< Yohanna 3 >
1 akwai wani Bafarise da ake kira Nikodimu, shugaba a cikin Yahudawa.
Now there was one of the Pharisees whose name was Nicodemus--a ruler among the Jews.
2 Wannan mutum ya zo wurin Yesu da dare ya ce masa, “Rabbi, mun sani cewa kai malami ne da kazo daga wurin Allah, gama ba wanda zai iya yin wadannan alamu da kake yi sai idan Allah na tare da shi.”
He came to Jesus by night and said, "Rabbi, we know that you are a teacher from God; for no one can do these miracles which you are doing, unless God is with him.
3 Yesu ya amsa masa, “Hakika, hakika, idan ba a sake haifuwar mutum ba, ba zai iya ganin mulkin Allah ba.”
"In most solemn truth I tell you," answered Jesus, "that unless a man is born anew he cannot see the Kingdom of God."
4 Nikodimu ya ce masa, “Yaya za a sake haifuwar mutum bayan ya tsufa? Ba zai iya sake shiga cikin cikin uwarsa kuma a haife shi ba, zai iya?”
"How is it possible," Nicodemus asked, "for a man to be born when he is old? Can he a second time enter his mother's womb and be born?"
5 Yesu ya amsa, “Hakika, hakika, idan ba a haifi mutum da ruwa da kuma Ruhu ba, ba zai iya shiga cikin mulkin Allah ba.
"In most solemn truth I tell you," replied Jesus, "that unless a man is born of water and the Spirit, he cannot enter the Kingdom of God.
6 Abin da aka haifa ta wurin jiki, jiki ne, kuma abin da aka haifa ta wurin Ruhu, Ruhu ne.
Whatever has been born of the flesh is flesh, and whatever has been born of the Spirit is spirit.
7 Kada ka yi mamaki don na ce maka, 'dole a maya haifuwar ka.'
Do not be astonished at my telling you, 'You must all be born anew.'
8 Iska takan hura duk inda ta ga dama. Ka kan ji motsin ta, amma ba ka san inda ta fito ko inda za ta tafi ba. Haka duk wanda aka haifa daga Ruhu.”
The wind blows where it chooses, and you hear its sound, but you do not know where it comes from or where it is going. So is it with every one who has been born of the Spirit."
9 Nikodimu ya amsa yace masa, “Yaya wannan zai yiwu?”
"How is all this possible?" asked Nicodemus.
10 Yesu ya amsa yace masa, “Kai malami ne a Israila amma ba ka san wadannan al'amura ba?
"Are you," replied Jesus, "'the Teacher of Israel,' and yet do you not understand these things?
11 Hakika, hakika, ina gaya maka, muna fadin abubuwan da muka sani, kuma muna shaida abubuwan da muka gani. Duk da haka ba ku karbi shaidar mu ba.
In most solemn truth I tell you that we speak what we know, and give testimony of that of which we were eye-witnesses, and yet you all reject our testimony.
12 Idan na gaya maka abubuwan da ke na duniya amma baka gaskata ba, to yaya zaka gaskata idan na gaya maka abubuwa na sama?
If I have told you earthly things and none of you believe me, how will you believe me if I tell you of things in Heaven?
13 Babu wanda ya taba hawa zuwa sama sai dai shi wanda ya sauko daga sama: wato Dan Mutum.
There is no one who has gone up to Heaven, but there is One who has come down from Heaven, namely the Son of Man whose home is in Heaven.
14 Kamar yadda Musa ya ta da maciji a jeji, haka ma dole a ta da Dan Mutum
And just as Moses lifted high the serpent in the Desert, so must the Son of Man be lifted up,
15 domin dukan wadanda suka bada gaskiya gareshi su sami rai na har abada. (aiōnios )
in order that every one who trusts in Him may have the Life of the Ages." (aiōnios )
16 Gama Allah ya kaunaci duniya sosai, har ya ba da makadaicin Dansa, domin duk wanda ya bada gaskiya gareshi, kada ya mutu, amma ya samu rai madawwami. (aiōnios )
For so greatly did God love the world that He gave His only Son, that every one who trusts in Him may not perish but may have the Life of Ages. (aiōnios )
17 Gama Allah bai aiko da Dansa cikin duniya domin ya kayar da duniya ba, amma domin a ceci duniya ta wurin sa.
For God did not send His Son into the world to judge the world, but that the world might be saved through Him.
18 Duk wanda ya bada gaskiya gare shi ba a kayar da shi ba, amma duk wanda bai bada gaskiya gare shi ba an riga an kayar da shi, domin bai bada gaskiya ga sunan wannan da shi kadai ne Dan Allah ba.
He who trusts in Him does not come up for judgement. He who does not trust has already received sentence, because he has not his trust resting on the name of God's only Son.
19 Wannan shi ne dalilin shari'ar, domin haske ya zo duniya, amma mutane suka kaunaci duhu fiye da hasken, sabili da ayyukan su na mugunta ne.
And this is the test by which men are judged--the Light has come into the world, and men loved the darkness more than they loved the Light, because their deeds were wicked.
20 Domin duk wanda ke mugayen ayyuka ya ki haske, kuma baya zuwa wurin hasken domin kada ayyukansa su bayyanu.
For every wrongdoer hates the light, and does not come to the light, for fear his actions should be exposed and condemned.
21 Sai dai duk wanda yake aikata gaskiya kan zo wurin hasken domin ayyukansa, da ake aiwatarwa ga Allah, su bayyanu.
But he who does what is honest and right comes to the light, in order that his actions may be plainly shown to have been done in God.
22 Bayan wannan, Yesu da almajiransa suka tafi kasar Yahudiya. A can ya dan zauna tare da su ya kuma yi Baftisma.
After this Jesus and His disciples went into Judaea; and there He made a stay in company with them and baptized.
23 Yahaya ma yana Baftisma a Ainon kusa da Salim domin akwai ruwa da yawa a can. Mutane na zuwa wurin sa yana masu Baftisma,
And John too was baptizing at Aenon, near Salim, because there were many pools of water there; and people came and received baptism.
24 domin a lokacin ba a jefa Yahaya a kurkuku ba tukuna.
(For John was not yet in prison.)
25 Sai gardama ta taso tsakanin almajiran Yahaya da wani Bayahude akan al'adun tsarkakewa.
As the result, a discussion having arisen on the part of John's disciples with a Jew about purification,
26 Suka je wurin Yahaya suka ce, “Rabbi, wanda yake tare da kai a dayan ketaren kogin Urdun, kuma ka shaida shi, duba, yana baftisma, kuma mutane duka suna zuwa wurin sa.”
they came to John and reported to him, "Rabbi, he who was with you on the other side of the Jordan and to whom you bore testimony is now baptizing, and great numbers of people are resorting to him."
27 Yahaya ya amsa, “Mutum ba zai iya samun wani abu ba sai an ba shi daga sama.
"A man cannot obtain anything," replied John, "unless it has been granted to him from Heaven.
28 Ku da kanku zaku shaida na ce, 'Ba ni ne Almasihu ba' amma amaimakon haka, 'an aiko ni kafin shi.'
You yourselves can bear witness to my having said, 'I am not the Christ,' but 'I am His appointed forerunner.'
29 Amaryar ta angon ce. Yanzu abokin angon, wanda ke tsaye yana saurarensa, yana murna sosai saboda muryan angon. Murnata ta cika domin wannan.
He who has the bride is the bridegroom; and the bridegroom's friend who stands by his side and listens to him, rejoices heartily on account of the bridegroom's happiness. Therefore this joy of mine is now complete.
30 Dole shi ya karu, ni kuma in ragu.
He must grow greater, but I must grow less.
31 Shi wanda ya fito daga sama ya fi kowa. Shi Wanda ya zo daga duniya, na duniya ne, kuma game da duniya yake magana. Shi wanda ya fito daga sama yana saman kowa.
He who comes from above is above all. He whose origin is from the earth is not only himself from the earth, his teaching also is from the earth. He who comes from Heaven is above all.
32 Ya shaida abubuwan da ya ji ya kuma gani, amma babu wanda ya karbi shaidarsa.
What He has seen and heard, to that He bears witness; but His testimony no one receives.
33 Duk wanda ya karbi shaidarsa ya tabbatar Allah gaskiya ne.
Any man who has received His testimony has solemnly declared that God is true.
34 Domin duk wanda Allah ya aika kan yi magana da kalmomin Allah. Domin bai bada Ruhun da ma'auni ba.
For He whom God has sent speaks God's words; for God does not give the Spirit with limitations."
35 Uban ya kaunaci Dan, ya kuma ba da dukan komai a hanunsa.
The Father loves the Son and has entrusted everything to His hands.
36 Shi wanda ya bada gaskiya ga Dan ya na da rai madawwami, amma wanda ya ki yiwa Dan biyayya ba zai ga rai ba, amma fushin Allah na kansa. (aiōnios )
He who believes in the Son has the Life of the Ages; he who disobeys the Son will not enter into Life, but God's anger remains upon him. (aiōnios )