< Luka 24 >
1 Da sassafe a ranar farko ta mako, suka zo kabarin, suka kawo kayan kamshi wadda suka shirya.
Very early on the first day of the week, they came to the tomb, bringing the spices which they had prepared.
2 Sai suka samu dutsen a mirgine shi daga kabarin.
They found the stone rolled away from the tomb.
3 Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji Yesu ba.
They entered in, but did not find the body of the Lord Jesus.
4 Ya faru kuwa, yayin da suke a rikice game da wannan, ba zato, mutane guda biyu suka tsaya a gabansu da tufafi masu walkiya.
It happened that, while they were confused about this, suddenly, two men stood by them in bright shining robes.
5 Sa'adda matan suka sunkuyar da kansu kasa domin tsoro, suka ce wa matan, “Don me kuke neman mai rai ciki matattatu?
As the women were filled with fear and bowed down their faces to the earth, they said to the women, “Why do you seek the living among the dead?
6 Baya nan, amma ya tashi! Ku tuna fa yadda ya yi maku magana tun sa'adda ya ke Galili,
He is not here, but has been raised! Remember how he spoke to you when he was still in Galilee,
7 cewa za a ba da Dan Mutum ga mutane masu zunubi su kuma giciye shi, a rana ta uku, zai tashi kuma”
saying that the Son of Man must be delivered up into the hands of sinful men and be crucified, and on the third day rise again.”
8 Sai matan suka tuna da kalmominsa,
The women remembered his words,
9 suka koma daga kabarin sai suka gaya wa sha dayan wadannan abubuwan da dukan sauran.
and returned from the tomb, and told all these things to the eleven and all the rest.
10 Su Maryamu Magadaliya, Yuwana, Maryamu uwar Yakubu, da sauran matan da ke tare da su suka ba manzanni rohoton wadannan abubuwan.
Now Mary Magdalene, Joanna, Mary the mother of James, and the other women with them reported these things to the apostles.
11 Amma manzannin suka dauki maganar kamar ba ta da amfani, kuma ba su bada gaskiya ga matan ba.
But this message seemed like idle talk to the apostles, and they did not believe the women.
12 Duk da haka Bitrus ya tashi, sai ya gudu zuwa kabarin, ya sunkuya yana kallon ciki, sai ya gan likaftani linin kadai. Sa'annan Bitrus ya tafi gidansa, yana ta mamakin abinda ya faru.
Yet Peter rose up and ran to the tomb, and stooping and looking in, he saw the linen cloths by themselves. Peter then departed to his home, wondering what had happened.
13 A ranan nan, sai ga biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani kauye suna Imawus, wanda nisansa kimanin mil ne daga Urushalima.
Behold, two of them were going that very day to a village named Emmaus, which was sixty stadia from Jerusalem.
14 Suna tattaunawa da junansu game da dukan abubuwan da suka faru.
They discussed with each other about all the things that had happened.
15 Sai ya zama da cewa, sa'adda su ke tattaunawa tare da tambayoyi, sai Yesu da kansa ya matsa kusa yana tafiya tare da su.
It happened that, while they discussed and questioned together, Jesus himself approached and went with them.
16 Amma idanunsu basu iya ganewa da shi ba.
But their eyes were prevented from recognizing him.
17 Yesu ya ce masu, “Menene ku ke magana akai sa'adda ku ke tafiya?” Suka tsaya a wurin suna bakin ciki.
Jesus said to them, “What are the two of you talking about as you walk?” They stood there looking sad.
18 Daya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa, “Kai ne kadai mutumin da ke Urushalima wanda bai san abubuwan da suka faru a can a wannan kwanakin ba?”
One of them, named Cleopas, answered him, “Are you the only person in Jerusalem who does not know the things which have happened there these days?”
19 Yesu ya ce masu, “Wadanne abubuwa?” Suka amsa masa, “Abubuwa game da Yesu ba Nazarat, wanda ya ke annabi ne, mai manyan ayuka da kalmomi daga Allah da kuma mutane.
Jesus said to them, “What things?” They answered him, “The things concerning Jesus the Nazarene, who was a prophet, mighty in deed and word before God and all the people,
20 Da yadda manyan firistoci da masu mulkinmu suka bada shi domin a hukunta shi ga mutuwa a kuma giciye shi.
and how the chief priests and our rulers delivered him up to be condemned to death and crucified him.
21 Amma mun yi begen cewa shine wanda za ya yantar da Isra'ila. I, bayan wannan kuma, yanzu kwana uku kenan tunda wadannan abubuwan suka faru.
But we had confidence that he was the one who was going to redeem Israel. Yes, and what is more, it is now the third day since all these things happened.
22 Amma har'ila yau, wadansu mata da ke tare da mu sun yi mana abin al'ajabi, da suka kasance a kabarin tunda sassafe.
But also, some women of our company amazed us, having been at the tomb early in the morning.
23 Sa'adda ba su sami jikinsa ba, suka zo, da cewa su ma sun ga wahayin mala'iku wadanda suka ce masu ya na da rai.
When they did not find his body, they came, saying that they had also seen a vision of angels who said that he was alive.
24 Wasu maza wadanda ke tare da mu suka tafi kabarin, suka tarar da shi kamar yadda matan suka fada. Amma ba su ganshi ba.”
Some men who were with us went to the tomb, and found it just as the women had said. But they did not see him.”
25 Yesu ya ce masu, “Ku mutane masu wauta da marasa ba da gaskiya ga abin da annabawa suka fada!
Jesus said to them, “O foolish men and slow of heart to believe in all that the prophets have spoken!
26 Bai zama dole ne Almasihu ya sha wahalan wadannan abubuwan ba, ya kuma shiga cikin daukakarsa?”
Was it not necessary for the Christ to suffer these things, and to enter into his glory?”
27 Sa'annan da farko daga Musa da har zuwa dukan annabawa, Yesu ya fasara masu duka abubuwa da ke game da kansa a dukan littattafai.
Then beginning from Moses and through all the prophets, Jesus interpreted to them the things concerning himself in all the scriptures.
28 Da suka yi kusa da kauyen, inda suke tafiya, ko da yake Yesu ya yi kamar zai wuce su.
As they approached the village to which they were going, Jesus acted as though he were going further.
29 Amma suka tilasta shi, cewa, “Ka zauna da mu, gama yamma ta yi kusa rana kuma ta kusa karewa.” Sai Yesu ya tafi ya zauna da su.
But they compelled him, saying, “Stay with us, for it is toward evening and the day is almost over.” So Jesus went in to stay with them.
30 Ya faru cewa, sa'adda ya zauna tare da su domin ya ci abinci, sai ya dauki gurasan, ya albarkace shi, ya kakkarya, sai ya ba su.
It happened that, when he had sat down with them to eat, he took the bread, blessed it, and breaking it, he gave it to them.
31 Sa'annan idanunsu suka bude, da suka gane shi, sai ya bace daga garesu,
Then their eyes were opened, and they knew him, and he vanished out of their sight.
32 Suka ce wa junansu, ashe zuciyarmu ba ta yi kuna a cikinmu ba, sa'adda yake magana da mu a hanya, sa'adda ya bude mana littattafai?”
They said one to another, “Was not our heart burning within us, while he spoke to us on the way, while he opened to us the scriptures?”
33 Suka tashi a wancan sa'a, sai suka koma Urushalima. Suka sami sha dayan nan tare, da wadanda suke tare da su,
They rose up that very hour, and returned to Jerusalem. They found the eleven gathered together, and those who were with them,
34 cewa, “Lalle ne Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman.”
saying, “The Lord is risen indeed, and has appeared to Simon.”
35 Sai suka fadi abubuwan da suka faru a hanya, da yadda aka bayyana masu Yesu sa'adda ya kakkarya gurasa.
So they told the things that happened on the way, and how Jesus was shown to them in the breaking of the bread.
36 Sa'adda suke fadin wadannan abubuwan, sai Yesu ya tsaya a sakaninsu, sai ya ce masu, “Salama a gareku.”
As they spoke these things, Jesus himself stood in the midst of them, and said to them, “Peace be to you.”
37 Amma suka firgita suna cike da tsoro, suna tsammani sun ga fatalwa.
But they were terrified and filled with fear, and supposed that they saw a spirit.
38 Yesu ya ce masu, don me ku ke damuwa? Don me tambayoyi ke tasowa a zuciyarku?
Jesus said to them, “Why are you troubled? Why do questions arise in your heart?
39 Duba hannayena da kafafuna, cewa nine da kaina. Taba ni ku gani. Gama ruhu ba shi da jiki da kashi, kamar yadda ku ka ga nake da su.”
See my hands and my feet, that it is I myself. Touch me and see. For a spirit does not have flesh and bones, as you see me having.”
40 Bayan da ya fadi wannan, sai ya nuna masu hannayensa da kafafunsa.
When he had said this, he showed them his hands and his feet.
41 Sa'adda suke cike da farin ciki, da mamaki, Yesu ya ce masu, “Kuna da wani abinci?”
They still could not believe it because of joy, and they were amazed. Jesus said to them, “Do you have anything to eat?”
42 Sai suka bashi gasasshen kifi.
They gave him a piece of a broiled fish,
43 Yesu ya karba, ya ci a gabansu.
and he took it and ate it before them.
44 Sai ya ce masu, “Sa'adda nake tare da ku na gaya maku cewa duka abin da aka rubuta a cikin dokokin Musa da na annabawa da Zabura dole su cika.”
He said to them, “When I was with you, I told you that all that was written in the Law of Moses and the Prophets and the Psalms must be fulfilled.”
45 Sai ya bude hankalinsu, saboda su gane littattafai.
Then he opened their minds, that they might understand the scriptures.
46 Ya ce masu, “A rubuce yake, cewa Almasihu za ya sha wuya, zai tashi kuma daga matattu a rana ta uku.
He said to them, “Thus it is written, that the Christ should suffer, and rise again from the dead on the third day.
47 Ku yi wa'azin tuba da gafarar zunubai a cikin sunansa ga dukan al'ummai, ku fara daga Urushalima.
Repentance and forgiveness of sins should be preached in his name to all the nations, beginning from Jerusalem.
48 Ku shaidu ne ga wadannan abubuwan.
You are witnesses of these things.
49 Duba, ina aiko da alkawarin Ubana a kanku. Amma ku jira a birni, sai an suturta ku da iko daga sama.”
See, I am sending you what my Father promised. But remain in the city until you are clothed with power from on high.”
50 Sa'annan Yesu ya tafi tare da su har sai da suka kai kusa da Betanya. Sai ya daga hannunsa ya albarkace su.
Then Jesus led them out until they were near Bethany. He lifted up his hands and blessed them.
51 Ya zama sa'adda yake sa masu albarka, ya bar su sai aka dauke shi zuwa cikin sama.
It happened that, while he was blessing them, he left them and was carried up into heaven.
52 Sai suka yi masa sujada, suka komo Urushalima da murna mai yawa.
So they worshiped him, and returned to Jerusalem with great joy.
53 Kullayaumin suna cikin haikali, suna albarkatar Allah.
They were continually in the temple, blessing God.