< Salmi 81 >
1 [Salmo] di Asaf, [dato] al Capo de' Musici, sopra Ghittit CANTATE lietamente a Dio nostra forza; Date grida di allegrezza all'Iddio di Giacobbe.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
2 Prendete a salmeggiare, ed aggiugnete[vi] il tamburo, La cetera dilettevole, col saltero.
Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
3 Sonate colla tromba alle calendi, Nella nuova luna, al giorno della nostra festa.
Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
4 Perciocchè questo [è] uno statuto [dato] ad Israele, Una legge dell'Iddio di Giacobbe.
wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
5 Egli lo costituì [per] una testimonianza in Giuseppe, Dopo ch'egli fu uscito fuori contro al paese di Egitto; [Allora che] io udii un linguaggio [che] io non intendeva.
Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
6 Io ho ritratte, [dice Iddio], le sue spalle da' pesi; Le sue mani si son dipartite dalle corbe.
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
7 [O popol mio], tu gridasti [essendo] in distretta, ed io te [ne] trassi fuori; Io ti risposi, [stando] nel nascondimento del tuono; Io ti provai alle acque di Meriba. (Sela)
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
8 Io [ti dissi]: Ascolta, popol mio, ed io ti farò le mie protestazioni; O Israele, attendessi tu pure a me!
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9 Non siavi fra te alcun dio strano, E non adorare alcun dio forestiere.
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10 Io [sono] il Signore Iddio tuo, che ti ho tratto fuor del paese di Egitto; Allarga pur la tua bocca, ed io l'empierò.
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11 Ma il mio popolo non ha atteso alla mia voce; Ed Israele non mi ha acconsentito.
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12 Onde io li ho abbandonati alla durezza del cuor loro; [Acciocchè] camminino secondo i lor consigli.
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13 Oh! avesse pure ubbidito il mio popolo, [E] fosse Israele camminato nelle mie vie!
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14 Io avrei in uno stante abbattuti i lor nemici, Ed avrei rivolta la mia mano contro a' loro avversari.
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15 Quelli che odiano il Signore si sarebbero infinti inverso loro; E il tempo loro sarebbe durato in perpetuo.
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16 E [Iddio] li avrebbe cibati di grascia di frumento; E dalla roccia, [dice egli], io ti avrei satollato di miele.
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”