< Markus 1 >
1 Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
This is the beginning of the gospel of Jesus Christ, the Son of God.
2 kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
As it is written in Isaiah the prophet, “Look, I am sending my messenger before your face, the one who will prepare your way.
3 Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
The voice of one calling out in the wilderness, 'Make ready the way of the Lord; make his paths straight.'”
4 Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
John came, baptizing in the wilderness and preaching a baptism of repentance for the forgiveness of sins.
5 Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
The whole country of Judea and all the people of Jerusalem went out to him. They were baptized by him in the Jordan River, confessing their sins.
6 Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
John was wearing a coat of camel's hair and a leather belt around his waist, and he was eating locusts and wild honey.
7 Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
He proclaimed, “One will come after me who is more powerful than I; the strap of his sandals I am not worthy to stoop down and untie.
8 Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
I baptized you with water, but he will baptize you with the Holy Spirit.”
9 Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
It happened in those days that Jesus came from Nazareth in Galilee, and he was baptized by John in the Jordan River.
10 Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
As Jesus came up out of the water, he saw the heavens split open and the Spirit coming down on him like a dove.
11 Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
A voice came out of the heavens, “You are my beloved Son. I am very pleased with you.”
12 Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
Then the Spirit compelled him to go out into the wilderness.
13 Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
He was in the wilderness forty days, being tempted by Satan. He was with the wild animals, and the angels served him.
14 Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
Now after John was arrested, Jesus came into Galilee proclaiming the gospel of God.
15 Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
He said, “The time is fulfilled, and the kingdom of God is near. Repent and believe in the gospel.”
16 Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
When he was walking beside the Sea of Galilee, he saw Simon and Andrew the brother of Simon casting a net in the sea, for they were fishermen.
17 Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
Jesus said to them, “Come, follow me, and I will make you fishers of men.”
18 Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
Then immediately they left the nets and followed him.
19 Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
As Jesus was walking on a little farther, he saw James son of Zebedee and John his brother; they were in the boat mending the nets.
20 Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
He called them and they left their father Zebedee in the boat with the hired servants, and they followed him.
21 Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
Then they came into Capernaum, and on the Sabbath, Jesus went into the synagogue and taught.
22 Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
They were astonished at his teaching, for he was teaching them as someone who has authority and not as the scribes.
23 A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
Just then a man in their synagogue who had an unclean spirit cried out,
24 Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
saying, “What do we have to do with you, Jesus of Nazareth? Have you come to destroy us? I know who you are. You are the Holy One of God!”
25 Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
Jesus rebuked the demon and said, “Be quiet and come out of him!”
26 Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
The unclean spirit threw him down and went out from him while crying out with a loud voice.
27 Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
All the people were amazed, so they asked each other, “What is this? A new teaching with authority? He even commands the unclean spirits and they obey him!”
28 Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
The news about him went out everywhere into the whole region of Galilee.
29 Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
After coming out of the synagogue, they came into the house of Simon and Andrew, along with James and John.
30 Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
Now Simon's mother-in-law was lying sick with a fever, and they told Jesus about her.
31 Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
So he came, took her by the hand, and raised her up; the fever left her, and she started serving them.
32 Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
That evening, after the sun had set, they brought to him all who were sick or possessed by demons.
33 Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
The whole city gathered together at the door.
34 ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
He healed many who were sick with various diseases and cast out many demons, but he did not allow the demons to speak because they knew him.
35 Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
He got up very early, while it was still dark; he left and went out into a solitary place and there he prayed.
36 Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
Simon and those who were with him searched for him.
37 Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
They found him and they said to him, “Everyone is looking for you.”
38 Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
He said, “Let us go elsewhere, out into the surrounding towns, so that I may preach there also. That is why I came out here.”
39 Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
He went throughout all of Galilee, preaching in their synagogues and casting out demons.
40 Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
A leper came to him. He was begging him; he knelt down and said to him, “If you are willing, you can make me clean.”
41 Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
Moved with compassion, Jesus reached out his hand and touched him, saying to him, “I am willing. Be clean.”
42 Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
Immediately the leprosy left him, and he was made clean.
43 Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
Jesus strictly warned him and sent him away.
44 Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
He said to him, “Be sure to say nothing to anyone, but go, show yourself to the priest, and offer for your cleansing what Moses commanded, as a testimony to them.”
45 Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.
But he went out and began to spread the news widely, so much that Jesus could no longer enter a town openly but he stayed out in remote places. Yet people were still coming to him from everywhere.