< Deotoronomia 11 >
1 Aa le kokò t’Iehovà Andrianañahare’o naho tomiro nainai’e o nampiambena’eo, o fañè’eo, o fepè’eo, vaho o lili’eo.
To, sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kullum ku kuma kiyaye abubuwan da yake bukata, ku kiyaye ƙa’idodinsa, dokokinsa da kuma umarnansu.
2 Le mahafohina anito te tsy o ana’ areoo ty ivolañako, ie mbe tsy maharendreke naho tsy nahatrea ty fanampiha’ Iehovà Andrianañahare’ areo, naho ty hajabahina’e naho ty fità’e maozatse vaho i sira’e natora-kitsiy,
Ku tuna a yau, cewa’ya’yanku ba su ne suka gani suka kuma ɗanɗana horon Ubangiji Allahnku ba; ba su suka gani girmansa, hannunsa mai ƙarfi, hannunsa mai iko;
3 o vilo’eo naho ze hene fitoloñañe nanoe’e e Mitsraime ao amy Parò mpanjaka’ i Mitsraime naho amo tane’eo;
alamun da ya aikata da abubuwan da ya yi a cikin Masar, ga Fir’auna sarkin Masar da kuma ga dukan ƙasarsa ba;
4 ty nanoe’e o lahindefo’ i Mitsraimeo naho o soavala reketse sarete’eo, te najorobo’e an-drano’ i Ria-Binday o lahara’ iareoo, ie nañoridañe anahareo, toly ndra nandrotsaha’ Iehovà pake henane;
ba su suka gani abin da ya yi wa mayaƙan Masar, da dawakansu da keken yaƙinsu, yadda ya sha kansu da ruwan Jan Teku yayinda suke bin ku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf ba.
5 naho o nanoe’e ama’ areo ampatrambey ao ampara’ ty nivotraha’ areo atoio;
Ba’ya’yanku ba ne suka gani abin da ya yi dominku a hamada har sai da kuka kai wannan wuri ba,
6 le ty nanoe’e i Datane naho i Abirame, ana’i Eliabe ana’i Reòbene, ie nanokake ty vava’e i taney, nampibotseke iareo rekets’ o keleia’eo naho o kiboho’eo vaho ze fonga raha veloñe nañorike iareo, añivo’ Israele iaby ao;
ba su ba ne suka gani abin da ya yi ga Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab mutumin Ruben, sa’ad da ƙasa ta buɗe bakinta a tsakiyar dukan Isra’ila ta haɗiye su tare da gidajensu, tentunansu da kowane abu mai rai da yake nasu ba.
7 o fihaino’ areoo ro nahaisake ze hene fitoloñañe fanjàka nanoe’ Iehovào.
Amma idanunku ne suka ga dukan waɗannan manyan abubuwan da Ubangiji ya yi.
8 Ambeno arè ze hene lily lilieko androany, soa t’ie ho aman’ ozatse hahafionjoñe hitsake mb’ an-tane ho tavane’ areo mb’eo,
Saboda haka sai ku kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, don ku sami ƙarfin da za ku shiga, ku kuma karɓi ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaka,
9 vaho t’ie ho lava havelo amy tane nifantà’ Iehovà aman-droae’ areo hatolo’e iareo naho o tarira’eoy, tane orikorihen-dronono naho tantele.
domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su da zuriyarsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
10 Tsy hambañe an-tane Mitsraime niavota’ areo i tane hiziliha’ areo ho tavaneñey, i nitongisa’ areo tabiry naho nanondraha’ areo rano am-pandia hoe fanondrahan-golobon’ añañey,
Ƙasar da kuke shiga, ku karɓa, ba kamar ƙasar Masar ba ce, inda kuka fito, inda kuka shuka iri, ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu.
11 te mone tane aman-kivohibohitse naho vavatane tondrahen-orañe boak’ andikerañe i tane hitsaha’ areo ho tavaneñey,
Amma ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaki, ƙasa ce ta duwatsu da kwaruruka wadda ruwan sama ne yake jiƙe ta.
12 tane ambena’ Iehovà Andrianañahare’o. Toe ama’e nainai’e boa-taom-pak’ am-paran-taoñe o fihaino’ Iehovà Andrianañahare’oo.
Ƙasa ce da Ubangiji Allahnku yake lura da ita; idanun Ubangiji Allahnku yana a kai daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta.
13 Aa naho hambena’ areo ze hene lily lilieko anahareo androany—ty hikoko Iehovà Andrianañahare’ areo, hitoroñe aze an-kàampon’ arofo naho an-kaliforam-pañova—
Saboda haka in kun yi biyayya ga umarnan da nake ba ku a yau cikin aminci, kuna ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna kuma bauta masa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
14 le hoe ty tsara’e: Hampahaviako orañe an-tsa’e ty tane’ areo, i orañ’ aoloy naho i oram-para-ranoy, hahatontoña’o ty mahakama’o naho ty divai’o naho ty mena’o;
sai in aika da ruwan sama a ƙasarku a lokacinsa, ruwan saman bazara da kuma na kaka, don ku tattara hatsinku, sabon inabinku da kuma manku.
15 le hampitiriako ahetse o fiandraza’oo ho a o hare’oo, le hikama irehe vaho ho anjañe.
Zan tanadar da ciyawa a filaye don shanunku, za ku ci, ku kuma ƙoshi.
16 Aa le mitomira tsy ho fañahieñe añ’arofo, hitsile, hitoron-drahare tovo’e naho hiambaneañe,
Ku yi hankali, kada a ruɗe ku har ku bauta wa alloli, ku kuma yi musu sujada,
17 toly ndra hisolebotse ama’ areo ty haviñera’ Iehovà vaho hagabe’e o likerañeo tsy hizotsoa’ i orañey, tsy hahavokara’ i taney mahakama; le hikoromak’ aniany nahareo amy tane soa natolo’ Iehovà anahareoy.
don kada fushin Ubangiji yă ƙuna a kanku, yă rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.
18 Aa le ahajao añ’arofo’ areo ao naho am-pañova’ areo ao o taroko zao le rohizo am-pità’ areo ho viloñe, le reketo hoe alama añivom-pihaino’ areo.
Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.
19 Anaro amo amori’ areoo, le isaontsio naho miambesatse añ’anjomba’o ao naho midraidraitse an-dalañe ey naho màndre vaho mitroatse.
Ku koyar da su ga’ya’yanku, ku yi ta haddace su, sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
20 Isokiro an-tokonan-dalañ’ anjomba’o eo naho amo lalambei’oo,
Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,
21 soa te hitombo ty andro’ areo naho ty andro’ o ana’ areoo amy tane nifantà’ Iehovà aman-droae’ areo hatolo’e iareoy, ho mira amo andron-dikerañe ambone’ ty tane toy eñeo.
saboda kwanakinku da kwanakin’ya’yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, muddin sama tana bisa duniya.
22 Ie ambena’ areo an-kahimbañañe naho orihe’ areo ze hene lily lilieko anahareo, ty hikokoa’ areo Iehovà Andrianañahare’ areo naho hañavelo amo lala’e iabio vaho hitambozòtse ama’e,
In kuka lura, kuka kuma kiyaye dukan umarnai da nake ba ku, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma riƙe shi gam,
23 le hanoe’ Iehovà soik’ aolo’ areo mb’eo o fifeheañe iabio vaho ho tavane’ areo o foko jabajaba naho maozatse te ama’ areoo.
Ubangiji zai kori dukan waɗannan al’ummai a gabanku, za ku kuma kore al’umman da suka fi ku yawa da ƙarfi.
24 Le ho anahareo ze hene tane liàm-pandia’ areo; mifototse am-patrambey añe naho e Libanone naho boak’ amy oñey; le i oñe Peràtey pak’an-dRiak’ ahandrefañe añe ty ho efe-tane’ areo.
Duk inda tafin ƙafanku ya taka, zai zama naku; iyakarku zai kama daga hamadan Lebanon da kuma daga Kogin Yuferites zuwa Bahar Rum.
25 Tsy eo t’indaty hahafiatreatre ama’ areo amy te hampihembañeñe naho hampirevendreveñe’ Iehovà Andrianañahare’ areo ama’ areo ze hene tane ho liàm-pandia’ areo, amy nitsara’e ama’ areoy.
Babu mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku, zai sa razana da tsoronku a dukan ƙasar, a duk inda kuka tafi, kamar yadda ya alkawarta muku.
26 Ingo apoko añatrefa’ areo androany ty tata naho ty fatse:
Ga shi, a yau, ina sa a gabanku albarka da kuma la’ana,
27 i tatay, naho haoñe’ areo o lili’ Iehovà Andrianañahare’ areo lilieko androanio;
albarka in kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, da nake ba ku;
28 i fatsey, naho tsy haoñe’ areo o lili’ Iehovà Andrianañahare’ areoo, te mone mitsile hienga o lalañe andiliako androanio, hañoriha’ areo o ndrahare ila’e tsy nifohi’ areoo.
la’ana in ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma juya daga hanyar da na umarce ku, ta wurin bin waɗansu alloli, waɗanda ba ku sani ba.
29 Aa ie fa nasese’ Iehovà Andrianañahare’o mb’an-tane imoaha’o ho rambese’o ao, le havotra’o amy Vohin-Geriziy ty tata naho amy vohi-Ebàley ty fatse.
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da za ku shiga ku ci gādonta, sai ku yi shelar albarkun nan a dutsen Gerizim, ku kuma yi na la’ana a dutsen Ebal.
30 Aa tsy alafe’ Iardeney añe hao irezay, amy fitsofora’ i àndroy añey, an-tane’ o nte-Kanàne mimoneñe an-diolio tandrife i Gilgale añe añ’ ila’ o varo’ i Morèoo?
Waɗannan duwatsu biyu suna a hayin Urdun, yamma da hanya a ƙasar Kan’aniyawa mazaunan Araba, kusa da Gilgal wajajen manyan itatuwan More.
31 Fa hitsake Iardeney mb’eo nahareo hitavañe i tane atolo’ Iehovà Andrianañahare’ areoy, aa ie tavane’ areo le himoneña’ areo,
Kuna gab da ƙetare Urdun fa, ku shiga, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa’ad da kuka karɓe ta, kuka kuma zauna a can,
32 le hene ambeno naho oriho o fañè naho fepètse amantohako anahareo androanio.
ku tabbata kun yi biyayya da dukan ƙa’idodi, da kuma dokokin da nake sawa a gabanku a yau.