< Yohanna 4 >

1 Da Yesu ya sani cewa Farisawa sun ji cewa yana samun almajirai yana kuma yi masu baftisma fiye da Yahaya
Le Seigneur, ayant donc appris que les pharisiens avaient entendu dire qu'il faisait et baptisait plus de disciples que Jean
2 (ko da shike ba Yesu da kansa ke yin baftismar ba, amma almajiransa ne),
(Toutefois ce n'était pas Jésus lui-même qui baptisait, mais c'étaient ses disciples),
3 ya bar Yahudiya ya koma Galili.
Il quitta la Judée, et s'en retourna en Galilée.
4 Amma ya zamar masa dole ya ratsa ta Samariya.
Or, il fallait qu'il passât par la Samarie.
5 Ya zo wani birnin Samariya, mai suna Sika, kusa da filin da Yakubu ya ba dansa Yusufu.
Il arriva donc à une ville de Samarie, nommée Sichar, près de la terre que Jacob avait donnée à Joseph son fils.
6 Rijiyar Yakubu na wurin. Da Yesu ya gaji da tafiyarsa sai ya zauna gefen rijiyar. Kusan karfe goma sha biyu na rana ne.
Là était la fontaine de Jacob. Jésus donc, fatigué du chemin, s'assit sur la fontaine; c'était environ la sixième heure.
7 Wata mace, Ba-Samariya ta zo domin ta dibi ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha.”
Une femme samaritaine étant venue pour puiser de l'eau, Jésus lui dit: Donne-moi à boire.
8 Gama almajiransa sun tafi cikin gari don sayen abinci.
Car ses disciples étaient allés à la ville pour acheter des vivres.
9 Sai ba-Samariyar tace masa, “Yaya kai da kake Bayahude kake tambaya ta ruwan sha, ni da nike 'yar Samariya?” Domin Yahudawa ba su harka da Samariyawa.
La femme samaritaine lui répondit: Comment, toi qui es Juif, me demandes-tu à boire, à moi qui suis une femme samaritaine? (Car les Juifs n'ont point de communication avec les Samaritains. )
10 Sai Yesu ya amsa yace mata, “In da kin san kyautar Allah, da shi wanda yake ce da ke, 'Ba ni ruwan sha,' da kin roke shi, sai kuma ya ba ki ruwan rai.”
Jésus répondit et lui dit: Si tu connaissais le don de Dieu, et qui est celui qui te dit: Donne-moi à boire, tu lui demanderais toi-même, et il te donnerait de l'eau vive.
11 Matar tace masa, “Mallam, ga shi ba ka da guga, kuma rijiyar tana da zurfi. Ina za ka samu ruwan rai?
La femme lui dit: Seigneur, tu n'as rien pour puiser, et le puits est profond; d'où aurais-tu donc cette eau vive?
12 Ai ba ka fi Ubanmu Yakubu ba, ko ka fi shi, shi wanda ya ba mu rijiyar, shi kansa kuma ya sha daga cikin ta, haka kuma 'ya'yansa da shanunsa?”
Es-tu plus grand que Jacob notre père, qui nous a donné ce puits, et qui en a bu lui-même, ainsi que ses fils et ses troupeaux?
13 Yesu ya amsa yace mata, “duk wanda ya sha daga wannan ruwan zai sake jin kishi,
Jésus lui répondit: Quiconque boit de cette eau aura encore soif;
14 amma duk wanda ya sha daga ruwa da zan ba shi ba zai sake jin kishi ba. Maimakon haka, ruwan da zan bashi zai zama mabulbular ruwa a cikinsa wanda ke bulbula zuwa rai madawwami.” (aiōn g165, aiōnios g166)
Mais celui qui boira de l'eau que je lui donnerai, n'aura plus jamais soif, mais l'eau que je lui donnerai deviendra en lui une source d'eau qui jaillira pour la vie éternelle. (aiōn g165, aiōnios g166)
15 Matar tace masa, “Mallam, ka ba ni wannan ruwa yadda ba zan kara jin kishi ba ba kuma sai na zo nan don in dibi ruwa ba.”
La femme lui dit: Seigneur, donne-moi de cette eau, afin que je n'aie plus soif, et que je ne vienne plus puiser ici.
16 Yesu ya ce mata, “Je, ki kira maigidanki ku zo nan tare.”
Jésus lui dit: Va, appelle ton mari et viens ici.
17 Matar ta amsa tace masa, “Ba ni da miji.” Yesu yace, “Kin fadi daidai da kika ce, 'ba ni da miji,'
La femme répondit: Je n'ai point de mari. Jésus lui dit: Tu as fort bien dit: Je n'ai point de mari;
18 domin kin auri mazaje har biyar, kuma wanda kike da shi yanzu ba mijin ki bane. Abinda kika fada gaskiya ne.”
Car tu as eu cinq maris; et celui que tu as maintenant n'est pas ton mari; tu as dit vrai en cela.
19 Matar tace masa, “Mallam, Na ga kai annabi ne.
La femme lui dit: Seigneur, je vois que tu es un prophète.
20 Ubaninmu sun yi sujada a wannan dutse, amma kun ce Urushalima ce wurin da ya kamata mutane su yi sujada.”
Nos pères ont adoré sur cette montagne, et vous, vous dites que le lieu où il faut adorer est à Jérusalem.
21 Yesu ya ce mata, “Mace, ki gaskata ni, cewa lokaci na zuwa wanda ba za ku yi wa Uban sujada ba ko akan wannan dutse ko a Urushalima.
Jésus lui dit: Femme, crois-moi; le temps vient que vous n'adorerez plus le Père ni sur cette montagne, ni à Jérusalem.
22 Ku kuna bauta wa abinda ba ku sani ba. Mu muna bauta wa abinda muka sani, gama ceto daga Yahudawa yake.
Vous adorez ce que vous ne connaissez pas; pour nous, nous adorons ce que nous connaissons; car le salut vient des Juifs.
23 Sai dai, sa'a tana zuwa, har ma ta yi, wadda masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a cikin ruhu da gaskiya, domin irin wadannan ne Uban ke nema su zama masu yi masa sujada.
Mais l'heure vient, et elle est déjà venue, que les vrais adorateurs adoreront le Père en esprit et en vérité, car le Père demande de tels adorateurs.
24 Allah Ruhu ne, kuma mutanen da ke yi masa sujada, dole su yi sujada cikin ruhu da gaskiya.”
Dieu est esprit, et il faut que ceux qui l'adorent, l'adorent en esprit et en vérité.
25 Matar ta ce masa, “Na san Almasihu na zuwa (wanda ake kira Kristi). Sa'adda ya zo, zai bayyana mana kowane abu.
Cette femme lui répondit: Je sais que le Messie, celui qu'on appelle Christ, doit venir; quand il sera venu, il nous annoncera toutes choses.
26 Yesu ya ce mata, “Ni ne shi, wanda ke yi maki magana.”
Jésus lui dit: Je le suis, moi qui te parle.
27 A daidai wannan lokaci, almajiransa suka dawo. Suna ta mamakin dalilin da yasa yake magana da mace, amma babu wanda yace, “Me kake so?” Ko kuma, “Don me ka ke magana da ita?”
Sur cela ses disciples arrivèrent, et ils furent surpris de ce qu'il parlait avec une femme; néanmoins aucun ne lui dit: Que demandes-tu? ou, Pourquoi parles-tu avec elle?
28 Sai matar ta bar tulunta, ta koma cikin gari, tace wa mutanen,
Alors la femme laissa sa cruche, et s'en alla à la ville, et dit aux gens:
29 “Ku zo ku ga wani mutum wanda ya gaya mani duk wani abu da na taba yi. Wannan dai ba Almasihun bane, ko kuwa?”
Venez voir un homme qui m'a dit tout ce que j'ai fait; ne serait-ce point le Christ?
30 Suka bar garin suka zo wurinsa.
Ils sortirent donc de la ville, et vinrent vers lui.
31 A wannan lokacin, almajiransa suna rokansa, cewa, “Mallam, ka ci.”
Cependant, ses disciples le priant, lui disaient: Maître, mange.
32 Amma ya ce masu, “ina da abinci da ba ku san komai akai ba.”
Mais il leur dit: J'ai à manger une nourriture que vous ne connaissez pas.
33 Sai almajiran suka ce da junansu, “Babu wanda ya kawo masa wani abu ya ci, ko akwai ne?”
Les disciples se disaient donc l'un à l'autre: Quelqu'un lui aurait-il apporté à manger?
34 Yesu ya ce masu, “Abincina shine in yi nufin wanda ya aiko ni, in kuma cika aikinsa.
Jésus leur dit: Ma nourriture est de faire la volonté de celui qui m'a envoyé, et d'accomplir son ouvre.
35 Ba ku kan ce, 'akwai wata hudu tukuna kafin girbi ya zo ba?' Ina gaya maku, daga idanunku ku ga gonakin, sun rigaya sun isa girbi.
Ne dites-vous pas qu'il y a encore quatre mois jusqu'à la moisson? Voici, je vous le dis: Levez vos yeux, et regardez les campagnes qui blanchissent déjà pour la moisson.
36 Shi wanda ke girbi yakan karbi sakamako ya kuma tattara amfanin gona zuwa rai na har abada, ta haka shi mai shuka da shi mai girbi za su yi farinciki tare. (aiōnios g166)
Celui qui moissonne reçoit un salaire et recueille du fruit pour la vie éternelle, afin que celui qui sème se réjouisse aussi avec celui qui moissonne. (aiōnios g166)
37 Gama cikin wannan maganar take, 'Wani na shuka, wani kuma na girbi.'
Car en ceci, cette parole est vraie: Autre est le semeur, et autre le moissonneur.
38 Na aike ku ku yi girbin abinda ba ku yi aiki a kai ba. Wandansu sun yi aiki, ku kuma kun shiga cikin wahalarsu.
Je vous ai envoyés moissonner où vous n'avez pas travaillé; d'autres ont travaillé, et vous êtes entrés dans leur travail.
39 Yawancin Samariyawan da ke wannan birni suka gaskata da shi sabili da labarin matar data bada shaida, “Ya gaya mani duk abinda na taba yi.”
Or, plusieurs Samaritains de cette ville-là crurent en lui, à cause de la parole de la femme qui avait rendu ce témoignage: Il m'a dit tout ce que j'ai fait.
40 To sa'adda Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roke shi ya zauna tare da su, ya kuwa zauna wurin kwana biyu.
Les Samaritains étant donc venus vers lui, le prièrent de demeurer chez eux; et il y demeura deux jours.
41 Wasu da dama kuma suka gaskata domin maganarsa.
Et un plus grand nombre crurent à cause de sa prédication.
42 Suka cewa matar, “Mun bada gaskiya, ba saboda maganar ki kadai ba, amma mu kanmu munji, yanzu kuma mun sani cewa wannan lallai shine mai ceton duniya.”
Et ils disaient à la femme: Ce n'est plus à cause de ton récit, que nous croyons; car nous avons entendu nous-mêmes, et nous savons que celui-ci est véritablement le Sauveur du monde, le Christ.
43 Bayan wadannan kwana biyu, ya bar wurin zuwa Galili.
Deux jours après, il partit de là, et s'en alla en Galilée,
44 Domin Yesu da kansa yace, ba a girmama annabi a kasarsa.
Car Jésus lui-même avait déclaré qu'un prophète n'est point honoré dans son pays.
45 Da ya zo Galili, Galiliyawan suka marabce shi. Sun ga dukan abubuwan da ya yi a Urushalima wurin idin, domin su ma sun je idin.
Lors donc qu'il fut arrivé en Galilée, il fut bien reçu des Galiléens, qui avaient vu tout ce qu'il avait fait à Jérusalem à la fête; car ils étaient aussi allés à la fête.
46 Kuma ya koma Kana ta Galili inda ya mayar da ruwa zuwa ruwan inabi. Akwai wani ma'aikacin fada wanda dansa na rashin lafiya a Kafarnahum.
Jésus vint donc de nouveau à Cana en Galilée, où il avait changé l'eau en vin. Or, il y avait à Capernaüm un seigneur de la cour, dont le fils était malade.
47 Da ya ji cewa Yesu ya bar Yahudiya ya koma Galili, sai ya tafi wurin Yesu ya roke shi ya sauko ya warka da dansa wanda ke bakin mutuwa.
Cet homme, ayant appris que Jésus était venu de Judée en Galilée, s'en alla vers lui et le pria de descendre pour guérir son fils, car il allait mourir.
48 Yesu yace masa, “Idan ba ku ga alamu da mu'ujizai ba, ba za ku gaskata ba.”
Jésus lui dit: Si vous ne voyiez point de signes et de miracles, vous ne croiriez point.
49 Ma'aikacin ya ce masa, “Mallam, ka sauko kafin da na ya mutu.”
Ce seigneur de la cour lui dit: Seigneur, descends, avant que mon enfant ne meure.
50 Yesu yace masa, “Je ka. Dan ka ya rayu.” Mutumin ya gaskata maganar da Yesu ya gaya masa, Sai yayi tafiyarsa.
Jésus lui dit: Va, ton fils vit. Cet homme crut ce que Jésus lui avait dit, et s'en alla.
51 Yayin da yake sauka kasa, bayinsa suka same shi, suna cewa, danka yana raye.
Et comme il descendait, ses serviteurs vinrent au-devant de lui, et lui annoncèrent cette nouvelle: Ton fils vit.
52 Sai ya tambaye su sa'ar da ya fara samun sauki. Suka amsa masa, “Jiya a sa'a ta bakwai zazabin ya bar shi.”
Il leur demanda à quelle heure il s'était trouvé mieux. Et ils lui dirent: Hier, à la septième heure, la fièvre le quitta.
53 Sai Uban ya gane cewa wannan sa'a ce Yesu ya ce masa, “Jeka, danka na raye.” Sabili da haka, shi da dukan gidansa suka bada gaskiya.
Et le père reconnut que c'était à cette heure-là que Jésus lui avait dit: Ton fils vit; et il crut, lui et toute sa maison.
54 Wannan ce alama ta biyu da Yesu ya yi bayan da ya bar Yahudiya zuwa Galili.
Jésus fit ce second miracle à son retour de Judée en Galilée.

< Yohanna 4 >