< Zefaniya 3 >

1 Taki ta ƙare, ke birnin mai danniya, mai’yan tawaye da kuma masu ƙazanta!
Başkaldıran, yozlaşan, acımasız kentin vay haline!
2 Ba kya yi wa kowa biyayya, ba kya kuma yarda da kuskurenki. Ba kya dogara ga Ubangiji, ba kya kuma kusatowa kusa da Allahnki.
Söz dinlemedi, ders almadı, RAB'be güvenmedi, Tanrısı'na sığınmadı.
3 Sarakunanki ruri ne na zakoki, shugabanninki kyarketan dare ne, waɗanda ba sa rage kome don safe.
Yöneticileri kükreyen aslanlar, Önderleri akşam gezen aç kurtlar gibi, Sabaha bir şey bırakmazlar.
4 Annabawanki mahaukata ne mutanenki masu cin amana ne. Firistocinki suna ƙazantar da Wurin Mai Tsarki suna kuma keta dokoki.
Peygamberleri sorumsuz ve güvenilmezdir. Kâhinleri kutsal olanı kirletip, Yasayı çarpıtırlar.
5 Ubangiji da yake cikinki mai adalci ne; ba ya yin abin da ba daidai ba. Kowace safiya yakan bayyana dokokinsa a fili, kowace sabuwar rana kuma ba ya kāsawa, duk da haka marasa adalci ba sa jin kunya.
Ama adil RAB hâlâ o kentte; O haksızlık etmez, Aksatmadan dağıtır adaletini her yeni günün sabahında. Ne var ki, bu yetmiyor haksızları utandırmaya.
6 “Na daddatse al’ummai; an kuma rurrushe kagararsu. Na bar titunansu ba kowa, ba mai ratsawa a ciki. An ragargaza biranensu; ba wanda za a bari, babu ko ɗaya.
RAB diyor ki, “Ulusları yok ettim, Kalelerini yıktım, sokaklarını harap ettim. O sokaklardan geçen kimse yok artık. Kentleri viraneye döndü, Eser kalmadı insandan.
7 Na ce wa birnin, ‘Tabbatacce za ki ji tsorona ki kuma yarda da gyara!’ Ta haka ba za a datse wurin zamanki ba, ba kuwa dukan hukuncena za su hau bisa kansu ba. Amma har yanzu suna marmari su yi rashin gaskiya a duk abin da suke yi.
Halkım benden korkar, Ders alır bundan dedim. O zaman konutlarına dokunmaz, Onları tasarladığım cezaya çarptırmazdım. Ama her türlü kötülüğü yapmaya istekli görünüyorlar.”
8 Saboda haka ku jira ni,” in ji Ubangiji; “a ranar da zan tsaya in ba da shaida, Na yanke shawara in tattara dukan al’ummai, in tattara mulkoki in kuma zuba fushina a kansu, da dukan zafin haushina. Za a mamaye dukan duniya da zafin fushina.
Bu yüzden, “Bekleyin de görün” diyor RAB, “Ulusları yargılayacağım günü bekleyin. Ulusları toplamaya, Krallıkları bir araya getirmeye, Gazabımı, kızgın öfkemi Üzerlerine dökmeye karar verdim. Çünkü kıskançlığımın ateşi bütün dünyayı yiyip bitirecek.
9 “Sa’an nan zan tsarkake leɓunan mutanen, don dukansu su kira bisa ga sunan Ubangiji su kuma yi masa hidima kafaɗa da kafaɗa.
O zaman, hep birlikte beni adımla çağırmaları, Omuz omuza bana hizmet etmeleri için, Halkların dudaklarını pak kılacağım.
10 Tun daga ƙetaren rafuffukan Kush masu yi mini sujada, mutanena da suke a warwatse, za su kawo mini hadayu.
Dağılmış olan, bana tapan halkım, Kûş ırmaklarının ötesinden Bana sunular getirecek.
11 A wannan rana ba za ku sha kunya saboda laifofin da kuka yi mini, gama zan ɗauke wa wannan birni waɗanda suke farin ciki cikin girmankansu. Ba kuma za ka ƙara yin kallon reni a tuduna mai tsarki ba.
Halkım bana yaptığı bunca kötülük yüzünden utandırılmayacak o gün. Çünkü gururlu, küstah olanları uzaklaştıracağım aralarından. Kutsal dağımda bir daha böbürlenmeyecekler.
12 Amma zan zauna a cikinki masu tawali’u da masu ƙasƙantar da kai, waɗanda suke dogara ga sunan Ubangiji.
Orada sadece benim adıma sığınan uysal ve alçakgönüllüleri bırakacağım.
13 Raguwar Isra’ila ba za su ƙara aikata abin da ba daidai ba, ba za su faɗa ƙarya ba, ba kuwa za a sami ruɗu a bakunansu ba. Za su ci su kuma kwanta kuma babu wanda zai ba su tsoro.”
İsrailliler'den geride kalanlar haksızlık etmeyecek, Yalan söylemeyecek, Kimseyi aldatmayacak, Tok karna yatacaklar ve onları korkutan olmayacak.”
14 Ki rera, ya Diyar Sihiyona; ki tā da murya, ya Isra’ila! Ki yi murna ki kuma yi farin ciki da dukan zuciyarki, Ya Diyar Urushalima!
Ey Siyon kızı, ezgiler söyle! Ey İsrail, haykır! Yürekten sevin, sevinçle coş, Ey Yeruşalim kızı!
15 Ubangiji ya ɗauke hukuncinki, ya mai da abokan gābanki baya. Ubangiji, Sarkin Isra’ila, yana tare da ke; ba kuma za ki ƙara jin tsoron wani lahani ba.
RAB senin cezanı kaldırdı, Kovdu düşmanlarını. İsrail'in Kralı RAB seninle. Korkma artık kötülükten.
16 A wannan rana za su cewa Urushalima, “Kada ki ji tsoro, ya Sihiyona; kada ki bar hannuwanki su raunana.
O gün Yeruşalim'e denecek ki, “Korkma, ey Siyon, gevşemesin ellerin.
17 Ubangiji Allahnki yana tare da ke, mai iko ne don ceto. Zai yi matuƙar farin ciki da ke, zai rufe ki da ƙaunarsa, zai yi farin ciki da ke ta wurin rerawa.”
Tanrın RAB, o güçlü Kurtarıcı seninle. Alabildiğine sevinecek senin için, Sevgisiyle seni yenileyecek, ezgilerle coşacak.”
18 “Zan cire taƙaici daga gare ki a ƙayyadaddun bukukkuwa; su kaya ne da kuma zargi a gare ki.
RAB, “Bayramlar için çektiğiniz özlemleri sona erdireceğim” diyor, “Bunlar sizin için ağırlık ve utançtır. Sizi ezenlerin tümünü cezalandıracağım o gün. Düşkünleri kurtaracak, sürgünleri toplayacağım. Utanç içinde kaldıkları bütün ülkelerde Onları yüceltip onurlandıracağım. O zaman sizi toplayıp yurdunuza geri getireceğim. Göreceksiniz, sizi yeniden bayındır kılacak, Dünyanın bütün halkları arasında yüceltip onurlandıracağım.”
19 A wannan lokaci zan jijji wa waɗanda suka danne ku; zan kuɓutar da guragu in kuma tattara waɗanda suke a warwatse. Zan sa a yabe su a kuma girmama su a kowace ƙasar da aka kunyatar da su.
20 A wannan lokaci zan tattara ku; a wannan lokaci zan kawo ku gida, zan sa a yabe ku a kuma girmama ku a cikin dukan mutanen duniya a sa’ad da na maido da arzikinku a idanunku,” in ji Ubangiji.

< Zefaniya 3 >