< Izililo 3 >

1 Yimi umuntu olubonileyo usizi ngenxa yoswazi lokuthukuthela kukaThixo.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Ungixotshile, wangiphumputhekisa emnyameni hatshi ekukhanyeni;
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 ngempela usengiphakamisele isandla sakhe, waphindaphinda ilanga lonke.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 Usenze ijwabu lami laluphala, wangephula amathambo.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 Ungihanqile wangihonqolozela ngosizi langobunzima.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 Ungenze ngahlala emnyameni njengalabo abafa kudala.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 Ungihonqolozele ngenqaba ukuze ngingaphunyuki; ungibophe nko ngamaketane.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Kuthi lanxa ngimemeza loba ngidinga usizo, awuvalele phandle umkhuleko wami.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 Uvale indlela yami ngamatshe; waphambukisa izindlela zami.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 Njengebhele licathamile, njengesilwane sicatshile,
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 wangihudulela eceleni kwendlela, wangifohloza, wangitshiya ngingelamsizi.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 Wadonsa idandili lakhe, ngaba yikudla kwemitshoko yakhe.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 Wangiciba enhliziyweni ngemitshoko evela emxhakeni wakhe.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 Ngaba yinhlekisa ebantwini bakithi bonke; sengitshona ngiyingoma eyinhlekisa kubo.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 Ungigqibe ngemithi ebabayo, wanginathisa inyongo.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 Ungihlafunise ukhethe ngamazinyo; wangigiqa ebhuqwini.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 Ngincitshiwe ukuthula; angisakwazi ingabe iyini impumelelo.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 Ngakho ngithi, “Sebuphelile ubucwazicwazi bami, lakho konke engangikulindele kuThixo.”
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Ngikhumbula ukuhlupheka lokuntula kwami, ubumunyu lenyongo.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 Konke ngikukhumbula kamhlophe, umoya wami wephukile.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 Kodwa ngikhumbula lokhu ngibe lethemba:
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 Ngenxa yothando olukhulu lukaThixo kasibhujiswanga, ngoba isihawu sakhe kasipheli.
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 Siba sitsha ukusa kwamalanga; kukhulu ukuthembeka kwakho.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 Ngiyazitshela ngithi, “UThixo uyisabelo sami; ngakho ngizalindela yena.”
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 UThixo ulungile kulowo omethembayo, kulowo omdingayo;
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 kuhle ukulinda ngokuthula, ukulindela insindiso kaThixo.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 Kuhle ukuthi umuntu alithwale ijogwe ngesikhathi esesemutsha.
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 Kahlale yedwa ngokuthula, ngoba uThixo ulibeke phezu kwakhe.
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 Kembele ubuso bakhe ethulini, mhlawumbe ithemba lizakuba khona.
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 Kaphe isihlathi sakhe kulowo ofuna ukumhlankala, agcwale ihlazo.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 Ngoba uThixo kabalahli abantu kuze kube nini lanini.
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 Loba engaletha ubuhlungu, uzatshengisa uzwelo, lukhulu kakhulu uthando lwakhe olungapheliyo.
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 Ngoba kehliseli ukuhlupheka losizi ebantwini ngokuthanda.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 Ukuhlifiza ngezinyawo zonke izibotshwa elizweni,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 ukuncitsha umuntu amalungelo akhe phambi koPhezukonke,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 ukungahluleli kuhle, kambe uThixo uyabe engaziboni izinto ezinjalo na?
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Ngubani ongatsho ulutho lwenzakale nxa lungavunyelwanga nguThixo na?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Akuveli emlonyeni woPhezukonke ukuthi kuyehla inhlupheko lezinto ezinhle na?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Pho kungani umuntu ophilayo esola nxa ejeziselwa izono zakhe na?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Kasilingeni njalo sihlole izindlela zethu, sibuyele kuThixo.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Asiphakamiseleni inhliziyo lezandla zethu kuNkulunkulu ezulwini sithi:
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 “Sonile sahlamuka, njalo kawusithethelelanga.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Uzigubuzele ngolaka waxhumana lathi; ubhubhisile ungelazwelo.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 Uzisibekele ngeyezi ukuze kungafinyeleli mkhuleko kuwe.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Usenze saba ngamanyala lengcekeza phakathi kwezizwe.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 Izitha zethu zonke zivule imilomo yazo zezwakala zisihoza.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Sesihlukuluzwe yikuthuthumela lokukhilikithela, ukudilika lokubhidlika.”
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Imifula yezinyembezi iyajuluka emehlweni ami ngoba abantu bakithi babhujisiwe.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Amehlo ami azajuluka kokuphela, engelakuphumula,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 UThixo aze akhangele phansi esezulwini, angibone.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Engikubonayo kuthelela usizi emphefumulweni wami ngenxa yabesifazane bonke bomuzi wakithi.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 Labo ababa yizitha zami kungelasizatho, bangizingela njengenyoni.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 Bazama ukuquma impilo yami emgodini bangijikijela ngamatshe;
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 amanzi asibekela ikhanda lami, ngabona ukuthi okwami sekuphelile.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 Ngalimemezela ibizo lakho, Oh Thixo, ngisekujuleni komgodi.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Wezwa ukuncenga kwami: “Ungavali indlebe zakho nxa ngikhalela ukwenyulwa.”
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Wasondela lapho ngikumemeza, wathi kimi, “Ungesabi.”
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Oh Thixo, wasamukela isikhalazo sami; wahlenga ukuphila kwami.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Ububonile Thixo, ububi obenziwe kimi. Ngisekela kulobubunzima!
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Usubonile ukujula kokusonga kwabo, lamacebo abo wonke ngami.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Awu Thixo, uzwile inhlamba zabo, wonke amacebo abo ngami,
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 ukunyenyeza lokungunguna kwabo ngami ukusa kwamalanga.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Ake ubabone! Bahlezi kumbe bajamile, bayangihleka ngezingoma zabo.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Awu Thixo, akubaphindisele ngokubafaneleyo, ngalokho okwenziwe yizandla zabo.
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 Basibekele ngelembu ezinhliziyweni zabo, isiqalekiso sakho sehlele phezu kwabo!
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 Xhumana labo ngolaka, ubabhubhise ngaphansi kwamazulu kaThixo.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Izililo 3 >