< Galatiyawa 1 >
1 Wannan Bulus manzo ne. Manzancina kuwa, bai zo daga mutane ba ko mutum, amma ta wurin Yesu Almasihu da Allah Uba wanda da ya tashe shi daga matattu.
Paul Apôtre, non de la part des hommes, ni de la part d'aucun homme, mais de la part de Jésus-Christ, et de la part de Dieu le Père, qui l'a ressuscité des morts;
2 Ni da dukan 'yan'uwa da nake tare da su a nan, ina rubuto maku ku iklisiyoyi da ke a Galatiya.
Et tous les frères qui sont avec moi, aux Eglises de Galatie.
3 Alheri zuwa gare ku da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangjinmu Yesu Almasihu,
Que la grâce et la paix vous soient données de la part de Dieu le Père, et de la part de notre Seigneur Jésus-Christ:
4 wanda ya ba da kansa domin zunubanmu saboda ya kubutar da mu daga wannan mugun zamani, bisa ga nufin Allah da Ubanmu. (aiōn )
Qui s'est donné lui-même pour nos péchés, afin que selon la volonté de Dieu notre Père, il nous retirât du présent siècle mauvais. (aiōn )
5 Daukaka ta tabbata a gare shi har abada abadin. (aiōn )
A lui soit gloire aux siècles des siècles; Amen! (aiōn )
6 Na yi mamaki kwarai yadda kuka juya da sauri zuwa wata bishara daban. Na yi mamakin cewa kuna juyawa daga shi wanda ya kira ku ta wurin alherin Almasihu.
Je m'étonne qu'abandonnant [Jésus-] Christ, qui vous avait appelés par sa grâce, vous ayez été si promptement transportés à un autre Evangile.
7 Ba wata bishara, amma akwai wadansu mutane da suke kawo maku rudani kuma suna so su gurbata bisharar Almasihu.
Qui n'est pas un autre [Evangile], mais il y a des gens qui vous troublent, et qui veulent renverser l'Evangile de Christ.
8 Amma, ko da mu ne ko mala'ika daga sama ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda muka yi shelar ta, la'ananne ne.
Mais quand nous-mêmes [vous évangéliserions], ou quand un Ange du Ciel vous évangéliserait outre ce que nous vous avons évangélisé, qu'il soit anathème.
9 Kamar yadda muka fadi maku a da, yanzu kuma ina sake fada, “Idan wani ya yi maku shelar wata bishara ta daban da wadda kuka karba, la'ananne ne.”
Comme nous l'avons déjà dit, je le dis encore maintenant: si quelqu'un vous évangélise outre ce que vous avez reçu, qu'il soit anathème.
10 To yanzu ina neman shaidar mutane ne ko Allah? Ina neman in gamshi mutane ne? Idan har yanzu ina kokarin in gamshi mutane ne, ni ba bawan Almasihu ba ne.
Car maintenant prêché-je les hommes, ou Dieu? ou cherché-je à complaire aux hommes? Certes si je complaisais encore aux hommes, je ne serais pas le serviteur de Christ.
11 Ina son ku sani fa 'yan'uwa, cewa bisharar da nake shelar ta ba daga mutane take ba.
Or mes frères, je vous déclare que l'Evangile que j'ai annoncé, n'est point selon l'homme.
12 Ban karbe ta daga mutum ba, ba ma wanda ya koyar mani A maimakon haka, ta wurin wahayin Yesu Almasihu ne zuwa gare ni.
Parce que je ne l'ai point reçu ni appris d'aucun homme, mais par la révélation de Jésus-Christ.
13 Kun riga kun ji game da rayuwa ta a da cikin Yahudanci, yadda da nake da kwazon tsananta wa iklisiyar Allah fiye da misali kuma ina lalatar da ita.
Car vous avez appris quelle a été autrefois ma conduite dans le Judaïsme, [et] comment je persécutais à outrance l'Eglise de Dieu, et la ravageais;
14 Ina gaba-gaba cikin Yahudanci fiye da yawancin tsararrakina. A kwazo kuwa fiye da kima game da al'adun ubannina.
Et j'avançais dans le Judaïsme plus que plusieurs de mon âge dans ma nation; étant le plus ardent zélateur des traditions de mes pères.
15 Amma ya gamshi Allah ya zabe ni daga cikin mahaifiyata. Ya kira ni ta wurin alherinsa.
Mais quand ç'a été le bon plaisir de Dieu, qui m'avait choisi dès le ventre de ma mère, et qui m'a appelé par sa grâce,
16 Ya bayyana dansa a gareni, saboda in yi shelar sa cikin al'ummai. Nan da nan, ban nemi shawarar nama da jini ba
De révéler son Fils en moi, afin que je l'évangélisasse parmi les Gentils, je ne commençai pas d'abord par prendre conseil de la chair et du sang;
17 kuma ban tafi Urushalima ba wurin wadanda suka zama manzanni kafin ni. Maimakon haka sai na tafi Arebiya, daga nan sai na dawo Dimashku.
Et je ne retournai point à Jérusalem vers ceux qui avaient été Apôtres avant moi, mais je m'en allai en Arabie, et je repassai à Damas.
18 Bayan shekara uku na je Urushalima don in san Kefas, na zauna da shi na kwana goma sha biyar.
Puis je retournai trois ans après à Jérusalem pour visiter Pierre, et je demeurai chez lui quinze jours.
19 Amma ban ga ko daya daga cikin manzannin ba sai Yakubu kadai, dan'uwan Ubangiji.
Et je ne vis aucun des autres Apôtres, sinon Jacques, le frère du Seigneur.
20 Duba, a gaban Allah, ba karya nake yi ba cikin abin da na rubuta maku.
Or dans les choses que je vous écris, voici, [je vous dis] devant Dieu, que je ne mens point.
21 Daga nan sai na je lardin Suriya da Kilikiya.
J'allai ensuite dans les pays de Syrie et de Cilicie.
22 Har a lokacin babu wanda ya san ni a fuska a iklisiyoyin Yahudiya da suke cikin Almasihu,
Or j'étais inconnu de visage aux Eglises de Judée qui étaient en Christ;
23 amma sai labari kawai suke ji, “Wanda a da yake tsananta mana yanzu yana shelar bangaskiyar da a da yake rusarwa.”
Mais elles avaient seulement ouï dire: celui qui autrefois nous persécutait, annonce maintenant la foi qu'il détruisait autrefois.
24 Suna ta daukaka Allah saboda ni.
Et elles glorifiaient Dieu à cause de moi.