< Luka 16 >

1 Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya.
Yesu akabhajobhela bhanafunzi bha muene, “Pajhele ni munu mmonga tajiri ajhe ni meneja, na ataarifibhu jha kujha meneja ojho itapanya mali sya muene.
2 Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'
Hivyo tajiri akan'kuta, akan'jobhela, “kiki ekhe kya nikakip'eleka juu jha bhebhe? Bhosiajhi hesabu jha umeneja bhwa jhobhi, kwandabha wibhwesya lepi kuja meneja kabhele.'
3 Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko.
Meneja jhola akajobha mu muoyo bhwa muene, nikhetayi kiki, maana bwana ghwa nene akanibhosya mu kazi jhangu jha umeneja? nijhelepi ni nghofu sya kulema, ni kus'oka nibhona soni.
4 Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.
Nimanyili lyaibeta kubhomba ili panibeta kubhosibhwa mu mbombo jhangu jha uwakili bhanu bhanikaribisiajhi mu nyumba sya bhene
5 Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?'
Hivyo wakili akabhakuta bhadeni bhwa bwana ghwa muene kwa khila mmonga akan'jobhela ghwa kuanza, 'ghwidaibhwa kiasi gani ni bwana bhangu?'
6 Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.'
Akajobha fipemu mia moja fya mafuta akan'jobhela 'tolayi hati jha jhobhi tamayi manyata yandikayi hamsini.'
7 Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'
Kisha akan'jobhela jhongi ni bhebhe widaibhwa kiasi gani?' akajobha 'fipemu mia moja fya sembe ghwa ngano.' Akan'jobhela 'letayi hati jha bhebhe jhandikayi themanini.'
8 Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. (aiōn g165)
bwana jhola akan'sifu meneja dhalimu kwa vile kyaabhombili kwa wereu. Kwa kujha bhanu bha ulimwengu obho bherevu bhingi na bhishughulika kwa ujanja ni bhanu bha lubhafu lwa bhene kuliko kya bhajhele bhana bha nuru. (aiōn g165)
9 Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama. (aiōnios g166)
Nani nikabhajobhela mwikibhekayi marafiki kwa mali gha udhalimu ili pajhibeta kukosekana bhabhakaribisiajhi mu makao gha milele. (aiōnios g166)
10 Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu.
Jhaajhe mwaminifu kwa e'le lidebe nesu ijha mwaminifu mu libhaha kabhele. na jhaajhe dhalimu kwa ele lidebe ijha dhahalimu kwa lijhele libhaha kabhele.
11 Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya?
Kama muenga mwajhelepi mwebhaaminifu mu mali gha udhalimu niani jha ibeta kubhaamini mu mali gha bhukweli?
12 Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?
Na kama mwajhelepi bhaaminifu katika mali gha munu jhongi niani ibeta kubhaamini kwa gha muenga?
13 Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba.”
Ajhelepi mtumishi jha ibhwesya kutumikila mabwana bhabhele, kwandabha ibeta kun'dadila mmonga ni kun'gana jhongi, ama ibeta kushikamana ni ojho nikumdharau ojho. Mwibhwesya lepi kun'tumikila K'yara ni mali.”
14 Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a.
Basi Mafarisayo, bhabhasiganili hela bhaghap'eliki agha ghoha na bhan'dhihakili.
15 Sai ya ce masu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.
Na akabhajobhela, “Muenga ndo mwamikidayi haki mbele jha bhanadamu, lakini Mungu ajhimanyili mioyo ghya muenga. Kwa kujha lyalitukuiki kwa mwanadamu lijha chukizo kwa K'yara.
16 Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta.
Sheria ni manabii fyajhele mpaka Yohana bho ahidili. Kuh'omela bhwakati obhu, habari jhinofu jha ufalme bhwa K'yara bhwitangesibhwa ni kila munu ijaribu kwijhingisya kwa nghofu.
17 Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.
Lakini rahisi kwa mbingu ni nchi fibhokayi kuliko hata herufi jhimonga jha sheria kukosekana.
18 Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.
Kila jhaakandeka nd'ala munu ni kun'gega n'dala jhongi idhinilepi, ni muene jhaakan'gega jha alekibhu ni n'gosi munu izinilepi.
19 Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana.
Pajhele ni munu mmonga tajiri jhaafwalili nghobho sya rangi sya zambarau ni kitani kinofu na akajha furahila kila ligono utajiri bhwa muene mbaha.
20 Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne,
Ni maskini mmonga lihina lya muene Lazaro abhekibhu pageti lya muene, na ajhe ni filonda.
21 Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.
Ni muene akajha inoghela kushibishwa kwa makombo ghaghabinili kuh'oma pameza pa jhola tajiri hata mabwa ghakahida kun'yabha filonda fya muene.
22 Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi,
Ikajha maskini jhola afwili na atolibhu ni malaika mpaka pakifua kya Ibrahimu. Tajiri jhola ni muene afwili na asyelibhu.
23 yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa. (Hadēs g86)
Ni khola kuzimu paajhele mu malombosi akaghajhinula mihu gha muene akambona Ibrahimu kwa patali ni Lazaro pakifua kya muene. (Hadēs g86)
24 Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'
Akalela akajobha, 'Dadi Ibrahimu, unihurumilayi un'tumayi Lazaro ajhinayi ncha jha kikonji kya muene mumasi, auburudisiajhi lumilu lwa nene; kwandabha nitesibhwa mu muoto obho.
25 Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba.
Lakini Ibrahimu akajobha, 'Mwanabhangu khombokayi katika maisha gha jhobhi ghwa ejhapokili mambo gha jhobhi manofu ni Lazaro mebhu akabhili manofu lepi. Ila henu ajhe apa ifarijibhwa ni bhebhe wilamasibhwa.
26 Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'
Ni zaidi jha aghu libhekibhu lilende libhaha na litali kati jha tete, ili bhala bhabhilonda kubhoka khoni kulota kwa jhomu bhasibhwesi wala bhanu bha muenga bhasilobhoki kuhida khoni.'
27 Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina -
Tajiri jhola akajobha, 'Nikus'oka Dadi Ibrahimu, kwamba undaghisiajhi kunyumba kwa dadijhangu
28 domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'
kwakujha nijhe nibhalongo bhangu bhahanu ili abhaonyanyi, kwa hofu kujha na bhene kabhele bhibeta kuhida mahali pa mal'ombosi.
29 Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.'
Lakini Ibrahimu akajobha, 'Bhajheni Musa ni manabii. Bhalekayi bhabhapelekesiajhi bhene.
30 Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.'
Tajiri jhola akajobha, 'lepi, Dadi Ibrahimu, lakini kama abhalotili munu jha ih'omela kwa bhafu bhibeta kutubu.'
31 Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'”
Lakini Ibrahimu akabhajobhela, 'bhakabelayi lubhap'eleka Musa ni manabii bhibeta lepi kushawishibhwa hata munu akafufukayi kwa bhafu.

< Luka 16 >