< Zakariya 12 >

1 Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
Bildiri: İşte RAB'bin İsrail'e ilişkin sözleri. Gökleri geren, yeryüzünün temelini atan, insanın içindeki ruha biçim veren RAB şöyle diyor:
2 “Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
“Yeruşalim'i çevredeki bütün halkları sersemleten bir kâse yapacağım. Yeruşalim gibi Yahuda da kuşatma altına alınacak.
3 A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
O gün Yeruşalim'i bütün halklar için ağır bir taş yapacağım. Onu kaldırmaya yeltenen herkes ağır yaralanacak. Yeryüzünün bütün ulusları Yeruşalim'e karşı birleşecek.
4 A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
O gün her atı dehşete düşürecek, her atlıyı çılgına döndüreceğim. Yahuda halkını gözeteceğim, ama öbür halkların bütün atlarını kör edeceğim.
5 Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
O zaman Yahuda önderleri, ‘Her Şeye Egemen Tanrısı RAB'be güvenen Yeruşalim halkı güç kaynağımızdır’ diye düşünecekler.
6 “A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
“O gün Yahuda önderlerini odunların ortasında yanan bir mangal gibi, ekin demetleri arasında alev alev yanan bir meşale gibi yapacağım. Sağda solda, çevredeki bütün halkları yakıp yok edecekler. Yeruşalim ise sapasağlam yerinde duracak.
7 “Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
“Ben RAB önce çadırlarda oturan Yahuda halkını kurtaracağım. Öyle ki, Davut soyuyla Yeruşalim'de oturanlar Yahuda'dan daha çok onura kavuşmasın.
8 A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
Ben RAB o gün Yeruşalim'de oturanları koruyacağım. Böylece aralarındaki en güçsüz kişi Davut gibi, Davut soyu da Tanrı gibi, kendilerine öncülük eden RAB'bin meleği gibi olacak.
9 A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
O gün Yeruşalim'e saldıran bütün ulusları yok etmeye başlayacağım.
10 “Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
“Davut soyuyla Yeruşalim'de oturanların üzerine lütuf ve yakarış ruhunu dökeceğim. Bana, yani deştiklerine bakacaklar; biricik oğlu için yas tutan biri gibi yas tutacak, ilk oğlu için acı çeken biri gibi acı çekecekler.
11 A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
O gün Yeruşalim'de tutulan yas, Megiddo Ovası'nda, Hadat-Rimmon'da tutulan yas gibi büyük olacak.
12 Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
Ülkede her boy kendi içinde yas tutacak: Davut, Natan, Levi, Şimi boyundan ve geri kalan boylardan aileler. Her boyun erkekleri ayrı, kadınları ayrı yas tutacak.”
13 iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
14 dukan sauran iyalan kuma da matansu.

< Zakariya 12 >