< Markus 15 >
1 Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus.
As soon as it was early morning, having already formed a plan, the chief priests with the elders and scribes, indeed the whole council, bound Jesus, led Him away and handed Him over to Pilate.
2 Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce “haka ka ce”
Pilate asked Him, “Are you the king of the Jews?” So in answer He said to him, “You stated a fact!”
3 Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.
But the chief priests kept accusing Him of many things.
4 Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka.
So Pilate asked Him again, saying: “Are you not going to answer? See how many things they are testifying against you!”
5 Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.
But Jesus still gave no answer, so that Pilate marveled.
6 A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka,
Now at the feast he would release to them one prisoner, whomever they would request.
7 A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas.
Well there was one called Barabbas, who had been bound with his fellow insurrectionists, who in the insurrection had committed murder.
8 Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.
Then the crowd began to call out and request that he do just as he always did for them.
9 Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?
So Pilate answered them, saying, “Do you want me to release to you the king of the Jews?”
10 Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa,
(He knew that the chief priests had handed Him over because of envy.)
11 Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.
But the chief priests stirred up the crowd, so that he should release Barabbas to them instead.
12 Bilatus ya sake yi masu tambaya “Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?”
Pilate answered and said to them again, “What then do you want me to do to him you call ‘king of the Jews’?”
13 sai suka amsa da kuwwa” a “giciye shi!”
Again they shouted, “Crucify him!”
14 Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, “a giciye shi.”
But Pilate said to them, “But what evil did he do?” They just yelled all the louder, “Crucify him!”
15 Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.
So Pilate, wanting to gratify the crowd, released Barabbas to them, and Jesus, after a flogging, he handed over to be crucified.
16 Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja,
Then the soldiers led Him away into the courtyard (that is, the Praetorium) and assembled the whole garrison.
17 Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya,
They clothed Him with purple, plaited a crown of thorns and put it on Him,
18 Suna masa kirari na ba'a suna cewa, “A gaida sarkin Yahudawa!”
and began to ‘acclaim’ Him by saying, “Hail, King of the Jews!”
19 Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a.
They kept hitting Him on the head with a rod and spitting on Him, and kneeling down they would ‘worship’ Him.
20 Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi.
When they had ridiculed Him, they took the purple off Him and put His own clothes on Him. Then they led Him out to crucify Him.
21 Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.
A certain passer-by, Simon a Cyrenian (the father of Alexander and Rufus), coming in from the countryside, was compelled to carry His cross.
22 Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai)
They brought Him to a place Golgotha, which is translated, ‘Place of a Skull’.
23 Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha.
They offered Him wine mixed with myrrh to drink, but He did not take it.
24 Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.
After crucifying Him, they divided His clothes by casting lots for them, to see who would take what.
25 A sa'a ta uku aka giciye shi.
It was the third hour when they crucified Him.
26 Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa “Ga Sarkin Yahudawa”
The statement of His ‘crime’ that had been written was: THE KING OF THE JEWS.
27 Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu.
With Him they also crucified two bandits, one on His right and one on His left.
28 Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.
So the Scripture was fulfilled which says, “And He was numbered with transgressors.”
29 suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, “Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku,
Those who passed by kept ridiculing Him, wagging their heads and saying, “Hey! You who can destroy the temple and build it in three days,
30 ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!”
save yourself and come down from the cross!”
31 Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa “Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba”
Similarly, the chief priests, with the scribes, kept mocking among themselves saying: “He saved others; he can't save himself!
32 Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.
Let the Christ, the king of Israel, descend now from the cross, that we may see and believe him.” Those who were crucified with Him insulted Him as well.
33 sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina,
Now when the sixth hour had come [noon], darkness came over the whole land until the ninth hour.
34 A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?” Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?”
At the ninth hour Jesus called out strongly, saying, “Eloi, Eloi, lima sabachthani?” which is translated, “O God, my God, why have You forsaken me?”
35 Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, “Duba, yana kiran Iliya.”
When some of the bystanders heard it they said, “Listen, he's calling Elijah.”
36 Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi.
Then someone ran, filled a sponge with wine vinegar, put it on a reed and started offering it to Him to drink, saying, “You let him be! ‘Let's see if Elijah is coming to take him down’!”
37 Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu.
Then Jesus gave a loud shout and breathed out His spirit;
38 Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.
and the veil of the temple was torn in two from top to bottom.
39 Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce “hakika, wannan mutum Dan Allah ne.”
Well when the centurion, who was standing opposite Him, saw that He breathed out His spirit after giving such a loud shout, he said, “This man really was God's Son!”
40 Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.
There were also women looking on from a distance, among whom were Mary Magdalene, Mary the mother of James the Less and of Joses, and Salome
41 Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.
—they used to follow Him and minister to Him when He was in Galilee—and many other women who had come up with Him to Jerusalem.
42 Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce.
Now when evening had come, because it was Preparation Day (that is, the day before the Sabbath),
43 Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu.
Joseph of Arimathea, a prominent council member who also himself was waiting for the Kingdom of God, came and boldly went in to Pilate and asked for the body of Jesus.
44 Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.
Well Pilate was surprised that He was already dead; and summoning the centurion he asked him when He had died.
45 Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu.
Upon the centurion's confirmation he granted the body to Joseph.
46 Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi.
Having bought linen, he took Him down, wrapped Him in the linen and laid Him in a tomb that had been cut out of rock; then he rolled a stone against the door of the tomb.
47 Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.
Mary Magdalene and Mary the mother of Joses observed where He was placed.