< תהילים 105 >

הודו ליהוה קראו בשמו הודיעו בעמים עלילותיו 1
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
שירו-לו זמרו-לו שיחו בכל-נפלאותיו 2
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
התהללו בשם קדשו ישמח לב מבקשי יהוה 3
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
דרשו יהוה ועזו בקשו פניו תמיד 4
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
זכרו--נפלאותיו אשר-עשה מפתיו ומשפטי-פיו 5
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
זרע אברהם עבדו בני יעקב בחיריו 6
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
הוא יהוה אלהינו בכל-הארץ משפטיו 7
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
זכר לעולם בריתו דבר צוה לאלף דור 8
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
אשר כרת את-אברהם ושבועתו לישחק 9
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
ויעמידה ליעקב לחק לישראל ברית עולם 10
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
לאמר--לך אתן את-ארץ-כנען חבל נחלתכם 11
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
בהיותם מתי מספר כמעט וגרים בה 12
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
ויתהלכו מגוי אל-גוי מממלכה אל-עם אחר 13
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
לא-הניח אדם לעשקם ויוכח עליהם מלכים 14
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
אל-תגעו במשיחי ולנביאי אל-תרעו 15
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
ויקרא רעב על-הארץ כל-מטה-לחם שבר 16
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
שלח לפניהם איש לעבד נמכר יוסף 17
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
ענו בכבל רגליו (רגלו) ברזל באה נפשו 18
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
עד-עת בא-דברו-- אמרת יהוה צרפתהו 19
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
שלח מלך ויתירהו משל עמים ויפתחהו 20
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
שמו אדון לביתו ומשל בכל-קנינו 21
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
לאסר שריו בנפשו וזקניו יחכם 22
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
ויבא ישראל מצרים ויעקב גר בארץ-חם 23
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
ויפר את-עמו מאד ויעצמהו מצריו 24
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
הפך לבם לשנא עמו להתנכל בעבדיו 25
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
שלח משה עבדו אהרן אשר בחר-בו 26
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
שמו-בם דברי אתותיו ומפתים בארץ חם 27
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
שלח חשך ויחשך ולא-מרו את-דבריו (דברו) 28
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
הפך את-מימיהם לדם וימת את-דגתם 29
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
שרץ ארצם צפרדעים בחדרי מלכיהם 30
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
אמר ויבא ערב כנים בכל-גבולם 31
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
נתן גשמיהם ברד אש להבות בארצם 32
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
ויך גפנם ותאנתם וישבר עץ גבולם 33
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
אמר ויבא ארבה וילק ואין מספר 34
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
ויאכל כל-עשב בארצם ויאכל פרי אדמתם 35
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
ויך כל-בכור בארצם ראשית לכל-אונם 36
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
ויוציאם בכסף וזהב ואין בשבטיו כושל 37
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
שמח מצרים בצאתם כי-נפל פחדם עליהם 38
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
פרש ענן למסך ואש להאיר לילה 39
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
שאל ויבא שלו ולחם שמים ישביעם 40
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
פתח צור ויזובו מים הלכו בציות נהר 41
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
כי-זכר את-דבר קדשו את-אברהם עבדו 42
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
ויוצא עמו בששון ברנה את-בחיריו 43
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
ויתן להם ארצות גוים ועמל לאמים יירשו 44
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
בעבור ישמרו חקיו-- ותורתיו ינצרו הללו-יה 45
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< תהילים 105 >