< Zakariya 14 >

1 Ranar Ubangiji tana zuwa sa’ad da za a raba muku ganimar da aka washe daga gare ku.
Behold, a day has come to YHWH, And your spoil has been divided in your midst.
2 Zan tara dukan al’ummai su yaƙi Urushalima; za a ci birnin da yaƙi, za a washe gidaje, a kuma yi wa mata fyaɗe. Rabin birnin zai je bauta, amma ba za a kwashe sauran mutanen daga birnin ba.
And I have gathered all the nations to Jerusalem to battle, And the city has been captured, And the houses have been spoiled, And the women are lain with, Half the city has gone forth in a removal, And the remnant of the people are not cut off from the city.
3 Sa’an nan Ubangiji zai fita yă yi yaƙi da waɗannan al’ummai, kamar yadda yake yaƙi a ranar yaƙi.
And YHWH has gone forth, And He has fought against those nations, As in the day of His fighting in a day of conflict.
4 A ranan nan ƙafafunsa za su tsaya a kan Dutsen Zaitun, gabas da Urushalima, za a kuma tsage Dutsen Zaitun kashi biyu daga gabas zuwa yamma, yă zama babban kwari, rabin dutsen zai matsa zuwa wajen arewa, rabi kuma zai matsa zuwa wajen kudu.
And His feet have stood, in that day, On the Mount of Olives, That [is] eastward before Jerusalem, And the Mount of Olives has been cleft at its midst, To the east, and to the west, a very great valley, And half of the mountain is removed toward the north, And half toward the south.
5 Za ku gudu ta wajen kwarin dutsena, gama zai miƙe har zuwa Azel. Za ku gudu kamar yadda kuka guje wa girgizar ƙasa a kwanakin Uzziya sarkin Yahuda. Sa’an nan Ubangiji Allahna zai zo, tare da duk masu tsarki.
And you have fled [to] the valley of My mountains, For the valley of the mountains joins to Azal, And you have fled as you fled before the shaking, In the days of Uzziah king of Judah, And my God YHWH has come in, All holy ones [are] with You.
6 A ranan nan ba za a kasance da haske ko sanyi ba, ko hazo mai duhu ba.
And it has come to pass in that day, The precious light is not, it is dense darkness,
7 Za tă zama rana ce ta musamman, ba yini ko dare, rana da take sananne ga Ubangiji. Sa’ad da yamma ta yi, za a yi haske.
And there has been one day, It is known to YHWH, not day nor night, And it has been at evening-time—there is light.
8 A ranan nan ruwan rai zai kwararo daga Urushalima, rabi zai gangara gabas zuwa teku rabi kuma zai gangara yamma zuwa Bahar Rum, a damina da rani.
And it has come to pass in that day, Living waters go forth from Jerusalem, Half of them to the Eastern Sea, And half of them to the Western Sea, It is in summer and in winter.
9 Ubangiji zai sama sarki bisa dukan duniya. A ranan nan za a kasance da Ubangiji ɗaya, ba wani suna kuma sai nasa.
And YHWH has become King over all the earth, In that day YHWH is one, and His Name one.
10 Ƙasar gaba ɗaya daga Geba zuwa Rimmon, kudu da Urushalima, za tă zama kamar Araba. Amma Urushalima za tă kasance a wurinta, daga Ƙofar Benyamin zuwa sashen Ƙofa ta Farko, zuwa Ƙofar Kusurwa, daga kuma Hasumiyar Hananel zuwa wurin matsin ruwan inabin sarki.
All the land is changed as a plain, From Gebo to Rimmon, south of Jerusalem, And she has been high, and has dwelt in her place, Even from the Gate of Benjamin To the place of the first gate, to the front gate, And from the Tower of Hananeel, To the wine-vats of the king.
11 Za a zauna a cikinka; ba za a ƙara hallaka ta ba. Urushalima za tă zauna lafiya.
And they have dwelt in her, And destruction is no more, And Jerusalem has dwelt confidently.
12 Ga bala’in da Ubangiji zai bugi dukan al’umman da suka yi yaƙi da Urushalima. Fatar jikinsu za tă ruɓe tun suna tsaye a ƙafafunsu, idanunsu za su ruɓe a cikin kwarminsu, harsunansu kuma zai ruɓe a cikin bakunansu.
And this is the plague with which YHWH plagues all the peoples who have warred against Jerusalem: He has consumed away its flesh, And it is standing on its feet, And its eyes are consumed in their holes, And its tongue is consumed in their mouth.
13 A ranan nan Ubangiji zai sa maza su cika da tsoro ƙwarai. Kowane mutum zai kama hannun ɗan’uwansa, za su kai wa juna hari.
And it has come to pass in that day, A great destruction [from] YHWH is among them, And they have each seized the hand of his neighbor, And his hand has gone up against the hand of his neighbor.
14 Yahuda ma za tă yi yaƙi a Urushalima. Za a tattara dukiyar al’umman da suke kewaye, za a tara zinariya da azurfa masu yawan gaske tare da tufafi.
And also Judah is fought with in Jerusalem, And the force of all the surrounding nations has been gathered, Gold, and silver, and apparel, in great abundance.
15 Irin wannan bala’i zai auko wa dawakai da alfadarai, raƙuma da jakuna, da kuma dukan dabbobi a wannan sansani.
And so is the plague of the horse, of the mule, Of the camel, and of the donkey, And of all the livestock that are in these camps, As this plague.
16 Sa’an nan waɗanda suka tsira daga cikin al’umman da suka yaƙe Urushalima za su haura shekara-shekara su yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada, su kuma yi Bikin Tabanakul.
And it has come to pass, Everyone who has been left of all the nations, Who are coming in against Jerusalem, They have also gone up from year to year, To bow themselves to the King, YHWH of Hosts, And to celebrate the Celebration of the Shelters.
17 In waɗansu mutanen da suke duniya ba su haura Urushalima suka yi wa Sarki, Ubangiji Maɗaukaki sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba.
And it has come to pass, That he who does not go up of the families of the land to Jerusalem, To bow himself to the King, YHWH of Hosts, Even on them there is no shower.
18 In mutanen Masar ba su haura sun yi sujada ba, ba za su sami ruwan sama ba. Ubangiji zai kawo masu bala’in da ya aika wa al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
And if the family of Egypt does not go up, nor come in, Then on them is the plague With which YHWH plagues the nations That do not go up to celebrate the Celebration of Shelters.
19 Wannan ne zai zama hukuncin Masar da kuma na dukan al’umman da ba su haura sun yi Bikin Tabanakul ba.
This is the punishment of the sin of Egypt, And the punishment of the sin of all the nations, That do not go up to celebrate the Celebration of Shelters.
20 A ranan nan za a rubuta TSARKI GA Ubangiji a jikin ƙararrawar dawakai, kuma tukwanen dahuwa a gidan Ubangiji za su zama kamar kwanoni masu tsarki a gaban bagade.
In that day “Holy to YHWH” is [engraved] on bells of the horse, And the pots in the house of YHWH Have been as bowls before the altar.
21 Kowace tukunya a Urushalima da Yahuda za tă zama mai tsarki ga Ubangiji Maɗaukaki, kuma duk wanda ya zo don miƙa hadaya zai ɗauki waɗansu tukwane yă yi dahuwa da su. A ranan nan kuwa, ba Bakan’ane da zai ƙara kasance a gidan Ubangiji Maɗaukaki.
And every pot in Jerusalem and in Judah, Have been holy to YHWH of Hosts, And all those sacrificing have come in, And have taken of them, and boiled in them, And in that day there is no merchant anymore in the house of YHWH of Hosts!

< Zakariya 14 >