< UHezekheli 1 >
1 Ngomnyaka wamatshumi amathathu, ngenyanga yesine ngosuku lwesihlanu, lapho ngangiphakathi kwabathunjwayo, eduze komfula uKhebhari, amazulu avuleka ngabona umbono kaNkulunkulu.
A shekara ta talatin, a wata na huɗu a rana biyar, yayinda nake cikin’yan zaman bauta kusa da Kogin Kebar, sai sammai suka buɗe na kuwa ga wahayoyin Allah.
2 Ngosuku lwesihlanu lwenyanga ngomnyaka wesihlanu wokuthunjwa kwenkosi uJehoyakhini
A rana biyar ga wata, a shekara ta biyar ne ta zaman bautan Sarki Yehohiyacin,
3 ilizwi likaThixo lafika kuHezekhiyeli umphristi, indodana kaBhuzi, phansi komfula uKhebhari elizweni lamaBhabhiloni. Khonapho isandla sikaThixo sasiphezu kwakhe.
maganar Ubangiji ta zo wa Ezekiyel firist, ɗan Buzi, kusa da Kogin Kebar a ƙasar Babiloniyawa. A can hannun Ubangiji yana a kansa.
4 Ngakhangela, ngabona isiphepho sisiza sivela enyakatho, kuliyezi elikhulukazi lokuphazima kombane njalo lizungezwe yikukhanya okubenyezelayo. Phakathi laphakathi komlilo kwakungathi yinsimbi evuthayo,
Na duba, sai na ga guguwa ta taso daga arewa babban hadari cike da walƙiya kewaye da haske mai haske sosai. Tsakiyar wutar ta yi kamar ƙarfe mai cin wuta balbal,
5 njalo phakathi komlilo kwakulokwakungathi yizidalwa ezine eziphilayo. Ngokukhangeleka isimo sazo sasingesomuntu,
a cikin wutar kuwa akwai abin da ya yi kamar halittu guda huɗu. A bayyane kamanninsu ya yi kamar siffar mutum,
6 kodwa ngasinye sazo sasilobuso obune lempiko ezine.
amma kowannensu yana da fuskoki huɗu da fikafikai guda huɗu.
7 Imilenze yazo yayiqondile; inyawo zazo zinjengezethole njalo zinkanyazela njengethusi elilolongiweyo.
Ƙafafunsu miƙaƙƙu ne; kuma ƙafafunsu sun yi kamar na maraƙi suna kuma walƙiya kamar tagullar da aka goge.
8 Ngaphansi kwempiko zazo emaceleni azo amane zazilezandla zomuntu. Zonke zozine zazilobuso lempiko,
A ƙarƙashin fikafikansu huɗu suna da hannuwan mutum a kowane gefe. Dukansu huɗu suna da fuskoki da fikafikai,
9 njalo impiko zazo zazithintana. Esinye lesinye sazo saya phambili; kaziphendukanga ekuhambeni kwazo.
kuma fikafikansu suna taɓan juna. Kowanne ya miƙe gaba; ba sa juyawa sa’ad da suke tafiya.
10 Ubuso bazo babukhangeleka kanje: Esinye lesinye sazo sasilobuso bomuntu, njalo eceleni langakwesokudla esinye lesinye sasilobuso besilwane, ngakwesenxele silobuso benkabi; njalo ngasinye sasilobuso bengqungqulu.
Fuskokinsu sun yi kamar haka. Kowanne a cikin huɗun yana da fuskar mutum, kuma a gefen dama kowanne yana da fuskar zaki, a hagu kuma fuskar maraƙi; kowanne yana kuma da fuskar gaggafa.
11 Babunjalo ubuso bazo. Impiko zazo zazichayekele phezulu; ngasinye silamaphiko amabili olunye luthinta uphiko lwesinye isidalwa emaceleni womabili, lempiko ezimbili zigubuzele umzimba waso.
Haka fuskokinsu suka kasance. Fikafikansu sun buɗu sama; kowanne yana da fikafikai biyu, ɗaya yana taɓa fikafikan ɗayan halittar a ɗayan gefe, fikafikai biyu kuma suna rufe jikinsa.
12 Esinye lesinye saya phambili. Loba kungaphi lapho umoya owaya khona lazo zaya khona zingaphenduki ekuhambeni kwazo.
Kowanne ya miƙe gaba sosai. Duk inda ruhu zai tafi, can za su, ba tare da juyawa ba yayinda suke tafiya.
13 Isimo sezidalwa eziphilayo sasinjengamalahle avuthayo omlilo loba njengezibane. Umlilo wahamba usiya phambili lasemuva phakathi kwezidalwa; wawukhazimula, njalo umbane uphazima uphuma kuwo.
Kamannin halittun ya yi kamar garwashi mai cin wuta ko kuwa kamar fitilu. Wuta tana kai da kawowa a cikin halittun; ta yi haske ƙwarai, walƙiya kuma tana wulgawa daga cikinta.
14 Izidalwa zagijima zisiya emuva laphambili njengokuphazima kombane.
Halittun suna gaggauta kai da kawowa kamar walƙiya.
15 Kwathi lapho ngizikhangele izidalwa eziphilayo, ngabona ivili phansi eceleni kwesidalwa ngasinye silobuso obune.
Yayinda nake kallon rayayyun halittun nan, sai na ga da’ira a ƙasa kusa da kowace halitta da fuskokinsa huɗu.
16 Nansi isimo lokwakhiwa kwamavili: Ayecazimula njengekhrisoli, njalo wonke womane ayefanana. Elinye lelinye lalingathi lenziwa lanquma kwelinye ivili.
Ga kamanni da fasalin da’irorin. Suna ƙyalƙyali kamar kirisolit, kuma dukan huɗun sun yi kama da juna. Kowacce ta yi kamar da’ira a cikin da’ira.
17 Ekuhambeni, ayesiya loba kuliphi lamacele amane lapho izidalwa ezazikhangele khona, njalo amavili ayengaphenduki lapho izidalwa zihamba.
Yayinda suke tafiya, sukan nufi duk wani gefe guda cikin gefe huɗun da halittun suka nufa; da’irorin ba za su juya ba sa’ad da halittun suke tafiya.
18 Amarimu awo ayephakeme njalo esesabeka, njalo womane amarimu ayelamehlo indawo yonke.
Ƙarafansu da suka yi kamar zobe sun yi tsayi suna kuma da bantsoro, dukan ƙarafan nan huɗu kuwa da suka yi kamar zobe suna cike da idanu a kewaye.
19 Lapho izidalwa eziphilayo zihamba, lamavili eceleni kwazo ayehamba, njalo lapho izidalwa eziphilayo ziphakama emhlabathini amavili lawo ayephakama lazo.
Sa’ad da rayayyun halittun suke tafiya, da’irorin da suke kusa da su kan motsa; kuma sa’ad da rayayyun halittun sun tashi sama, da’irorin su ma sukan tashi sama.
20 Loba kungaphi lapho umoya owaya khona lazo zaya khona, njalo lamavili ayephakama lazo, ngoba umoya wezidalwa eziphilayo wawusemavilini.
Duk inda ruhu za shi, su ma can za su, kuma da’irorin za su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
21 Kwakusithi izidalwa zingahamba lawo ahambe, kuthi izidalwa zingema lawo ame; njalo kuthi lapho izidalwa ziphakama emhlabathini lawo aphakame lazo, ngoba umoya wezidalwa eziphilayo wawusemavilini.
Sa’ad da halittun sun motsa, sai su ma su motsa; sa’ad da halittun sun tsaya cik, su ma sai su tsaya cik, sa’ad da kuma halittun sukan tashi sama, da’irorin suka tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
22 Ngaphezu kwamakhanda ezidalwa eziphilayo kwakwendlaleke okwakungathi ngumkhathi, kucazimula njengongqwaqwane, njalo kusesabeka.
A bisa kawunan rayayyun halittun nan akwai abin da ya yi kamar ƙanƙara, mai bantsoro.
23 Ngaphansi komkhathi impiko zazo zazelulekile olunye kolunye, njalo esinye lesinye sasilezimpiko ezimbili ezembese umzimba waso.
A ƙarƙashin al’arshin fikafikansu sun miƙe kyam ɗaura da juna, kuma kowanne yana da fikafikai biyu da suka rufe jikinsa.
24 Lapho izidalwa zihamba ngezwa umsindo wezimpiko zazo, unjengokuhlokoma kwamanzi ahamba ngesiqubu, njengelizwi likaSomandla, njengokuxokozela kwebutho. Lapho sezimi, zehlisa impiko zazo.
Sa’ad da halittun suke tafiya, sai na ji ƙarar fikafikansu, kamar rurin ruwaye masu gudu, kamar muryar Maɗaukaki, kamar hayaniyar rundunar mayaƙa. In sun tsaya cik, sukan sauko da fikafikansu.
25 Emva kwalokho kweza ilizwi elavela ngaphezu komkhathi ngaphezu kwamakhanda azo lapho zazimi impiko zazo zehlisiwe.
Sai aka ji murya daga al’arshi a kan kawunansu yayinda suke tsaye da fikafikansu a sauke.
26 Ngaphezu komkhathi phezu kwamakhanda azo kwakulokwakungathi yisihlalo sobukhosi esenziwe ngesafire, njalo ngaphezulu esihlalweni sobukhosi kwakulolutho olwalufana lomuntu.
A bisa al’arshin a kan kawunansu akwai abin da ya yi kamar saffaya, kuma a can bisa a kan kursiyin akwai siffa kamar na mutum.
27 Lokho ngakubona kokwakungathi lukhalo lwakhe kusiya phezulu ekhanya angathi yinsimbi evuthayo, kungathi kugcwele umlilo, njalo kusukela ekhalweni kusehla wayengathi ngumlilo, njalo ehonqolozelwe yikukhanya okucazimulayo.
Na ga daga abin da ya yi kamar kwankwasonsa zuwa bisa ya yi kamar ƙarfe mai walƙiya, sai ka ce wuta, kuma daga kwankwasonsa zuwa ƙasa ya yi kamar wuta; haske kuma mai walƙiya sosai kewaye da shi.
28 Ukukhanya okucazimulayo okwakumzungezile kwakunjengomchilo wamakhosikazi emayezini ngosuku lokuna kwezulu. Lokhu kwakuyisimo sesifanekiso senkazimulo kaThixo. Ngathi ngikubona ngawela phansi ngobuso, ngasengisizwa ilizwi lalowo owayekhuluma.
Kamar kamannin bakan gizo a cikin gizagizai a ranar da aka yi ruwan sama, haka hasken da ya kewaye shi. Wannan shi ne kwatancin kamannin ɗaukakar Ubangiji. Sa’ad da na gani, sai na fāɗi rubda ciki, na kuma ji muryar wani tana magana.