< Yohanna 1 >
1 A cikin farko akwai Kalma, Kalmar kuma tana tare da Allah, wannan Kalma kuwa Allah ne.
In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
2 Shi kuwa tare da Allah yake tun farko.
He was in the beginning with God.
3 Dukan abu ta wurinsa aka yi su, babu abin da aka halitta sai ta wurin sa.
All things came into being through Him, and apart from Him nothing that exists came into being.
4 A cikinsa rai ya ke, kuma wannan rai ya zama haske ga dukan mutane.
In Him was Life, and that Life was the Light of men.
5 Hasken ya haskaka a cikin duhu, kuma duhun bai rinjaye shi ba.
The Light shines in the darkness, and the darkness has not overpowered it.
6 Akwai wani mutum wanda Allah ya aiko, mai suna Yahaya.
There was a man sent from God, whose name was John.
7 Ya zo a matsayin mai ba da shaida game da hasken, domin kowa ya ba da gaskiya ta wurinsa.
He came as a witness, in order that he might give testimony concerning the Light--so that all might believe through him.
8 Ba Yahaya ne hasken ba, amma ya zo ne domin ya shaida hasken.
He was not the Light, but he existed that he might give testimony concerning the Light.
9 Wannan shine haske na gaskiya mai ba da haske ga dukan mutane, da ke zuwa cikin duniya.
The true Light was that which illumines every man by its coming into the world.
10 Yana cikin duniya, kuma an halicci duniya ta wurinsa, amma duniya bata san shi ba.
He was in the world, and the world came into existence through Him, and the world did not recognize Him.
11 Ya zo wurin nasa, amma nasa basu karbe shi ba.
He came to the things that were His own, and His own people gave Him no welcome.
12 Amma duk iyakar wadanda suka karbe shi, suka kuma ba da gaskiya ga sunansa, ya ba su 'yanci su zama 'ya'yan Allah.
But all who have received Him, to them--that is, to those who trust in His name--He has given the privilege of becoming children of God;
13 Wadanda aka haife su ba ta wurin jini ba, ko ta wurin nufin jiki, ko nufin mutum, amma ta wurin Allah.
who were begotten as such not by human descent, nor through an impulse of their own nature, nor through the will of a human father, but from God.
14 Kalmar kuma ya zama jiki ya zauna cikin mu. Mun ga daukakarsa, daukaka irin ta makadaici shi kadai wanda ya zo daga Uban, cike da alheri da gaskiya.
And the Word came in the flesh, and lived for a time in our midst, so that we saw His glory--the glory as of the Father's only Son, sent from His presence. He was full of grace and truth.
15 Yahaya ya yi shaida akansa yana kira da karfi, cewa, “Wannan shine wanda na yi magana a kansa cewa, 'Shi wanda ke zuwa bayana, ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'”
John gave testimony concerning Him and cried aloud, saying, "This is He of whom I said, 'He who is coming after me has been put before me,' for He was before me."
16 Domin daga cikarsa ne muka karbi alheri akan alheri.
For He it is from whose fulness we have all received, and grace upon grace.
17 Gama shari'a ta zo daga wurin Musa. Alheri da gaskiya sun zo ta wurin Yesu Almasihu.
For the Law was given through Moses; grace and truth came through Jesus Christ.
18 Babu lokacin da wani ya taba ganin Allah, shi wanda shi kadai ne Allah, wanda ke jingine da kirjin Uba, shi ya bayyana shi.
No human eye has ever seen God: the only Son, who is in the Father's bosom--He has made Him known.
19 Wannan ita ce shaidar Yahaya sa'adda Yahudawa suka aika da Firistoci da Lawiyawa zuwa gareshi don su tambaye shi, “Wanene kai?”
This also is John's testimony, when the Jews sent to him a deputation of Priests and Levites from Jerusalem to ask him who he was.
20 Ya fada dalla dalla, kuma bai musunta ba, yana amsa masu cewa, “ba nine Almasihu ba.”
He avowed--he did not conceal the truth, but avowed, "I am not the Christ."
21 Sai suka tambaye shi, “To kai wanene? Kai Iliya ne?” Yace, “Ba ni ba ne.” Suka ce, “Kai ne anabin?” Ya amsa, “A'a”.
"What then?" they inquired; "are you Elijah?" "I am not," he said. "Are you the Prophet?" "No," he answered.
22 Sai suka ce masa, “Kai wanene, domin mu bada amsa ga wadanda suka aiko mu? Me kake fadi game da kanka?”
So they pressed the question. "Who are you?" they said--"that we may take an answer to those who sent us. What account do you give of yourself?"
23 Yace, “Ni murya ne, da ke kira cikin jeji, 'Ku daidaita hanyar Ubangiji,' kamar yadda annabi Ishaya ya fada.”
"I am the voice," he replied, "of one crying aloud, 'Make straight the Lord's way in the Desert,' fulfilling the words of the Prophet Isaiah."
24 Su wadanda aka aika daga wurin Farisawa suke. Sai suka tambaye shi cewa,
They were Pharisees who had been sent.
25 “To don me kake baftisma idan kai ba Almasihu bane, ko Iliya, ko annabin?”.
Again they questioned him. "Why then do you baptize," they said, "if you are neither the Christ nor Elijah nor the Prophet?"
26 Yahaya ya amsa masu, cewa, “Ina baftisma ne da ruwa. Amma a cikinku akwai wani tsaye wanda ba ku sani ba,
"I baptize in water only," John answered, "but in your midst stands One whom you do not know--
27 shi wanda ke zuwa bayana, wanda ko igiyar takalminsa ban isa in kwance ba.”
He who is to come after me, and whose sandal-strap I am not worthy to unfasten."
28 Wadannan abubuwa sun faru ne a Baitanya, a dayan ketaren Urdun, a wurin da Yahaya ke Baftisma.
This conversation took place at Bethany beyond the Jordan, where John was baptizing.
29 Washegari, Yahaya ya ga Yesu yana zuwa wurinsa ya ce, “Duba, ga Dan Ragon Allah wanda ke dauke zunubin duniya!
The next day John saw Jesus coming towards him and exclaimed, "Look, that is the Lamb of God who is to take away the sin of the world!
30 Wannan shine wanda na fada maku cewa, “Shi wanda ke zuwa bayana ya fi ni, domin ya kasance kafin ni.'
This is He about whom I said, 'After me is to come One who has been put before me, because He was before me.'
31 Ban san shi ba, amma saboda a bayyana shi ga Isra'ila ne nazo ina baftisma da ruwa. “
I did not yet know Him; but that He may be openly shown to Israel is the reason why I have come baptizing in water."
32 Yahaya ya shaida, cewa, “Na ga Ruhu yana saukowa kamar kurciya daga sama, ya kuma zauna a kansa.
John also gave testimony by stating: "I have seen the Spirit coming down like a dove out of Heaven; and it remained upon Him.
33 Ban gane shi ba, amma shi wanda ya aiko ni in yi baftisma cikin ruwa ya fada mani cewa, 'duk wanda ka ga Ruhun ya sauka kuma ya zauna a kansa, shine wanda ke yin baftisma cikin Ruhu mai tsarki.'
I did not yet know Him, but He who sent me to baptize in water said to me, "'The One on whom you see the Spirit coming down, and remaining, He it is who baptizes in the Holy Spirit.'
34 Na gani, na kuma shaida cewa wannan shine Dan Allah.”
"This I have seen, and I have become a witness that He is the Son of God."
35 Kuma, washegari, da Yahaya na tsaye da biyu daga cikin almajiransa,
Again the next day John was standing with two of his disciples,
36 suka ga Yesu na wucewa, sai Yahaya ya ce, “Duba, ga Dan rago na Allah!”
when he saw Jesus passing by, and said, "Look! that is the Lamb of God!"
37 Sai almajiransa biyu suka ji ya fadi haka, suka kuwa bi Yesu.
The two disciples heard his exclamation, and they followed Jesus.
38 Da Yesu ya waiwaya ya gan su suna bin sa, sai ya ce masu, “Me kuke so?” Suka amsa, “Rabbi (wato 'Mallam'), ina kake da zama?”
Then Jesus turned round, and seeing them following He asked them, "What is your wish?" "Rabbi," they replied--'Rabbi' means 'Teacher' --"where are you staying?"
39 Yace masu, “Zo ku gani.” Sai suka zo suka ga inda yake zama; suka zauna da shi ranan nan, gama wajen sa'a ta goma ne.
"Come and you shall see," He said. So they went and saw where He was staying, and they remained and spent that day with Him. It was then about ten o'clock in the morning.
40 Daya daga cikin wadanda suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu shine Andarawus, dan'uwan Siman Bitrus.
Andrew, Simon Peter's brother, was one of the two who heard John's exclamation and followed Jesus.
41 Ya fara neman dan'uwansa Siman yace masa, “Mun sami Almasihu” (wanda ake kira 'Kristi').
He first found his own brother Simon, and said to him, "We have found the Messiah!" --that is to say, the Anointed One.
42 Ya kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi yace, “Kai ne Siman dan Yahaya. Za a kira ka Kefas,” (ma'ana, 'Bitrus').
He brought him to Jesus. Jesus looked at him and said, "You are Simon, son of John: you shall be called Cephas" --that is to say, Peter (or 'Rock').
43 Washegari, da Yesu yana shirin tafiya zuwa Galili, sai ya sami Filibus, ya ce masa, “ka biyo ni.”
The next day, having decided to leave Bethany and go into Galilee, Jesus found Philip, and invited him to follow Him.
44 Filibus dan asalin Baitsaida ne, garin Andarawus da Bitrus.
(Now Philip came from Bethsaida, the same town as Andrew and Peter.)
45 Filibus ya sami Natana'ilu yace masa, “Mun same shi, shi wanda Musa ya rubuta shi a cikin attaura, da annabawa: Yesu Dan Yusufu, Ba-Nazarat.”
Then Philip found Nathanael, and said to him, "We have found him about whom Moses in the Law wrote, as well as the Prophets--Jesus, the son of Joseph, a man of Nazareth."
46 Natana'ilu ya ce masa, “za a iya samun wani abu nagari a Nazarat?” Filibus yace masa, “Zo ka gani.”
"Can anything good come out of Nazareth?" replied Nathanael. "Come and see," said Philip.
47 Yesu ya ga Natana'ilu yana zuwa wurinsa sai yayi magana game da shi, “Duba, Ba-Isra'ile na hakika wanda babu yaudara a cikinsa.”
Jesus saw Nathanael approaching, and said of him, "Look! here is a true Israelite, in whom there is no deceitfulness!"
48 Natana'ilu yace masa, “Ta yaya ka san ni?” Sai Yesu ya amsa masa yace, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'adda kake a gindin baure, na gan ka.”
"How do you know me?" Nathanael asked. "Before Philip called you," said Jesus, "when you were under the fig-tree I saw you."
49 Natana'ilu ya amsa, “Rabbi, Kai Dan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!”
"Rabbi," cried Nathanael, "you are the Son of God, you are Israel's King!"
50 Yesu ya amsa masa yace, “Don na ce maka, 'Na gan ka a gindin Baure', ka gaskanta? Za ka ga abubuwa da suka fi wannan girma.”
"Because I said to you, 'I saw you under the fig-tree,'" replied Jesus, "do you believe? You shall see greater things than that."
51 Sai yace, 'Hakika, hakika ina gaya maka, zaka ga sammai a bude, mala'ikun Allah kuma suna hawa suna sauka akan Dan Mutum.”
"I tell you all in most solemn truth," He added, "that you shall see Heaven opened wide, and God's angels going up, and coming down to the Son of Man."