< Proverbiorum 1 >

1 parabolae Salomonis filii David regis Israhel
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 ad sciendam sapientiam et disciplinam
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 ad intellegenda verba prudentiae et suscipiendam eruditionem doctrinae iustitiam et iudicium et aequitatem
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 ut detur parvulis astutia adulescenti scientia et intellectus
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 audiens sapiens sapientior erit et intellegens gubernacula possidebit
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 animadvertet parabolam et interpretationem verba sapientium et enigmata eorum
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 timor Domini principium scientiae sapientiam atque doctrinam stulti despiciunt
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 audi fili mi disciplinam patris tui et ne dimittas legem matris tuae
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 ut addatur gratia capiti tuo et torques collo tuo
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 fili mi si te lactaverint peccatores ne adquiescas
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 si dixerint veni nobiscum insidiemur sanguini abscondamus tendiculas contra insontem frustra
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 degluttiamus eum sicut infernus viventem et integrum quasi descendentem in lacum (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 omnem pretiosam substantiam repperiemus implebimus domos nostras spoliis
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 sortem mitte nobiscum marsuppium unum sit omnium nostrum
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 fili mi ne ambules cum eis prohibe pedem tuum a semitis eorum
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 pedes enim illorum ad malum currunt et festinant ut effundant sanguinem
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 frustra autem iacitur rete ante oculos pinnatorum
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 ipsique contra sanguinem suum insidiantur et moliuntur fraudes contra animas suas
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 sic semitae omnis avari animas possidentium rapiunt
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 sapientia foris praedicat in plateis dat vocem suam
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 in capite turbarum clamitat in foribus portarum urbis profert verba sua dicens
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 usquequo parvuli diligitis infantiam et stulti ea quae sibi sunt noxia cupiunt et inprudentes odibunt scientiam
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 convertimini ad correptionem meam en proferam vobis spiritum meum et ostendam verba mea
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 quia vocavi et rennuistis extendi manum meam et non fuit qui aspiceret
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 despexistis omne consilium meum et increpationes meas neglexistis
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 ego quoque in interitu vestro ridebo et subsannabo cum vobis quod timebatis advenerit
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 cum inruerit repentina calamitas et interitus quasi tempestas ingruerit quando venerit super vos tribulatio et angustia
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 tunc invocabunt me et non exaudiam mane consurgent et non invenient me
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 eo quod exosam habuerint disciplinam et timorem Domini non susceperint
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 nec adquieverint consilio meo et detraxerint universae correptioni meae
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 comedent igitur fructus viae suae suisque consiliis saturabuntur
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 aversio parvulorum interficiet eos et prosperitas stultorum perdet illos
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 qui autem me audierit absque terrore requiescet et abundantia perfruetur malorum timore sublato
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Proverbiorum 1 >