< תהילים 106 >

הללו-יה הודו ליהוה כי-טוב-- כי לעולם חסדו 1
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
מי--ימלל גבורות יהוה ישמיע כל-תהלתו 2
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
אשרי שמרי משפט עשה צדקה בכל-עת 3
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
זכרני יהוה ברצון עמך פקדני בישועתך 4
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
לראות בטובת בחיריך-- לשמח בשמחת גויך להתהלל עם-נחלתך 5
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
חטאנו עם-אבותינו העוינו הרשענו 6
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
אבותינו במצרים לא-השכילו נפלאותיך-- לא זכרו את-רב חסדיך וימרו על-ים בים-סוף 7
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
ויושיעם למען שמו-- להודיע את-גבורתו 8
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
ויגער בים-סוף ויחרב ויוליכם בתהמות כמדבר 9
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
ויושיעם מיד שונא ויגאלם מיד אויב 10
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
ויכסו-מים צריהם אחד מהם לא נותר 11
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
ויאמינו בדבריו ישירו תהלתו 12
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
מהרו שכחו מעשיו לא-חכו לעצתו 13
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
ויתאוו תאוה במדבר וינסו-אל בישימון 14
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
ויתן להם שאלתם וישלח רזון בנפשם 15
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
ויקנאו למשה במחנה לאהרן קדוש יהוה 16
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
תפתח-ארץ ותבלע דתן ותכס על-עדת אבירם 17
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
ותבער-אש בעדתם להבה תלהט רשעים 18
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
יעשו-עגל בחרב וישתחוו למסכה 19
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
וימירו את-כבודם בתבנית שור אכל עשב 20
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
שכחו אל מושיעם-- עשה גדלות במצרים 21
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
נפלאות בארץ חם נוראות על-ים-סוף 22
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
ויאמר להשמידם לולי משה בחירו-- עמד בפרץ לפניו להשיב חמתו מהשחית 23
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
וימאסו בארץ חמדה לא-האמינו לדברו 24
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
וירגנו באהליהם לא שמעו בקול יהוה 25
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
וישא ידו להם-- להפיל אותם במדבר 26
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
ולהפיל זרעם בגוים ולזרותם בארצות 27
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
ויצמדו לבעל פעור ויאכלו זבחי מתים 28
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
ויכעיסו במעלליהם ותפרץ-בם מגפה 29
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
ויעמד פינחס ויפלל ותעצר המגפה 30
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
ותחשב לו לצדקה לדר ודר עד-עולם 31
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
ויקציפו על-מי מריבה וירע למשה בעבורם 32
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
כי-המרו את-רוחו ויבטא בשפתיו 33
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
לא-השמידו את-העמים-- אשר אמר יהוה להם 34
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
ויתערבו בגוים וילמדו מעשיהם 35
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
ויעבדו את-עצביהם ויהיו להם למוקש 36
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
ויזבחו את-בניהם ואת-בנותיהם-- לשדים 37
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
וישפכו דם נקי דם-בניהם ובנותיהם-- אשר זבחו לעצבי כנען ותחנף הארץ בדמים 38
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
ויטמאו במעשיהם ויזנו במעלליהם 39
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
ויחר-אף יהוה בעמו ויתעב את-נחלתו 40
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
ויתנם ביד-גוים וימשלו בהם שנאיהם 41
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
וילחצום אויביהם ויכנעו תחת ידם 42
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
פעמים רבות יצילם והמה ימרו בעצתם וימכו בעונם 43
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
וירא בצר להם-- בשמעו את-רנתם 44
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
ויזכר להם בריתו וינחם כרב חסדו 45
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
ויתן אותם לרחמים-- לפני כל-שוביהם 46
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
הושיענו יהוה אלהינו וקבצנו מן-הגוים להדות לשם קדשך להשתבח בתהלתך 47
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
ברוך יהוה אלהי ישראל מן-העולם ועד העולם-- ואמר כל-העם אמן הללו-יה 48
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.

< תהילים 106 >