< Iakobo 1 >

1 NA lakobo, he kauwa na ke Akua, a me ka Haku o Iesu Kristo, i ka poe ohana he umi a me kumamalua i hoopuehuia, Aloha oukou.
Yakubu, bawan Allah, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu, zuwa ga kabilun nan goma sha biyu da suke warwatse: ina gaishe ku.
2 E na hoahanau o'u, e manao oukou, he mea olioli wale no, ke loohia oukou e kela mea keia mea e hoao mai ai;
Ku dauke su duka da farin ciki, 'yan'uwana, duk sa'adda kuke fuskantar jarabobi.
3 Ua ike no hoi oukou, o ka hoao ana mai i ko oukou manaoio, oia ka mea e mahuahua'i ke ahonui.
Ku sani cewa gwajin banskiyar ku ta kan haifi jimiri.
4 E hoomau oukou ma ka mea ku pono i ke ahonui, i lako oukou, a i hemolele hoi, aole wahi hemahema iki.
Bari jimiri ya cika aikin sa, domin ku kai ga cikakken girma kuma ku kammalu, domin kada ku rasa komai.
5 Ina i nele kekahi o oukou i ke akamai, e noi aku oia i ke Akua i ka mea i haawi lokomaikai mai no na mea a pau me ka hoino ole mai, a e haawiia mai no ia nona.
Amma idan waninku yana bukatar hikima, sai ya roki Allah, wanda yake bayarwa a yalwace, ba tare da gori ba ga duk wanda ya roke shi, zai kuwa ba shi.
6 Aka, e noi aku oia me ka manaoio, aole me ke kanalua; no ka mea, o ka mea e kanalua ana, ua like no ia me ka ale o ke kai i puhiia e ka makani a kupikipikio.
Amma fa sai ya roka da banskiya ba tare da shakka ba, don mai shakka kamar rakumin ruwan teku yake, wanda iska take korarwa tana tunkudawa.
7 Mai manao ia kanaka, e loaa mai ia ia kekahi mea na ka Haku mai.
Tilas ne wannan mutum kada ya yi tunanin zai karbi wani abu a wurin Ubangiji.
8 O ke kanaka i lolelua ka naau, ua lauwili oia i kona mau aoao a pau.
Irin wannan mutumin mai zuciya biyu ne, mara tsai da hankali a dukan hanyoyin sa.
9 O ka hoahanau haahaa, e hauoli ia i kona hookiekieia.
Bari dan'uwa matalauci ya yi takama da matsayin sa babba,
10 A o ka mea waiwai hoi, i kona hoohaahaaia; no ka mea, e like me ka pua o ka nahelehele e mae wale ana ia.
amma mutum mai arziki kuma a kaskantaccen matsayin sa, gama zai shude kamar furen ciyawa na jeji.
11 No ka mea, i ke kau ana mai o ka la me ka wela nui, aole emo a hoomaloo iho la no ia i ka nahelehele, a haule iho la kona pua, a pau ae la ka nani o kona ano: pela no e mae ai ka mea waiwai i kona aoao iho.
Domin rana na bullowa da zafi mai konarwa kuma ya busar da ciyawa. Furen ya fadi, kuma kyaun sa ya lalace. Haka ma, mai arziki zai bushe yana cikin tsakiyar tafiyarsa.
12 Pomaikai wale ke kanaka, ke ku paa ia i ka hoowalewaleia mai; no ka mea, a pau kona hoaoia mai, e loaa auanei ia ia ka lei o ke ola i oleloia mai ai e ka Haku no ka poe e aloha aku ana ia ia.
Albarka ta tabbata ga mutum mai jurewa da gwaji. Domin in ya jure gwajin, zai sami rawanin rai, wanda aka yi alkawarin sa ga wadanda ke kaunar Allah.
13 A o ka mea i hoowalewaleia mai, mai olelo ae ia, ua hoowalewaleia mai au e ke Akua; no ka mea, aole i hoowalewaleia ke Akua e ka hewa, aole loa hoi oia i hoowalewale mai i kekahi.
Kada wani ya ce idan aka gwada shi, ''Wannan gwaji daga wurin Allah ne,'' domin ba a gwada Allah da mugunta, shi kan sa kuwa ba ya gwada kowa.
14 Aka, ua hoowalewaleia kela mea keia mea ma kona kuko iho no, i ke alakaiia'ku a puni ia.
Amma kowanne mutum yakan sami gwaji daga muguwar sha'awar sa, wadda take janye shi kuma ta rinjaye shi.
15 Aia hapai ke kuko, alaila, hanau mai ka hewa; a oo ka hewa, alaila, hoopukaia mai ka make.
Bayan da muguwar sha'awar ta dauki ciki, sai ta haifi zunubi. Kuma bayan da zunubi ya yi girma, yakan haifi mutuwa.
16 Mai kuhihewa, e o'u poe hoahanau aloha:
Kada fa ku yaudaru, 'yan'uwana kaunatattu.
17 O na haawina maikai a pau a me na makana hemolele a pau, noluna mai ia i iho mai ai no ka Makua mai o ka malamalama, aole ona ano hou, aole loa ia e luli iki.
Kowace kyakkyawar baiwa, da kowace cikakkiyar baiwa daga sama take. Ta sauko ne daga wurin Uban haskoki. Wanda babu sauyawa ko wata alamar sakewa kamar yadda inuwa ke yi.
18 No kona makemake iho i hoohanau mai ai oia ia kakou ma ka olelo oiaio, i lilo ae kakou i mau hua mua o ka poe ana i hana'i.
Allah ya zabi ya haife mu ta wurin maganar gaskiya, domin mu zama kamar nunar fari na dukan halittar sa.
19 No ia mea, e o'u poe hoahanau aloha, e hiki wawe oukou ma ka lohe, e akahele hoi ma ka olelo ana aku, a e hoolohi hoi ma ka inaina aku:
Kun san wannan, 'yan'uwana kaunatattu: bari kowanne mutum ya yi hanzarin kasa kunne, da jinkirin yin magana, da kuma jinkirin yin fushi.
20 No ka mea, o ka inaina o ke kanaka, aole ia e hana ana i ka pono o ke Akua.
Domin fushin mutum ba ya aikata adalcin Allah.
21 No ia mea la, e pale aku oukou i ka haumia a pau, a me ka hu wale ana o ka ino, a e apo mai oukou me ke akahai i ka olelo i pakuiia, oia ka mea e hiki ai ke hoola i ko oukou poe uhane.
Saboda haka, sai ku yar da kowanne irin aikin kazanta da yalwar mugunta. A cikin tawali'u ku karbi dassashiyar maganar, wadda ke iya ceton rayukan ku.
22 E lilo hoi oukou i poe malama i ka olelo, aole i poe lohe wale no, e hoopunipuni ana ia oukou iho:
Ku zama masu aikata maganar, kada ku zama masu jin ta kawai, kuna yaudarar kanku.
23 No ka mea, ina i lohe wale kekahi i ka olelo, aole oia i malama aku, ua like no ia me ke kanaka e nana ana i kona helehelena iho ma ke aniani;
Domin duk wanda ya ke mai jin maganar ne kawai, ba mai aikatawa ba, kamar mutum yake mai duba fuskarsa a madubi.
24 Nana no oia ia ia iho, a i ka hoi ana'ku, poina koke iho no ia i kona ano iho.
Yakan dubi kansa sai ya tafi, nan da nan kuwa sai ya manta da kamannin sa.
25 O ka mea e nana ae i ke kanawai hemolele o ke ola, a e ku paa malaila, aole e hoopoina wale i kana mea i lohe ai, aka, ua malama no ia i ka oihana; oia ka mea e pomaikai aua i kana hana ana.
Amma duk mai duba shari'ar da bin ka'idar nan ta 'yanci, ya kuma nace biyayya da ita, ba zai zama kamar wanda zai ji ya manta ba, wannan mutum zai zama da albarka a cikin abin da yake yi.
26 Ina i manaoia kekahi he haipule ia, aole hoi oia e kaulawaha i kona alelo, aka, e hoopunipuni i kona naau iho, ua lapuwale kona haipule ana.
Idan wani yana zaton shi mai addini ne, amma bai kame bakinsa ba, yana yaudarar zuciyarsa ne, addinin mutumin nan na banza ne.
27 O ka haipule io a me ka haumia ole imua i ke alo o ke Akua o ka Makua, eia no ia; e ike i ka poe makua ole, a me ka poe wahinekanemake i ko lakou wa e pihkia ai, a e malama hoi ia ia iho i haumia ole ia i ko ke ao nei.
Addini sahihi kuma marar aibi a gaban Allahnmu da Ubanmu, shine a kula da gwauraye da marayu a cikin kuntatar su, kuma mutum ya kebe kansa ya zama marar aibi daga duniya.

< Iakobo 1 >