho-ke, lithukuthelelani ngalindaba? Sike sadlani okwenkosi? Kumbe isinike isipho yini?
Dukan mutanen Yahuda suka ce wa mutanen Isra’ila, “Mun yi haka domin sarki danginmu na kurkusa ne. Don me kuke fushi game da wannan? Mun ci wani abu daga cikin kayan sarki ne? Mun ɗauki wani abu wa kanmu ne?”
43 Njalo amadoda akoIsrayeli aphendula amadoda akoJuda, athi: Silengxenye ezilitshumi enkosini, futhi lakuDavida silelungelo okwedlula lina. Pho, lasidelelelani ukuthi ilizwi lethu lingabi ngelokuqala ukubuyisa inkosi yethu? Kodwa ilizwi lamadoda akoJuda lalilukhuni kulelizwi lamadoda akoIsrayeli.
Sa’an nan mutanen Isra’ila suka ce wa mutanen Yahuda, “Muna da rabo goma a wurin sarki; ban da haka ma, muna da hakki mafi yawa a wurin Dawuda fiye da ku. Don me kuke mana reni? Ba mu ne ma muka fara magana dawowa da sarki ba?” Amma mutanen Yahuda suka ɗauka maganar da zafi fiye da mutanen Isra’ila.

< 2 USamuyeli 19 >