< Zakariya 13 >

1 “A ranan nan za a buɗe maɓulɓulan ruwa zuwa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima, don a tsarkake su daga zunubi da rashin tsabta.
“In that day there is a fountain opened To the house of David And to the inhabitants of Jerusalem, For sin and for impurity.
2 “A ranan nan, zan kawar da sunayen gumaka daga ƙasar, ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kawar da annabawa da kuma ruhu marar tsabta daga ƙasar.
And it has come to pass in that day,” A declaration of YHWH of Hosts, “I cut off the names of the idols from the land, And they are not remembered anymore, And also the prophets and the spirit of uncleanness I cause to pass away from the land.
3 In kuma wani ya yi annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa’ad da yake yin annabci, iyayensa za su soke shi da takobi.
And it has been, when one prophesies again, That his parents, his father and his mother, Have said to him, You do not live, For you have spoken falsehood in the Name of YHWH, And his father and his mother, his parents, Have pierced him through in his prophesying.
4 “A ranan nan kowane annabi zai ji kunyar annabcin wahayinsa. Ba zai sa rigar annabci mai gashi ba don yă yi ruɗu.
And it has come to pass in that day, The prophets are ashamed, each of his vision, in his prophesying, And they do not put on a hairy robe to deceive.
5 Zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne. Ni manomi ne; ƙasa ce nake samun abin zaman gari tun ina matashi.’
And [one] has said, I am not a prophet, A man—I am a tiller of ground, For ground [is] my possession from my youth.
6 In wani ya tambaye shi, ‘Waɗanne miyaku ne haka a jikinka?’ Zai amsa yă ce, ‘Miyakun da aka yi mini a gidan abokaina ne.’
And [one] has said to him, What [are] these wounds in your hands? And he has said, Because I was struck [at] home by my lovers.
7 “Tashi, ya takobi, gāba da makiyayina, mutumin da yake kusa da ni sosai!” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Kashe makiyayin, sai tumakin su watse, in kuma tayar wa ƙananan.
Sword, awake against My Shepherd, And against a hero—My Fellow,” A declaration of YHWH of Hosts. “Strike the Shepherd, and the flock is scattered, And I have put back My hand on the little ones.
8 A cikin ƙasar duka,” in ji Ubangiji, “kashi biyu bisa uku za a buge su su hallaka; duk da haka za a bar kashi ɗaya bisa uku a cikinta.
And it has come to pass, In all the land,” a declaration of YHWH, “Two parts in it are cut off—they expire, And the third is left in it.
9 Wannan kashi ɗaya bisa ukun zan kawo in sa a cikin wuta; zan tace su kamar azurfa in gwada su kamar zinariya. Za su kira bisa sunana zan kuwa amsa musu; zan ce, ‘Su mutanena ne,’ za su kuma ce, ‘Ubangiji ne Allahnmu.’”
And I have brought the third into fire, And refined them like a refining of silver, And have tried them like a trying of gold, It calls in My Name, and I answer it, I have said, It [is] My people, And it says, YHWH [is] my God!”

< Zakariya 13 >