< Job 3 >

1 post haec aperuit Iob os suum et maledixit diei suo
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
2 et locutus est
Ayuba ya ce,
3 pereat dies in qua natus sum et nox in qua dictum est conceptus est homo
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4 dies ille vertatur in tenebras non requirat eum Deus desuper et non inlustret lumine
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5 obscurent eum tenebrae et umbra mortis occupet eum caligo et involvatur amaritudine
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6 noctem illam tenebrosus turbo possideat non conputetur in diebus anni nec numeretur in mensibus
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7 sit nox illa solitaria nec laude digna
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8 maledicant ei qui maledicunt diei qui parati sunt suscitare Leviathan
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9 obtenebrentur stellae caligine eius expectet lucem et non videat nec ortum surgentis aurorae
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10 quia non conclusit ostia ventris qui portavit me nec abstulit mala ab oculis meis
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11 quare non in vulva mortuus sum egressus ex utero non statim perii
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12 quare exceptus genibus cur lactatus uberibus
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13 nunc enim dormiens silerem et somno meo requiescerem
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14 cum regibus et consulibus terrae qui aedificant sibi solitudines
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15 aut cum principibus qui possident aurum et replent domos suas argento
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16 aut sicut abortivum absconditum non subsisterem vel qui concepti non viderunt lucem
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
17 ibi impii cessaverunt a tumultu et ibi requieverunt fessi robore
A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
18 et quondam vincti pariter sine molestia non audierunt vocem exactoris
Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
19 parvus et magnus ibi sunt et servus liber a domino suo
Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
20 quare data est misero lux et vita his qui in amaritudine animae sunt
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21 qui expectant mortem et non venit quasi effodientes thesaurum
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22 gaudentque vehementer cum invenerint sepulchrum
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23 viro cuius abscondita est via et circumdedit eum Deus tenebris
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24 antequam comedam suspiro et quasi inundantes aquae sic rugitus meus
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25 quia timor quem timebam evenit mihi et quod verebar accidit
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26 nonne dissimulavi nonne silui nonne quievi et venit super me indignatio
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”

< Job 3 >