< Markus 16 >
1 Bayan ranar assabaci, Maryamu Magadaliya da Maryamu uwar Yakubu da Salomi, suka sayo man shafawa mai kamshi domin shafe jikin Yesu saboda jana'iza.
Now when the Sabbath was past, Mary Magdalene, Mary the mother of James, and Salome bought spices, in order to go and anoint Jesus.
2 Da safiyar ranar farko ta mako sai suka tafi kabarin a dai dai fitowar rana.
Very early on the first day of the week, they came to the tomb when the sun had risen.
3 Suna magana a tsakaninsu suna cewa, wanene zai gangarar da dutsen da aka rufe bakin kabarin da shi?”
And they were saying among themselves, “Who will roll away the stone from the door of the tomb for us?”
4 Da suka daga ido, sai suka ga an riga an gangarar da dutsen, domin yana da girma.
(because it was very large), but when they looked up, they saw that the stone had been rolled away!
5 Da suka shiga cikin kabarin sai ga wani saurayi saye da farar tufa, yana zaune a hannun dama, suna mamaki.
Upon entering the tomb they saw a young man dressed in a white robe sitting on the right side, and they were alarmed.
6 Sai ya ce masu, “Kada ku ji tsoro. Kuna neman Yesu banazare, wanda aka giciye. Ya tashi! Baya nan. Ku duba wurin da aka kwantar dashi.
But he said to them: “Don't be alarmed. You are looking for Jesus the Natsarene, who was crucified. He has risen! He isn't here! See, the place where they laid Him.
7 Sai ku je, ku gaya wa almajiransa da Bitrus cewa ya rigaya ya yi gabanku zuwa Galili. A can zaku ganshi, kamar yadda ya fada maku.”
But go, tell His disciples, also Peter: ‘He is going before you into Galilee; there you will see Him, as He said to you.’”
8 Suka fita daga cikin kabarin da gudu suna rawar jiki da mamaki, ba su cewa kowa komai ba domin suna jin tsoro.
Trembling and bewildered they went out and fled from the tomb; and they said nothing to anyone, because they were afraid.
9 (note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Da safiyar ranar farko ta mako ya fara bayyana kansa ga Maryamu Magadaliya wadda ya kori aljannu guda bakwai daga cikinta.
(note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Having risen early on the first day of the week, Jesus appeared first to Mary Magdalene, out of whom He had cast seven demons.
10 Sai ta tafi ta shaida wadanda suke tare da shi suke makoki da kuka.
She went and reported to those who had been with Him, as they were mourning and weeping.
11 Sai suka ji cewa ya tashi kuma ta ganshi, amma basu gaskata ba.
When they heard that He was alive and had been seen by her, they did not believe.
12 Bayan wadannan al'amura ya bayana kansa ta wata siffa ga mutum biyu sa'ilin da suke tafiya akan hanya.
After these things He appeared in a different form to two of them as they were walking, going into the country.
13 Sai suka tafi suka gaya wa sauran almajiransa, duk da haka basu gaskata ba.
So they returned and reported to the rest; neither did they believe them.
14 Bayan wani lokaci, Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa su goma sha daya, ya tsauta masu saboda rashin gaskatawa da taurin zuciya, bayansun ji daga wadanda suka ganshi bayan ya tashi daga matattu.
Later He appeared to the eleven as they were reclining at the table; and He rebuked their unbelief and hardness of heart, because they did not believe those who had seen Him after He had risen.
15 Sai ya umarcesu cewa “Ku tafi cikin duniya ku yi bishara ga dukan halitta.
Then He said to them: “Go to the whole world and proclaim the Gospel to all creation.
16 Wanda ya ba da gaskiya aka kuma yi masa baftisma, zaya sami ceto, wanda baya bada gaskiya ba za ya hallaka.
He who believes and is baptized will be saved; but he who does not believe will be condemned.
17 Wadannan alamu za su kasance da wadanda suka gaskata; a cikin sunana, za su fidda aljannu, za su yi magana da sabbin harsuna.
And these signs will accompany those who believe: in my name they will cast out demons; they will speak with new languages;
18 Za su dauki macizai da hannayesu, idan sun sha guba ba ta cutar dasu ba, za su dibiya hannayensu ga marasa lafiya, za su sami warkaswa.”
they will remove ‘snakes’; and if they drink anything deadly, it will not hurt them at all; they will lay hands on sick people, and they will get well.”
19 Bayan Ubangiji ya gama magana da su, sai aka dauke shi zuwa sama in da zai zauna a hannun dama na Allah.
So then, after the Lord had spoken to them, He was received up into heaven and sat down at God's right.
20 Almajiransa kuma suka tafi ko'ina suna sheilar bishara. Ubangiji kuma yayi aiki tare da su, yana tabbatar da kalma ta wurin ayukan al'ajiba tare da su.
And they went out and preached everywhere, the Lord working with them and confirming the message by the accompanying signs. Amen.