< תהילים 106 >
הללו-יה הודו ליהוה כי-טוב-- כי לעולם חסדו | 1 |
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
מי--ימלל גבורות יהוה ישמיע כל-תהלתו | 2 |
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
אשרי שמרי משפט עשה צדקה בכל-עת | 3 |
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
זכרני יהוה ברצון עמך פקדני בישועתך | 4 |
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
לראות בטובת בחיריך-- לשמח בשמחת גויך להתהלל עם-נחלתך | 5 |
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
חטאנו עם-אבותינו העוינו הרשענו | 6 |
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
אבותינו במצרים לא-השכילו נפלאותיך-- לא זכרו את-רב חסדיך וימרו על-ים בים-סוף | 7 |
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
ויושיעם למען שמו-- להודיע את-גבורתו | 8 |
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
ויגער בים-סוף ויחרב ויוליכם בתהמות כמדבר | 9 |
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
ויושיעם מיד שונא ויגאלם מיד אויב | 10 |
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
ויכסו-מים צריהם אחד מהם לא נותר | 11 |
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
ויאמינו בדבריו ישירו תהלתו | 12 |
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
מהרו שכחו מעשיו לא-חכו לעצתו | 13 |
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
ויתאוו תאוה במדבר וינסו-אל בישימון | 14 |
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
ויתן להם שאלתם וישלח רזון בנפשם | 15 |
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
ויקנאו למשה במחנה לאהרן קדוש יהוה | 16 |
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
תפתח-ארץ ותבלע דתן ותכס על-עדת אבירם | 17 |
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
ותבער-אש בעדתם להבה תלהט רשעים | 18 |
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
יעשו-עגל בחרב וישתחוו למסכה | 19 |
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
וימירו את-כבודם בתבנית שור אכל עשב | 20 |
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
שכחו אל מושיעם-- עשה גדלות במצרים | 21 |
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
נפלאות בארץ חם נוראות על-ים-סוף | 22 |
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
ויאמר להשמידם לולי משה בחירו-- עמד בפרץ לפניו להשיב חמתו מהשחית | 23 |
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
וימאסו בארץ חמדה לא-האמינו לדברו | 24 |
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
וירגנו באהליהם לא שמעו בקול יהוה | 25 |
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
וישא ידו להם-- להפיל אותם במדבר | 26 |
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
ולהפיל זרעם בגוים ולזרותם בארצות | 27 |
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
ויצמדו לבעל פעור ויאכלו זבחי מתים | 28 |
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
ויכעיסו במעלליהם ותפרץ-בם מגפה | 29 |
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
ויעמד פינחס ויפלל ותעצר המגפה | 30 |
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
ותחשב לו לצדקה לדר ודר עד-עולם | 31 |
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
ויקציפו על-מי מריבה וירע למשה בעבורם | 32 |
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
כי-המרו את-רוחו ויבטא בשפתיו | 33 |
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
לא-השמידו את-העמים-- אשר אמר יהוה להם | 34 |
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
ויתערבו בגוים וילמדו מעשיהם | 35 |
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
ויעבדו את-עצביהם ויהיו להם למוקש | 36 |
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
ויזבחו את-בניהם ואת-בנותיהם-- לשדים | 37 |
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
וישפכו דם נקי דם-בניהם ובנותיהם-- אשר זבחו לעצבי כנען ותחנף הארץ בדמים | 38 |
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
ויטמאו במעשיהם ויזנו במעלליהם | 39 |
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
ויחר-אף יהוה בעמו ויתעב את-נחלתו | 40 |
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
ויתנם ביד-גוים וימשלו בהם שנאיהם | 41 |
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
וילחצום אויביהם ויכנעו תחת ידם | 42 |
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
פעמים רבות יצילם והמה ימרו בעצתם וימכו בעונם | 43 |
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
וירא בצר להם-- בשמעו את-רנתם | 44 |
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
ויזכר להם בריתו וינחם כרב חסדו | 45 |
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
ויתן אותם לרחמים-- לפני כל-שוביהם | 46 |
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
הושיענו יהוה אלהינו וקבצנו מן-הגוים להדות לשם קדשך להשתבח בתהלתך | 47 |
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
ברוך יהוה אלהי ישראל מן-העולם ועד העולם-- ואמר כל-העם אמן הללו-יה | 48 |
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.