< Rut 4 >
1 Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
И Вооз прииде ко вратом и седе тамо: и се, ужик мимоидяше, о немже глагола Вооз. И рече ему Вооз: уклонився сяди зде. Он же уклонися и седе.
2 Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
И поя Вооз десять мужей от старейшин града, и рече: сядите зде. И седоша.
3 Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
И рече Вооз ужику: часть села, яже есть брата нашего Елимелеха, яже дадеся Ноеммине возвратившейся от села Моавля:
4 Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
аз же рекох: явлю тебе сие во ухо твое, глаголя, пристяжи пред седящими и пред старейшины людий моих: и аще ужичествуеши, ужичествуй: аще же не ужичествуеши, повеждь ми, да ведаю: яко несть разве тебе еже ужичествовати ближший, и аз есмь по тебе. Он же рече: аз есмь, ужичествую.
5 Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
И рече Вооз: в день в оньже пристяжеши село от руки Ноеммини, и от Руфы Моавитяныни жены умершаго, и сию достоит ти пояти, да возставиши имя умершаго в наследие его.
6 Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
И рече ужик: не возмогу ужичествовати себе, да не разсыплю наследия моего: ужичествуй себе ты ужичество мое, аз бо не возмогу ужичествовати.
7 (To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
И сие управление бысть прежде во Израили о ужичествовании и о пременении, еже укрепити всякое слово: и иззуваше муж сапог свой, и даяше подругу своему ужичествующу ужичество его: и сие бяше свидетелство во Израили.
8 Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
И рече ужик Воозу: пристяжи себе ужичество мое. И иззув сапог свой, даде ему.
9 Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
И рече Вооз старейшинам и всем людем: свидетеле вы днесь, яко пристяжах днесь вся, яже Елимелехова, и вся елика суть Хелеонова и Маалонова, от руки Ноеммини:
10 Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
ксему же Руфь Моавитяныню жену Маалоню поемлю себе в жену возставити имя умершаго в наследие его, да не погибнет имя умершаго от братии его и от племене людий его: свидетеле вы днесь.
11 Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
И отвещаша вси людие иже у врат: свидетеле есмы. И старейшины реша: да даст Господь жене твоей, входящей в дом твой, якоже Рахили и яко Лии, яже создаша обе дом Израилев, и сотвориша силу во Ефрафе, и будет имя в Вифлееме:
12 Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
и буди дом твой якоже дом Фаресов, егоже роди Фамарь Иуде, от семене твоего даст тебе Господь от рабы сея чада.
13 Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
И поя Вооз Руфь, и бысть ему жена, и вниде к ней: и даде ей Господь зачати, и роди сына.
14 Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
И рекоша жены к Ноеммине: благословен Господь, Иже не разсыпа ужика твоего днесь, и прозовется имя твое во Израили,
15 Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
и будет тебе во обращающаго душу и в прекормление старости твоея, яко сноха твоя, возлюбившая тебе, роди сына, яже есть блага тебе паче седми сынов.
16 Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
И взя Ноемминь отроча, и положи е на лоне своем, и бысть ему кормилица.
17 Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
И прозваша соседи имя его, глаголюще: родися сын Ноеммине. И нарекоша имя ему Овид: сей есть отец Иессеа, отца Давидова.
18 Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
И сия родства Фаресова: Фарес роди Есрома:
19 Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
Есром же роди Арама: Арам же роди Аминадава:
20 Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
Аминадав же роди Наассона: Наассон же роди Салмона:
21 Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
Салмон же роди Вооза: Вооз же роди Овида:
22 Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.
Овид же роди Иессеа: Иессей же роди Давида.