< Salmi 80 >

1 Salmo di Asaf, [dato] al Capo de' Musici sopra Sosannim-edut O PASTORE d'Israele, che guidi Giuseppe come una greggia, Porgi gli orecchi; Tu che siedi sopra i Cherubini, Apparisci in gloria.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
2 Eccita la tua potenza davanti ad Efraim, ed a Beniamino, ed a Manasse; E vieni a nostra salute.
a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
3 O Dio, ristoraci; E fa' risplendere il tuo volto, e noi saremo salvati.
Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
4 O Signore Iddio degli eserciti, Infino a quando fumerai tu contro all'orazione del tuo popolo?
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
5 Tu li hai cibati di pan di pianto, E li hai abbeverati di lagrime a larga misura.
Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
6 Tu ci hai posti [in] contesa co' nostri vicini; E i nostri nemici si fanno beffe [di noi].
Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
7 O Dio degli eserciti, ristoraci; E fa' risplendere il tuo volto, e noi saremo salvati.
Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
8 Tu avevi trasportata di Egitto una vigna; Tu avevi cacciate le nazioni, e l'avevi piantata.
Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
9 Tu avevi sgomberato davanti a lei [il suo luogo]; Ed avevi fatto ch'ella aveva messe radici, ed aveva empiuta la terra.
Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
10 I monti erano coperti della sua ombra, E i suoi tralci [erano come] cedri altissimi.
Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
11 Aveva gettati i suoi rami infino al mare, E i suoi rampolli infino al fiume.
Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
12 Perchè hai tu rotte le sue chiusure, Sì che tutti i passanti l'han vendemmiata?
Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
13 I cinghiali l'hanno guastata, E le fiere della campagna l'hanno pascolata.
Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
14 O Dio degli eserciti, rivolgiti, ti prego; Riguarda dal cielo, e vedi, e visita questa vigna.
Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
15 E le piante che la tua destra aveva piantate, E le propaggini [che] tu ti avevi fortificate.
saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
16 [Quella è] arsa col fuoco, ella è ricisa fino dal piè; [Quelle] periscono per lo sgridar della tua faccia.
An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
17 Sia la tua mano sopra l'uomo della tua destra, Sopra il figliuol dell'uomo [che] tu ti avevi fortificato.
Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
18 E noi non ci trarremo indietro da te; Mantienci in vita, e noi invocheremo il tuo Nome.
Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
19 O Signore Iddio degli eserciti, ristoraci; Fa' risplendere il tuo volto, e noi saremo salvati.
Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.

< Salmi 80 >