< Luka 1 >
1 Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
Plusieurs ayant entrepris d'écrire l'histoire des choses dont la vérité a été pleinement établie parmi nous;
2 kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
Selon que nous les ont transmises ceux qui dès le commencement les ont vues eux-mêmes, et qui ont été les ministres de la Parole;
3 Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
J'ai cru aussi, très excellent Théophile, que je devais te les écrire par ordre, moi qui les ai toutes examinées avec soin;
4 Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
Afin que tu reconnaisses la certitude des choses dont tu as été instruit.
5 A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
Au temps d'Hérode, roi de Judée, il y avait un sacrificateur nommé Zacharie, du rang d'Abia; sa femme était de la race d'Aaron, et elle s'appelait Élisabeth.
6 Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
Ils étaient tous deux justes devant Dieu, et ils suivaient tous les commandements et toutes les ordonnances du Seigneur, d'une manière irréprochable.
7 Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
Ils n'avaient point d'enfants, parce qu'Élisabeth était stérile, et qu'ils étaient tous deux avancés en âge.
8 Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
Or, il arriva comme Zacharie faisait les fonctions de sacrificateur devant Dieu, selon l'ordre de son rang,
9 Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
Qu'il lui échut par le sort, selon la coutume de la sacrificature, d'entrer dans le temple du Seigneur, pour y offrir les parfums.
10 Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
Et toute la multitude du peuple était dehors en prières, à l'heure des parfums.
11 A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
Alors un ange du Seigneur lui apparut, se tenant debout au côté droit de l'autel des parfums.
12 Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
Et Zacharie le voyant, fut troublé, et la frayeur le saisit.
13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
Mais l'ange lui dit: Zacharie, ne crains point; car ta prière est exaucée, et Élisabeth ta femme t'enfantera un fils, et tu lui donneras le nom de Jean.
14 Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
Il sera pour toi un sujet de joie et de ravissement, et plusieurs se réjouiront de sa naissance.
15 Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
Car il sera grand devant le Seigneur; il ne boira ni vin, ni boisson forte, et il sera rempli du Saint-Esprit dès le sein de sa mère;
16 Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
Il convertira plusieurs des enfants d'Israël au Seigneur leur Dieu,
17 Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
Et il marchera devant lui dans l'esprit et avec la vertu d'Élie, pour tourner les cœurs des pères vers les enfants, et les rebelles à la sagesse des justes, afin de préparer au Seigneur un peuple bien disposé.
18 Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
Et Zacharie dit à l'ange: A quoi connaîtrai-je cela? Car je suis vieux, et ma femme est avancée en âge?
19 Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
Et l'ange lui répondit: Je suis Gabriel, qui assiste devant Dieu; et j'ai été envoyé pour te parler et t'annoncer ces bonnes nouvelles.
20 Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
Et voici, tu vas devenir muet, et tu ne pourras parler jusqu'au jour où ces choses arriveront, parce que tu n'as pas cru à mes paroles, qui s'accompliront en leur temps.
21 Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
Cependant, le peuple attendait Zacharie, et s'étonnait de ce qu'il tardait si longtemps dans le temple.
22 Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
Et quand il fut sorti, il ne pouvait leur parler, et ils connurent qu'il avait eu une vision dans le temple, parce qu'il le leur faisait entendre par des signes; et il demeura muet.
23 Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
Et lorsque les jours de son ministère furent achevés, il s'en alla en sa maison.
24 Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
Quelque temps après, Élisabeth sa femme conçut; elle se cacha durant cinq mois, et disait:
25 “Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
C'est là ce que le Seigneur a fait en ma faveur, au jour où il a jeté les yeux sur moi, pour ôter mon opprobre du milieu des hommes.
26 A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
Or, au sixième mois, Dieu envoya l'ange Gabriel dans une ville de Galilée,
27 zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
appelée Nazareth, à une vierge fiancée à un homme nommé Joseph, de la maison de David; et cette vierge s'appelait Marie.
28 Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
Et l'ange étant entré auprès d'elle, lui dit: Je te salue, toi qui as été reçue en grâce; le Seigneur est avec toi; tu es bénie entre les femmes.
29 Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
Et ayant vu l'ange, elle fut troublée de son discours, et elle pensait en elle-même ce que pouvait être cette salutation.
30 Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
Alors l'ange lui dit: Marie, ne crains point, car tu as trouvé grâce devant Dieu.
31 Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
Et tu concevras et tu enfanteras un fils, et tu appelleras son nom JÉSUS.
32 Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
Il sera grand, et sera appelé Fils du Très-Haut, et le Seigneur Dieu lui donnera le trône de David son père.
33 Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
Il régnera éternellement sur la maison de Jacob, et il n'y aura point de fin à son règne. (aiōn )
34 Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
Alors Marie dit à l'ange: Comment cela se fera-t-il, puisque je ne connais point d'homme?
35 Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
Et l'ange lui répondit: Le Saint-Esprit viendra sur toi, et la puissance du Très-Haut te couvrira de son ombre; c'est pourquoi aussi le saint enfant qui naîtra de toi sera appelé le Fils de Dieu.
36 Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
Et voilà, Élisabeth ta parente a aussi conçu un fils en sa vieillesse; et c'est ici le sixième mois de celle qui était appelée stérile.
37 Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
Car rien n'est impossible à Dieu.
38 Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
Et Marie dit: Voici la servante du Seigneur; qu'il me soit fait selon ta parole. Et l'ange se retira d'auprès d'elle.
39 Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
Alors Marie se leva, et s'en alla en hâte au pays des montagnes, dans une ville de Juda.
40 Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
Et étant entrée dans la maison de Zacharie, elle salua Élisabeth.
41 Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
Et aussitôt qu'Élisabeth eut entendu la salutation de Marie, le petit enfant tressaillit dans son sein, et Élisabeth fut remplie du Saint-Esprit.
42 Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
Et élevant la voix, elle s'écria: Tu es bénie entre les femmes, et le fruit de ton sein est béni.
43 Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
Et d'où me vient ceci, que la mère de mon Seigneur vienne me visiter?
44 Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
Car la voix de ta salutation n'a pas plutôt frappé mes oreilles, que le petit enfant a tressailli de joie dans mon sein.
45 Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
Et heureuse est celle qui a cru; car les choses qui lui ont été dites de la part du Seigneur auront leur accomplissement.
46 Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
Alors Marie dit: Mon âme magnifie le Seigneur,
47 kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
Et mon esprit se réjouit en Dieu mon Sauveur;
48 Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
Parce qu'il a regardé la bassesse de sa servante. Et voici désormais tous les âges me diront bienheureuse.
49 Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
Car le Tout-Puissant m'a fait de grandes choses; son nom est saint;
50 Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
Et sa miséricorde s'étend d'âge en âge sur ceux qui le craignent.
51 Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
Il a déployé la force de son bras; il a dissipé les desseins que les orgueilleux formaient dans leur cœur;
52 Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
Il a détrôné les puissants, et il a élevé les petits;
53 Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
Il a rempli de biens ceux qui avaient faim, et il a renvoyé les riches à vide.
54 Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
Il a pris en sa protection Israël son serviteur;
55 (kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
Et comme il en avait parlé à nos pères, il s'est souvenu de sa miséricorde envers Abraham et sa postérité pour toujours. (aiōn )
56 Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
Et Marie demeura avec elle environ trois mois; puis elle s'en retourna en sa maison.
57 Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
Or, le terme d'Élisabeth étant venu, elle enfanta un fils.
58 Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
Et ses voisins et ses parents, ayant appris que le Seigneur avait fait éclater sa miséricorde en sa faveur, s'en réjouissaient avec elle.
59 Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
Et étant venus le huitième jour pour circoncire le petit enfant, ils l'appelaient Zacharie, du nom de son père.
60 amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
Mais sa mère prit la parole et dit: Non, mais il sera nommé Jean.
61 Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
Ils lui dirent: Il n'y a personne dans ta parenté qui soit appelé de ce nom.
62 Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
Alors ils demandèrent par signe à son père comment il voulait qu'il fût nommé.
63 Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
Et Zacharie ayant demandé des tablettes, écrivit ces mots: Jean est son nom; et ils en furent tous surpris.
64 Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
A l'instant sa bouche s'ouvrit, sa langue fut déliée, et il parlait en bénissant Dieu.
65 Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
Et tous leurs voisins furent remplis de crainte, et toutes ces choses se divulguèrent par tout le pays des montagnes de Judée.
66 Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
Et tous ceux qui les entendirent, les conservèrent dans leur cœur, et disaient: Que sera donc ce petit enfant? Et la main du Seigneur était avec lui.
67 Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
Alors Zacharie son père fut rempli du Saint-Esprit, et il prophétisa, en disant:
68 “Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
Béni soit le Seigneur, le Dieu d'Israël, de ce qu'il a visité et racheté son peuple,
69 Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
Et de ce qu'il nous a suscité un puissant Sauveur, dans la maison de David son serviteur;
70 kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
Comme il en avait parlé par la bouche de ses saints prophètes, depuis longtemps; (aiōn )
71 Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
De ce qu'il nous a sauvés de nos ennemis, et de la main de tous ceux qui nous haïssent,
72 Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
Pour exercer sa miséricorde envers nos pères, et se souvenir de sa sainte alliance,
73 rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
Savoir du serment qu'il avait fait à Abraham notre père,
74 Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
De nous accorder que, étant délivrés de la main de nos ennemis, nous le servirions sans crainte,
75 a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
Dans la sainteté et dans la justice, en sa présence, tous les jours de notre vie.
76 I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
Et toi, petit enfant, tu seras appelé le prophète du Très-Haut; car tu marcheras devant la face du Seigneur, pour préparer ses voies,
77 domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
Afin de donner la connaissance du salut à son peuple, dans la rémission de leurs péchés,
78 Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
Par les entrailles de la miséricorde de notre Dieu, par lesquelles le soleil levant nous a visités d'en haut;
79 domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
Pour éclairer ceux qui sont assis dans les ténèbres et dans l'ombre de la mort, et pour conduire nos pas dans le chemin de la paix.
80 Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.
Et le petit enfant croissait et se fortifiait en esprit; et il demeura dans les déserts jusqu'au jour où il devait être manifesté à Israël.