< Psalmorum 25 >

1 In finem. Psalmus David. Ad te, Domine, levavi animam meam:
Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
2 Deus meus, in te confido; non erubescam.
A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
3 Neque irrideant me inimici mei: etenim universi qui sustinent te, non confundentur.
Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
4 Confundantur omnes iniqua agentes supervacue. Vias tuas, Domine, demonstra mihi, et semitas tuas edoce me.
Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
5 Dirige me in veritate tua, et doce me, quia tu es Deus salvator meus, et te sustinui tota die.
ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
6 Reminiscere miserationum tuarum, Domine, et misericordiarum tuarum quæ a sæculo sunt.
Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
7 Delicta juventutis meæ, et ignorantias meas, ne memineris. Secundum misericordiam tuam memento mei tu, propter bonitatem tuam, Domine.
Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
8 Dulcis et rectus Dominus; propter hoc legem dabit delinquentibus in via.
Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
9 Diriget mansuetos in judicio; docebit mites vias suas.
Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
10 Universæ viæ Domini, misericordia et veritas, requirentibus testamentum ejus et testimonia ejus.
Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
11 Propter nomen tuum, Domine, propitiaberis peccato meo; multum est enim.
Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
12 Quis est homo qui timet Dominum? legem statuit ei in via quam elegit.
To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
13 Anima ejus in bonis demorabitur, et semen ejus hæreditabit terram.
Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
14 Firmamentum est Dominus timentibus eum; et testamentum ipsius ut manifestetur illis.
Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
15 Oculi mei semper ad Dominum, quoniam ipse evellet de laqueo pedes meos.
Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
16 Respice in me, et miserere mei, quia unicus et pauper sum ego.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
17 Tribulationes cordis mei multiplicatæ sunt: de necessitatibus meis erue me.
Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
18 Vide humilitatem meam et laborem meum, et dimitte universa delicta mea.
Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
19 Respice inimicos meos, quoniam multiplicati sunt, et odio iniquo oderunt me.
Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
20 Custodi animam meam, et erue me: non erubescam, quoniam speravi in te.
Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
21 Innocentes et recti adhæserunt mihi, quia sustinui te.
Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
22 Libera, Deus, Israël ex omnibus tribulationibus suis.
Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!

< Psalmorum 25 >