< Job 40 >

1 et adiecit Dominus et locutus est ad Iob
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
2 numquid qui contendit cum Deo tam facile conquiescit utique qui arguit Deum debet respondere ei
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
3 respondens autem Iob Domino dixit
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
4 qui leviter locutus sum respondere quid possum manum meam ponam super os meum
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
5 unum locutus sum quod utinam non dixissem et alterum quibus ultra non addam
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
6 respondens autem Dominus Iob de turbine ait
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7 accinge sicut vir lumbos tuos interrogabo te et indica mihi
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8 numquid irritum facies iudicium meum et condemnabis me ut tu iustificeris
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9 et si habes brachium sicut Deus et si voce simili tonas
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10 circumda tibi decorem et in sublime erigere et esto gloriosus et speciosis induere vestibus
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11 disperge superbos furore tuo et respiciens omnem arrogantem humilia
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12 respice cunctos superbos et confunde eos et contere impios in loco suo
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13 absconde eos in pulvere simul et facies eorum demerge in foveam
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
14 et ego confitebor quod salvare te possit dextera tua
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
15 ecce Behemoth quem feci tecum faenum quasi bos comedet
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
16 fortitudo eius in lumbis eius et virtus illius in umbilicis ventris eius
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
17 constringit caudam suam quasi cedrum nervi testiculorum eius perplexi sunt
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
18 ossa eius velut fistulae aeris cartilago illius quasi lamminae ferreae
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
19 ipse principium est viarum Dei qui fecit eum adplicabit gladium eius
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
20 huic montes herbas ferunt omnes bestiae agri ludent ibi
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
21 sub umbra dormit in secreto calami et locis humentibus
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
22 protegunt umbrae umbram eius circumdabunt eum salices torrentis
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
23 ecce absorbebit fluvium et non mirabitur habet fiduciam quod influat Iordanis in os eius
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
24 in oculis eius quasi hamo capiet eum et in sudibus perforabit nares eius
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?

< Job 40 >