< Ieremia 33 >

1 A LAILA, hiki lua mai la ka ole lo a Iehova io Ieremia la, i kona paa ana iloko o ka pahale o ka halepaahao, i mai la,
Yayinda Irmiya yana a tsare a sansanin matsara, sai maganar Ubangiji ta zo masa sau na biyu cewa,
2 Penei ka olelo ana mai a Iehova, a ka mea hana, o Iehova ka mea i hoonohonoho ia mea, i mea e paa ai; o Iehova kona inoa;
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci duniya, Ubangiji wanda ya siffanta ta ya kuma kafa ta, Ubangiji ne sunansa.
3 E hea mai oe ia'u, a e o aku no wau ia oe, a e hoike aku ia oe i na mea nui a paakiki, au i ike ole ai.
‘Kira gare ni zan kuwa amsa maka in kuma faɗa maka manyan abubuwan da ba a iya kaiwa, da ba ka sani ba.’
4 No ka mea, ke olelo mai nei o Iehova, ke Akua o ka Iseraela penei, no na hale o keia kulanakauhale, a no na hale o na'lii o ka Iuda, na mea i hoohioloia e na puu, a me ka pahikaua:
Gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana cewa game da gidaje a wannan birni da fadodin Yahuda da aka rurrushe domin a yi amfani da su a kan mahaurai da kuma takobi
5 Ke hele mai nei lakou e kaua me ko Kaledea, he mea nae ia e hoopiha ai ia lakou i na kupapau o na kanaka, ka poe a'u i luku ai i ko'u huhu, a i ko'u ukiuki, a ua huna hoi au i ko'u maka mai keia kulanakauhale aku, no ka hewa a pau o lakou.
a yaƙi da Babiloniyawa. ‘Za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata. Zan ɓoye fuskata wa wannan birni saboda dukan muguntarsu.
6 Aia hoi, e lawe mai no au io na la i ka wahi, a me ka mea e ola'i, a e hoola no wau ia lakou, a e hoike aku au ia lakou i ka maluhia nui, me ka oiaio.
“‘Duk da haka, zan kawo lafiya da warkarwa gare ta; zan warkar da mutanena in kuma wadata su da salama da zama lafiya.
7 A e hoihoi mai au i ke pio ana o Iuda, a me ke pio ana o ka Iseraela, a kukulu no au ia lakou, e like me ka wa mamua.
Zan komo da Yahuda da Isra’ila daga bauta zan kuma sāke gina su kamar yadda suke a dā.
8 A e hoomaemae au ia lakou i ko lakou hewa a pau a lakou i hana hewa mai ai ia'u: a e kala no hoi au i ko lakou hala a pau a lakou i lawehala'i, a kipi mai hoi ia'u.
Zan tsarkake su daga dukan zunubin da suka yi mini zan kuma gafarta musu dukan zunubansu na yin mini tawaye.
9 A e lilo mai ia ia'u i inoa e olioli ai, no ka maikai, a no ka nani imua o na lahuikanaka a pau o ka honua, ka poe e lohe ana i ka maikai a pau a'u e hana aku ai ia lakou. A e makau auanei lakou a e haalulu hoi no ka maikai a pau, a no ka pomaikai a pau a'u e haawi aku ai ia wahi.
Sa’an nan birnin nan za tă sa in zama sananne, farin ciki, yabo da girma a gaban dukan al’ummai a duniya da suka ji abubuwa masu kyau da na yi mata; za su kuma yi mamaki su kuma yi rawan jiki saboda yalwar wadata da salamar da na ba ta.’
10 Ke olelo mai nei o Iehova; Ma keia wahi, kahi a oukou i olelo ai, ua mehameha, aohe kanaka, aohe holoholona, ma na kulanakauhale o ka Iuda, a ma na alanui o Ierusalema, ua mehameha, aohe kanaka, aohe mea nana e noho, aohe holoholona;
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Kuna cewa game da wannan wuri, “Kango ne, babu mutane ko dabbobi.” Duk da haka a cikin garuruwan Yahuda da titunan Urushalima da aka yashe, inda ba mutane ko dabbobi, za a sāke jin
11 E lohe hou ia no ka leo o ka olioli, a me ka leo o ka hauoli; ka leo o ke kanemare, a me ka leo o ka wahinemare; ka leo hoi o ka poe e olelo ana, E hoomaikai ia Iehova o na kaua, no ka mea, ua maikai o Iehova no kona lokomaikai mau loa; o ko ka poe hoi e lawe ana i na mohai hoomana iloko o ka hale o Iehova. No ka mea, e hoihoi no wau i na pio o ka aina, e like me ka wa mamua, wahi a Iehova.
sowa ta farin ciki da murna, muryoyin amarya da na ango, da muryoyin waɗanda suka kawo hadayun salama a gidan Ubangiji suna cewa, “‘“Ku yi godiya ga Ubangiji Maɗaukaki, gama Ubangiji mai alheri ne; ƙaunarsa za tă dawwama har abada.” Gama zan mayar da wadatar ƙasar kamar yadda suke a dā,’ in ji Ubangiji.
12 Ke olelo mai nei o Iehova o na kaua penei; Ma keia wahi mehameha, kanaka ole, a holoholona ole, a ma kona mau kulanakauhale a pau, e loaa hou no kahi noho no na kahuhipa, e hoomoe ana i ka lakou poe hipa.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, ‘A wannan wuri, kango da babu mutane ko dabbobi, cikin dukan garuruwansa za a sāke kasance da wurin kiwo don makiyaya su hutar da garkunansu.
13 Ma na kulanakauhale o na mauna, a ma na kulanakauhale o ke awawa, a ma na kulanakauhale o ke kukuluhema, a ma ka aina o ka Beniamina, a ma na wahi e puni ana ia Ierusalema, a ma na kulanakauhale o ka Iuda, e hele hou ae no na poe hipa malalo iho o ka lima o ka mea helu, wabi a Iehova.
A cikin garuruwan ƙasar tudu, garuruwan yammancin gindin dutse da na Negeb, a yankin Benyamin, a cikin ƙauyuka kewayen Urushalima da kuma a cikin garuruwan Yahuda, garkuna za su sāke bi a ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,’ in ji Ubangiji.
14 Aia hoi, e hiki mai ana no na la, wahi a Iehova, e hana aku ai au i ka mea maikai a'u i olelo ai i ko ka hale o ka Iseraela, a i ko ka hale o ka Iuda.
“‘Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan cika alkawarin alheri da na yi wa gidan Isra’ila da kuma gidan Yahuda.
15 Ia mau la, a ia manawa, na'u no e houlu no Davida i ka Lala o ka pono; a nana no e hana i ka hoopono, a me ka pololei ma ka aina.
“‘A waɗannan kwanaki da kuma a wannan lokaci zan tā da Reshe mai adalci daga zuriyar Dawuda; zai yi abin da yake daidai da kuma gaskiya a ƙasar.
16 Ia mau la, e hoolaia o ka Iuda, a e noho maluhia hoi o ka Ierusalema, a o kona e kapaia'i, O Iehova ko kakou pono.
A kwanakin nan zan ceci Yahuda Urushalima kuma za tă zauna lafiya. Sunan da za a kira ta shi ne, Ubangiji Adalcinmu.’
17 No ka mea, ke olelo mai nei o Iehova penei; Aole e nelo o Davida i ke kanaka e noho ma ka nohoalii o ko ka hale o ka Iseraela.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra’ila ba,
18 Aole hoi e nele imua o'u o na kahuna, o na Levi i ke kanaka e kaumaha aku i ka mohaikuni, a e kuni aku i na mohai makana, a e hana i ka mohai mau.
ba kuwa firistoci waɗanda suke Lawiyawa za su rasa mutumin da zai ci gaba da tsaya a gabana don miƙa hadayun ƙonawa, ya ƙona hadayun hatsi ya kuma miƙa sadakoki ba.’”
19 Alaila hiki mai ka olelo a Iehova io Ieremia la, i mai la,
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
20 Ke i mai nei o Iehova penei; Ina hiki ia oukou ke uhai i ka'u berita o ke ao, a me ka'u berita o ka po, i ole ai he ao, a he po i ko laua manawa;
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ka tā da alkawarina na rana da kuma alkawarina na dare, har dare da rana ba za su ƙara bayyana a ƙayyadaddun lokutansu ba,
21 Alaila e uhaiia no hoi ka'u berita me Davida ka'u kauwa, i loaa ole ia ia ke keiki, e noho aupuni maluna o kona nohoalii; a me na Levi, ka poe kahuna, ko'u poe lawelawe.
to, sai a tā da alkawarina da Dawuda bawana da alkawarina da Lawiyawan da suke firistoci masu hidima a gabana, Dawuda kuma ba zai ƙara kasance da zuriyar da za tă yi mulki.
22 E like hoi me na hoku o ka lani hiki ole ke helu, a me ke one o ke kai hiki ole ke ana; pela no wau e hoonui ai i ka pua a Davida, a ka'u kauwa, a me na Levi, ka poe lawelawe na'u.
Zan sa zuriyar Dawuda bawana da kuma Lawiyawan da suke hidima a gabana su yi yawa kamar taurarin sararin sama da kuma yashin bakin tekun da ba a iya ƙidaya.’”
23 Alaila hiki mai ka olelo a Iehova io Ieremia la, i mai la,
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
24 Aole anei oe i noonoo i ka mea a keia poe kanaka i olelo ai, i ka i ana'e, O na ohana elua a Iehova i koho ai, ua hoole oia ia lakou? Pela lakou i hoowahawaha'i i ko'u poe kanaka, i pau ae ko lakou noho lahuikanaka ana imua o lakou.
“Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
25 Ke i mai nei o Iehova penei; Ina aohe a'u berita me ke ao a me ka po, aole hoi i kau i na kanawai o ka lani a me ka honua;
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
26 Alaila, e hoole no wau i ka pua a Iakoba, a me Davida ka'u kauwa, aole hoi e lawe i kana mamo i alii maluna o ka pua a Aberahama, a me Isaaka, a me Iakoba; no ka mea, e hoihoi no wau i ko lakou pio ana, a e lokomaikai aku no hoi au ia lakou.
to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’”

< Ieremia 33 >