< Waƙar Waƙoƙi 2 >

1 Ni furen bi-rana ne na Sharon, furen bi-rana na kwari.
Ngililuba laseSharoni, imbali yasezigodini.
2 Kamar furen bi-rana a cikin ƙayayyuwa haka ƙaunatacciyata take a cikin’yan mata.
Njengembali phakathi kwameva sinjalo isithandwa sami phakathi kwezintombi.
3 Kamar itacen gawasa a cikin itatuwan jeji haka ƙaunataccena yake a cikin samari. Ina farin ciki in zauna a inuwarsa,’ya’yan itacensa suna da daɗin ɗanɗanon da nake so
Njengesihlahla se-aphula phakathi kwezihlahla zeganga sinjalo isithandwa sami phakathi kwamajaha. Kumnandi kimi ukuhlala emthunzini waso, lezithelo zakhe ziyahlabusa kimi.
4 Ya kai ni babban zauren da ake liyafa, ƙauna ita ce tutarsa a gare ni.
Useke wangisa endlini yedili, lophawu lwakhe kimi luthando.
5 Ka ƙarfafa ni da zabibi ka wartsake ni da gawasa, gama ina suma don ƙauna.
Ngiqinisani ngamavini awonyisiweyo, lingivuselele ngama-aphula, ngoba sengiyathiswa luthando.
6 Hannunsa na hagu yana a ƙarƙashin kaina, hannunsa na dama kuma ya rungume ni.
Ingalo yakhe yobunxele ngiyiqamele, kuthi ingalo yakhe yokunene ingigonile.
7 ’Yan matan Urushalima, ku yi mini alkawari da bareyi da ƙishimai na jeji. Ba za ku tā da ko ku farka ƙauna ba sai haka ya zama lalle.
Madodakazi aseJerusalema, ngiyaliqonqosela ngezimpala langezimpalakazi zeganga. Lingalunyakazisi loba liluvuse uthando luze luzifunele lona.
8 Saurara! Ƙaunataccena! Duba! Ga shi ya iso, yana tsalle a duwatsu, yana rawa a bisa tuddai.
Zwanini! Yisithandwa sami! Khangelani! Nansi siyeza, siseqa ezintabeni siqolotsha emaqaqeni.
9 Ƙaunataccena yana kama da barewa ko sagarin ƙishimi Duba! Ga shi can tsaye a bayan katangarmu, yana leƙe ta tagogi, yana kallo ta cikin asabari.
Isithandwa sami sinjengempala loba ithole lomziki. Khangela! Nansiyana simi ngale komduli wakwethu, sikhangele sibona emawindini, silunguza ngezimbotshana.
10 Ƙaunataccena ya yi magana ya ce mini, “Tashi, ƙaunatacciyata, kyakkyawata, ki zo tare da ni.
Isithandwa sami sakhuluma sathi kimi, “Sukuma, sithandwa sami, wena omuhle, woza sihambe.
11 Duba! Damina ta wuce; ruwan sama ya ɗauke ya kuma ƙare.
Khangela! Ubusika sebudlulile; isikhathi sezulu sesidlule.
12 Furanni sun hudo a duniya; lokaci yin waƙa ya zo, ana jin kukan kurciyoyi ko’ina a ƙasarmu.
Amaluba asebonakala emangweni; isikhathi sokuhlabelela kwezinyoni sesifikile, ukukhala kwamajuba sekuzwakala elizweni lakithi.
13 Itacen ɓaure ya fid da’ya’yansa da sauri; tohon inabi suna ba da ƙanshinsu. Tashi, zo, ƙaunatacciyata; kyakkyawata, zo tare da ni.”
Umkhiwa usuthela izithelo zawo zakuqala; amavini aqhakazayo aseletha iphunga elimnandi. Sukuma, woza sithandwa sami; wena omuhle wami, woza sihambe.”
14 Kurciyata a kogon dutse, a wuraren ɓuya a gefen dutse, nuna mini fuskarki, bari in ji muryarki; gama muryarki da daɗi take, fuskarki kuma kyakkyawa ce.
Juba lami elisezingoxweni zedwala, ekusithekeni kwamawa entaba, akungitshengise ubuso bakho, akungizwise ilizwi lakho; ngoba limnandi ilizwi lakho, lobuso bakho buyabukeka.
15 Kama mana ɓeraye, ƙananan ɓerayen da suke lalatar da gonakin inabi, gonakin inabinmu da suke cikin yin fure.
Sibambeleni amakhanka, amakhanka amancinyane onayo ezivinini, izivini zethu esezithela.
16 Ƙaunataccena nawa ne ni kuma tasa ce; yana kiwon garkensa a cikin furannin bi-rana.
Isithandwa sami ngesami lami ngingowakhe; uzithokozisa ngoba phakathi kwamaluba.
17 Sai gari ya waye inuwa kuma ta watse, ka juye, ƙaunataccena, ka zama kamar barewa ko kamar sagarin ƙishimi a kan tuddai masu ciyawa.
Akuze kube emadabukakusa lapho kunyamalala khona izithunzi, phenduka sithandwa sami, ube njengempala loba njengegogo elisengumntwana phezu kwezintaba ezilamakhelekethe.

< Waƙar Waƙoƙi 2 >