< Ayyukan Manzanni 16 >
1 Bulus ya kuma isa Darbe da Listira, in da akwai wani almajiri mai suna Timoti a wurin, dan wata Bayahudiya wadda ta ba da gaskiya; ubansa kuwa Baheline ne.
And he came to Derbe and Lystra; and behold, a certain disciple was there, named Timothy, the son of a Jewess, who was a believer; but his father was a Greek.
2 Ana maganar kirki a kansa ta bakin 'yan'uwa da ke Listira da Ikoniyan.
A good report was given of him by the brethren in Lystra and Iconium.
3 Bulus ya yi wa Timoti kaciya, domin yana so su yi tafiya tare, domin kuma saboda Yahudawan da ke wurin, sun san cewa ubansa Baheline ne.
This man Paul wished to go with him: and he took him and circumcised him, on account of the Jews that were in those places: for they all knew that his father was a Greek.
4 Suna shiga cikin biranen, suna yi wa iklisiyoyi gargadi da su yi biyayya da umurnan da Manzanni da dattawa suka rubuta a Urushalima.
And as they went through the cities, they delivered to them the decrees that had been resolved on by the apostles and elders at Jerusalem, that they might keep them.
5 Bangaskiyar iklisiyoyi kuwa ta karu, ana kuma samun karuwa na wadanda suke ba da gaskiya kowace rana.
Therefore, the churches were established in the faith, and they increased in number daily.
6 Bulus da abokan aikin sa sun shiga cikin lardin Firigiya da Galatiya, tun da Ruhu Mai Tsarki ya hana su wa'azin kalmar a cikin yankin Asiya.
When they had gone throughout Phrygia and the region of Galatia, being forbidden by the Holy Spirit to preach the word in Asia,
7 Sun zo kusa da Misiya, da nufin shiga cikin Bitiniya, Ruhun Yesu ya hana su.
and had come to Mysia, they attempted to go into Bithynia; and the Spirit did not permit them.
8 Da suka ratse ta cikin Misiya, sai suka shiga birnin Taruwasa.
But having passed by Mysia, they came down to Troas.
9 Bulus ya ga wahayi cikin dare, wani mutumin Makidoniya na kiransa, yana cewa. ''Ka zo Makidoniya ka taimake mu''.
And, during the night, a vision appeared to Paul. A certain man of Macedonia stood and besought him, saying: Come over to Macedonia and help us.
10 Bulus, da ganin haka, ya kama hanya zuwa Makidoniya, da tunanin Allah ne ya ke so su kai wa mutanen Makidoniya bishara.
After he had seen the vision, we immediately endeavored to go into Macedonia, concluding that the Lord had called us to preach the gospel to them.
11 Da barin Taruwasa, Bulus da kungiyarsa sun shiga jirgin ruwa zuwa Samutaraki, da gari ya waye kuma sun tafi Niyafolis;
Therefore, setting sail from Troas, we came by a straight course to Samothracia, and, on the following day, to Neapolis,
12 Daga nan kuma suka tafi Filibi, birni na Makidoniya, mai muhimmanci ne a yankin Roma, in da mun yi zango kwanaki da dama.
and thence to Philippi, which is the first city of that part of Macedonia, and a colony. We remained in that city some days:
13 Ranar Asabaci mun je kofar gari, gefen rafi, da tunanin samun wurin addu'a. Mun zauna mun kuma yi magana da matan da sun taru a wurin.
and on the sabbath-day we went out of the city to the side of a river, where, as usual, was the house of prayer; and we sat down and spoke to the women who had come together.
14 Wata mace mai suna Lidiya, 'yar kasuwa ce a birnin Tiyatira, mai bautar Allah ce, ta saurare mu. Ubangiji ya bude zuciyarta, ta mai da hankali ga maganar da Bulus ke fadi.
And a certain woman, named Lydia, a seller of purple, of the city of Thyatira, who worshiped God, heard; whose heart the Lord opened to attend to the things that were spoken by Paul.
15 Sa'anda da aka yi mata Baftisma tare da mutanen gidanta, ta ce da mu, “Idan kun dauke ni mai bautar Allah, ku zo gidana ku zauna.” Sai ta rinjaye mu.
And when she and her household had been immersed, she besought us, saying: If you judge me to be faithful to the Lord, come into my house, and make it your home. And she con strained us.
16 A daidai wannan lokaci, muna tafiya wurin addu'a, wata yarinya mai ruhun duba ta hadu da mu. Iyayen gijinta na arziki da ita sosai.
And it came to pass, that as we were going to the house of prayer, there met us a certain maid-servant that had a spirit of Python, who brought much gain to her masters, by giving responses.
17 Tana bin Bulus, tare da mu, tana fadi da murya mai karfi cewa, ''Wadannan mutanen, bayin Allah mafi daukaka ne, suna sanar maku hanyar ceto ne''.
She followed Paul and us, and cried out, saying: These men are the servants of the most High God, who show us the way of salvation.
18 Ta dauki kwanaki tana haka. Amma Bulus ya yi fushi da ita ainun, ya juya ya umarci ruhun, ya ce, ''Na umarce ka, ka rabu da ita a cikin sunan Yesu Almasihu''. Ruhun ya yi biyayya ya rabu da ita nan take.
And this she continued to do for many days. But Paul, being grieved, turned and said to the spirit: I command you, in the name of Jesus Christ, to come out of her. And it came out that very hour.
19 Da iyayengijinta suka ga cewa hanyar shigar kudinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila, suka ja su cikin kasuwa suka kai su gaban mahunkunta.
And when her masters saw that the hope of their gain was gone, they seized Paul and Silas, and dragged them into the market to the rulers.
20 Da suka kai su Kotu, suka ce, ''Wadannan mutane Yahudawa ne, suna kawo tashin hankali a birninmu.
And having brought them to the magistrates, they said: These men, who are Jews, do greatly trouble our city;
21 Suna koyar da abubuwa da ba su karbuwa a gare mu, balle mu aikata, a matsayinmu na Romawa.”
and they teach customs which it is not lawful for us, who are Romans, to receive or to observe.
22 Sai jama'a gaba daya sun tayar wa Bulus da Sila; alkalan kuma sun yage rigunansu, sun ba da umarni a duki Bulus da Sila da bulala.
And the multitude rose up together against them; and the magistrates stripped off their clothes, and gave command to beat them with rods.
23 Bayan dukan, an jefa su Bulus a kurkuku, an ba mai tsaron kurkukun umurni ya kulle su da kyau, kada su gudu.
And when they had laid many stripes on them, they threw them into prison, and charged the jailer to keep them securely.
24 Shi kuma ya yi hakanan, ya sa masu sarkoki a kafafun su, kamar yadda aka umurce shi.
And having received such a charge, he put them into the inner prison, and made their feet fast in the stocks.
25 Da tsakar dare, Bulus da Sila suna yin adu'a, su na raira wakoki ga Allah, sauran 'yan sarkar su na jin su.
And at midnight Paul and Silas prayed, and sung a hymn to God; and the prisoners were listening to them.
26 Nan da nan sai ga wata girgizar kasa, wadda ta sa ginshikan kurkukun sun kadu, nan da nan kofofin kurkukun sun bude, 'yan sarka kuma, sarkokin su sun karkatse.
And suddenly there was a great earthquake, so that the foundations of the prison were shaken; and immediately all the doors were opened, and every one’s bonds were loosed.
27 Mai tsaron kurkukun ya tashi daga barci ya ga kofofin kurkukun a bude, ya zaro takobi, zai kashe kan sa, a tunanin sa, 'yan sarkar sun gudu.
And the jailer, being aroused from sleep, and seeing the doors of the prison open, drew his sword, and was about to kill himself, supposing that the prisoners had fled.
28 Amma Bulus ya ta da murya da karfi, ya ce, ''kada kayi wa kanka barna, domin dukan mu muna nan''.
But Paul called out with a loud voice, saying: Do yourself no harm, for we are all here.
29 Mai tsaron kurkukun ya aika a kawo fitila, ya shiga ciki a gurguje da rawan jiki, ya fadi a gaban Bulus da Sila,
Then he called for a light, and sprang in, and trembling, he fell down before Paul and Silas;
30 ya fitar da su waje ya ce, ''Shugabanni, me ya kamata in yi domin in tsira?''
and, having brought them out, he said: Sirs, what must I do to be saved?
31 Sun ce masa, ''ka ba da gaskiya ga Yesu Ubangiji, da kai da gidan ka, za ku sami tsira''.
They replied: Believe on the Lord Jesus Christ, and you and your house shall be saved.
32 Bulus da Sila suka fada masa maganar Ubangiji, tare da iyalinsa.
And they spoke the word of the Lord to him, and to all that were in his house.
33 Shi mai tsaron kurkukun ya dauke su cikin daren, ya wanke raunukansu, an kuma yi masa Baftisma nan da nan tare da iyalinsa.
And he took them at that hour of the night, and washed the blood from their stripes; and he was immersed, himself and all his, immediately.
34 Ya kai Bulus da Sila gidansa, ya ba su abinci. Murna ta cika gidan mai tsaron kurkukun, domin iyalin sa duka sun ba da gaskiya ga Allah.
And he brought them into his house, and set food before them, and rejoiced, believing in God, with all his house.
35 Da gari ya waye, alkalai sun ba da sako a saki Bulus da Sila.
But when it was day, the magistrates sent the lictors, saying: Release those men.
36 Mai tsaron kurkukun kuwa ya sanar wa Bulus wannan magana ta alkalan, saboda haka ya ce wa Bulus, ''Ku tafi cikin salama''.
And the jailer told these words to Paul: The magistrates have sent to release you. Now, therefore, come out, and go in peace.
37 Amma Bulus ya ce masu, “Sun yi mana duka a fili a gaban mutane mu da muke Romawa, ba a kashe mu ba, sun kuma sa mu a kurkuku; suna koran mu a asirce? Su zo da kansu su fitar da mu.
But Paul said to them: Having publicly scourged us uncondemned, us who are Romans, they threw us into prison: and do they now put us out secretly? No, verily: but let them come and lead us out.
38 Masu tsaron kurkuku sun mayar da maganar Bulus ga alkalan, wanda ya sa sun firgita, da jin cewa Bulus da Sila Romawa ne.
And the lictors told these words to the magistrates: and they were alarmed when they heard that they were Romans;
39 Alkalai da kansu sun zo sun roki Bulus da Sila; da suka fitar da su daga kurkukun, sun ce wa Bulus da Sila su bar birnin.
and they came, and entreated them, and led them out, and requested them to depart from the city.
40 Da hakanan ne Bulus da Sila suka fita daga kurkuku, sun je gidan Lidiya. Da Bulus da Sila sun ga 'yan'uwa, sun karfafa su, sa'annan suka bar birnin.
And having come out of the prison, they went into the house of Lydia; and when they had seen the brethren, they comforted them, and departed.