< Waƙar Waƙoƙi 1 >
Ingoma yezingoma kaSolomoni.
2 Bari yă sumbace ni da sumbar bakinsa, gama ƙaunarka ta fi ruwan inabi zaƙi.
Kangange ngezangiwo zomlomo wakhe ngoba uthando lwakho lumnandi kulewayini.
3 Ƙanshin turarenka mai daɗi ne; sunanka kuwa kamar turaren da aka tsiyaye ne. Shi ya sa mata suke ƙaunarka!
Limnandi iphunga lamagcobo akho; ibizo lakho linjengamakha atheliweyo. Yikho izintombi zikuthanda kangaka!
4 Ka ɗauke ni mu gudu, mu yi sauri! Bari sarki yă kai ni gidansa. Ƙawaye Muna farin ciki muna kuma murna tare da kai, za mu yabi ƙaunarka fiye da ruwan inabi. Ƙaunatacciya Daidai ne su girmama ka!
Ngithatha uhambe lami, kasiphangise! Inkosi kayingingenise endlini yayo. Abangane Siyathokoza njalo siyajabula ngawe; sizalubabaza uthando lwakho okudlula iwayini. Umlobokazi Kabazenzi ukuba bakuthande!
5 Ni baƙa ce, duk da haka kyakkyawa. Ya ku’yan matan Urushalima, ni baƙa ce kamar tentunan Kedar, kamar labulen tentin Solomon.
Ngimnyama kodwa ngiyabukeka, lina madodakazi aseJerusalema ngimnyama okwamathente aseKhedari, okwamakhetheni amathente kaSolomoni.
6 Kada ku harare ni domin ni baƙa ce, gama rana ta dafa ni na yi baƙa.’Ya’yan mahaifiyata maza sun yi fushi da ni suka sa ni aiki a gonakin inabi; na ƙyale gonar inabi na kaina.
Linganginyonkolozi ngoba ngimnyama, ngimnyama ngenxa yokutshiswa lilanga. Abanewethu bangizondela bangenza umlindi wesivini; angabe ngisanaka esami isivini.
7 Faɗa mini, kai da nake ƙauna, ina kake kiwon garkenka kuma ina kake kai tumakinka su huta da tsakar rana. Me ya sa zan kasance kamar macen da aka lulluɓe kusa da garkunan abokanka?
Akungitshele, wena engikuthandayo, uyelusela ngaphi imihlambi yezimvu zakho lokuthi ziphumula ngaphi izimvu zakho emini? Kungani ngisiba njengomfazi ombozileyo eceleni kwemihlambi yabangane bakho na?
8 Ke mafiya kyau a cikin mata, in ba ki sani ba, to, ki dai bi labin da tumaki suke bi ki yi kiwon’yan awakinki kusa da tentunan makiyaya.
Nxa ungazi, wena omuhle okudlula bonke abesifazane, landela umkhondo wezimvu udlisele amazinyane embuzi zakho eduze lamathente abelusi.
9 Ina kwatanta ke ƙaunatacciyata, da goɗiya mai jan keken yaƙin kayan Fir’auna.
Sithandwa sami, ngikufanisa lebhiza elisikazi elibotshwe enqoleni kaFaro.
10 ’Yan kunne sun ƙara wa kumatunki kyau, wuyanki yana da jerin kayan wuya masu daraja.
Izihlathi zakho zinhle ngokuceciswa, intamo yakho ngobuhlalu obucazimulayo.
11 Za mu yi’yan kunnenki na zinariya, da adon azurfa.
Sizakwenzela amacici egolide, ebalazwe ngesiliva.
12 Yayinda sarki yake a teburinsa, turarena ya bazu da ƙanshi.
Khonapho inkosi isetafuleni amakha ami enadi alanquza iphunga lawo elimnandi.
13 Ƙaunataccena yana kamar ƙanshin mur a gare ni, kwance a tsakanin ƙirjina.
Kimi isithandwa sami sinjengemfuko yemure ithe khoxo phakathi kwamabele ami.
14 Ƙaunataccena kamar tarin furanni jeji ne gare ni daga gonakin inabin En Gedi.
Kimi isithandwa sami sinjengelixha lempoko zehena eliphuma esivinini se-Eni-Gedi.
15 Ke kyakkyawa ce, ƙaunatacciyata! Kai, ke kyakkyawa ce! Idanunki kamar na kurciya ne.
Bakithi, umuhle njani sithandwa sami! Ngeqiniso umuhle! Amehlo akho angamajuba.
16 Kai kyakkyawa ne, ƙaunataccena! Kai, kana ɗaukan hankali! Gadonmu koriyar ciyawa ce.
Umuhle ngempela, sithandwa sami! Bakithi, uyabukeka! Umbheda wethu butshani obuluhlaza tshoko.
17 Al’ul su ne ginshiƙan gidanmu; fir su ne katakan rufin gidanmu.
Izinsika zendlu yethu ngezomsedari lezintungo ngezefire.