< 1 Korintiana 1 >
1 I Paoly, kinanjy ho Firàhe’ Iesoà Norizañey ami’ty satrin’ arofon’ Añahare, naho i Sostena rahalahy.
Bulus, wanda aka kira domin yă zama manzon Kiristi Yesu, bisa ga nufin Allah, da kuma ɗan’uwanmu Sostenes,
2 Ho ami’ty Fivorin’ Añahare e Korinto añe, ho amo nampiavahe’ Iesoà Norizañeio, o kinanjy ho noro’eo, miharo amy ze hene mpikanjy ty tahina’ Iesoà Talèntika Norizañey ndra aia aia, i Talè’ iareo naho antikañey.
Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, da waɗanda aka tsarkake cikin Kiristi Yesu, aka kuma kira domin su zama masu tsarki, tare da dukan waɗanda suke ko’ina da suke kiran sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, Ubangijinsu da kuma namu.
3 Hasoa ama’ areo naho fañanitsiñe boak’ aman’ Añahare Raen-tika naho Iesoà Talè Norizañey.
Alheri da salama daga Allah Ubanmu, da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
4 Andriañeko nainai’e t’i Andrianañahareko ty ama’ areo, ty hasoan’ Añahare natolotse anahareo am’ Iesoà Norizañeiy,
Ina gode wa Allah kullum dominku, saboda alherinsa da aka ba ku a cikin Kiristi Yesu.
5 ie ama’e ro niaboeñe amy ze lafi’e iaby an-tsara heneke naho an-kihitse fonitse,
Gama a cikinsa kuka sami wadata ta kowace hanya, a cikin dukan maganarku, da kuma cikin dukan saninku
6 ie niventèñe ama’ areo ty fitaroñañe i Norizañey.
gama shaidarmu game da Kiristi ta tabbata a cikinku.
7 Aa le tsy eo ty tsy eneñe ama’areo amo falalàñe iabio, hene rototse mitamà ty fiboaha’ i Talèntika Iesoà Norizañey.
Saboda haka, ba ku rasa kowace baiwa ta ruhaniya ba, yayinda kuke jira da marmari, saboda bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
8 Ie ty hampijadoñe anahareo sikal’ am-pigadoña’e añe, tsy hanan-kila amy andro’ i Talèntika Iesoà Norizañeiy.
Zai ƙarfafa ku har zuwa ƙarshe, domin ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
9 Migahiñe t’i Andrianañahare nikanjy anahareo ho amy fifampilongoañe amy Ana’e, Talèntika Iesoà Norizañeiy.
Allah, wanda ya kira ku zuwa ga zumunci tare da Ɗansa Yesu Kiristi Ubangijinmu, shi mai aminci ne.
10 Ie amy zao, mañosike anahareo iraho ry longo, amy tahina’ i Talèntika Iesoà Norizañeiy, ty hiharo saontsy, tsy hifampiriaria, f’ie ho fonireñe ho raike an-kilala naho raike an-tsafiry.
Ina roƙonku’yan’uwa, a cikin sunan Ubangijinmu Yesu Kiristi, dukanku ku yarda da juna, domin kada a sami tsattsaguwa a cikinku, domin kuma ku zama ɗaya, cikakku a cikin halinku da tunaninku.
11 O ry longo, fa natalili’ o mpiamy Kloaio amako t’ie amam-pifandierañe;
’Yan’uwana, waɗansu daga iyalin gidan Kulos sun gaya mini cewa, akwai faɗa a cikinku.
12 ty anoako zao, le te ao ty manao ty hoe: mpiamy Paoly iraho, le ty raike: amy Apolosy iraho, naho ty raike: amy Kefasy iraho, vaho ty ila’e: izaho amy Norizañey.
Abin da nake nufi shi ne, ɗaya daga cikinku na cewa, “Ni ina bin Bulus,” wani na cewa, “Ni ina bin Afollos,” wani kuma, “Ni ina bin Kefas,” har wa yau wani kuma, “Ni ina bin Kiristi.”
13 Aa vaho mitsiriaria hao i Norizañey? Pinèke ho anahareo hao t’i Paoly? He nalipotse ami’ty añara’ i Paoly?
Kiristi a rabe ne? Bulus ne aka gicciye dominku? An yi muku baftisma a cikin sunan Bulus ne?
14 Andriañeko t’i Andrianañahare te tsy ia ama’ areo ty nalipoko naho tsy i Krispo naho i Gaio avao,
Ina godiya domin ban yi wa wani baftisma a cikinku ba, sai dai Kirisbus da Gayus kaɗai.
15 ke eo ty hanao ty hoe t’ie nilipotse ami’ty añarako.
Don haka, ba wanda na iya cewa an yi muku baftisma a cikin sunana.
16 (Toe nalipoko ka o añ’anjomba’ i Stefanasio. Fa tsy apotako ze ila’e mete ho nampiliporeko.)
(I, na kuma yi wa iyalin gidan Istifanas baftisma, ban da wannan, ban tuna da wani da na yi masa baftisma ba.)
17 Toe tsy nañitrik’ ahy handipotse i Norizañey, fa ty hitaroñe i talili-soay, tsy an-dreha-kante kera hampikoaheñe i hatae’ ajale’ i Norizañeiy.
Gama Kiristi bai aike ni yin baftisma ba, sai dai wa’azin bishara ba da kalmomin hikimar mutum ba, domin kada gicciyen Kiristi ya rasa ikonsa.
18 Toe borosode amo mikoromakeo ty tsara’ i hatae’ ajaley, fe haozaran’ Añahare amantika rombaheñeo.
Gama saƙon gicciye wauta ne ga waɗanda suke hallaka, amma a gare mu, mu da ake ceto, ikon Allah ne.
19 Fa hoe ty pinatetse: Ho rotsaheko ty hihi’ o mahihitseo, naho hakafitse ty hilala’ o mahilalao.
Gama a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, basirar mai azanci kuma zan rikita shi.”
20 Aia ze o mahihitse zao? Aia ty mahay taratasy? Aia ty mpionim-piheotse ami’ty sa’ toy? Tsy nanoen’ Añahare hanèñe hao ty hilala’ ty tane toy? (aiōn )
Ina mai hikima? Ina mai zurfin bincike? Ina masana na wannan zamani? Ashe, Allah bai wofinta hikimar duniya ba? (aiōn )
21 Ie amy hihin’ Añaharey, kanao tsy nampahafohiñe an’ Andrianañahare ty hihi’ ty tane toy, le nisatrien’ Añahare ty handrombake ze mahafiantoke ami’ty hagegea’ i tsara taroñeñey.
Gama tun da a cikin hikimar Allah, duniya a cikin hikimarta ba tă san shi ba, Allah ya ji daɗin ceton waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin wautar wa’azin bishara.
22 Toe mipay viloñe o Jiosio, naho mitsoe-kihitse o Grikao;
Yahudawa suna so su ga alama, Hellenawa kuma suna neman hikima,
23 fe mitaroñe i Norizañe pinèkey zahay: ie boloko fitsikapia’ o Jiosio, naho hadagolàñe amo Grikao;
amma mu, muna wa’azin Kiristi wanda aka gicciye ne, wanda ya zama dutsen tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga Al’ummai,
24 fe amo kinanjio, he te Jiosy ke Grika, le ie ty haozaran’ Añahare naho ty hihin’ Añahare.
amma ga su waɗanda Allah ya kira, Yahudawa da Hellenawa, Kiristi ikon Allah ne, da kuma hikimar Allah.
25 Fa mahihitse te am’ondatio ty hagegean’ Añahare, naho maozatse te am’ondatio ty haifoifoan’ Añahare.
Gama wautar Allah ta fi hikimar mutum, kuma rashin ƙarfin Allah ya fi ƙarfin mutum.
26 Haraharao i nikanjiañe anahareoy: tsy nimaro ty nahihitse amo nofotseo, tsy nimaro ty fanalolahy, tsy niampeampe ty ana-donake.
’Yan’uwa, ku tuna yadda kuke sa’ad da aka kira ku. Babu masu hikima da yawa a cikinku, bisa ga ganin mutum; babu masu iko da yawa, babu masu martaba da yawa bisa ga haihuwa.
27 Fe jinobon’ Añahare o gege an-tane atoio hanalatse o mahilalao, naho jinobon’ Añahare o maifoifo’ ty tane toio hañameñatse o jomakeo;
Amma Allah ya zaɓi abubuwa masu wautata duniya, don yă kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abubuwa marasa ƙarfi na duniya, domin ya ba wa masu ƙarfi kunya.
28 jinobon’ Añahare o tsy vara’ ty tane toio naho o mavoiñeo vaho o atao tsy vente’eo, hampikoaha’e o raha eoo,
Ya zaɓi abubuwa marasa martaba na wannan duniya da kuma abubuwan da aka rena da abubuwan da ba a ɗauka a bakin kome ba, domin a wofinta abubuwan da ake ganinsu da daraja,
29 soa te tsy eo ty nofotse hirengevoke añatrefan’ Añahare.
domin kada wani ya yi taƙama a gabansa.
30 Ie ro maha am’ Iesoà Norizañey anahareo, Ie ty nanoan’ Añahare hihitse naho havantañañe naho fiavahañe vaho fijebañañe an-tika,
Saboda Allah ne kuke cikin Kiristi Yesu, shi wanda ya zama hikima a gare mu daga Allah. Kiristi shi ne adalcinmu, da tsarkinmu, da kuma fansarmu.
31 soa te, amy pinatetse ty hoe: Ze mirenge, Ee te i Talè ro firengea’e.
Saboda haka, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Duk wanda yake taƙama, ya yi taƙama a cikin Ubangiji.”