< Psalmorum 51 >

1 in finem psalmus David cum venit ad eum Nathan propheta quando intravit ad Bethsabee miserere mei Deus secundum magnam misericordiam tuam et secundum multitudinem miserationum tuarum dele iniquitatem meam
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
2 amplius lava me ab iniquitate mea et a peccato meo munda me
Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
3 quoniam iniquitatem meam ego cognosco et peccatum meum contra me est semper
Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
4 tibi soli peccavi et malum coram te feci ut iustificeris in sermonibus tuis et vincas cum iudicaris
Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
5 ecce enim in iniquitatibus conceptus sum et in peccatis concepit me mater mea
Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
6 ecce enim veritatem dilexisti incerta et occulta sapientiae tuae manifestasti mihi
Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
7 asparges me hysopo et mundabor lavabis me et super nivem dealbabor
Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
8 auditui meo dabis gaudium et laetitiam exultabunt ossa humiliata
Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
9 averte faciem tuam a peccatis meis et omnes iniquitates meas dele
Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
10 cor mundum crea in me Deus et spiritum rectum innova in visceribus meis
Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
11 ne proicias me a facie tua et spiritum sanctum tuum ne auferas a me
Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
12 redde mihi laetitiam salutaris tui et spiritu principali confirma me
Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
13 docebo iniquos vias tuas et impii ad te convertentur
Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
14 libera me de sanguinibus Deus Deus salutis meae exultabit lingua mea iustitiam tuam
Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
15 Domine labia mea aperies et os meum adnuntiabit laudem tuam
Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
16 quoniam si voluisses sacrificium dedissem utique holocaustis non delectaberis
Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
17 sacrificium Deo spiritus contribulatus cor contritum et humiliatum Deus non spernet
Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
18 benigne fac Domine in bona voluntate tua Sion et aedificentur muri Hierusalem
Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
19 tunc acceptabis sacrificium iustitiae oblationes et holocausta tunc inponent super altare tuum vitulos
Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.

< Psalmorum 51 >