< Mahukunta 1 >

1 Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
И бысть по скончании Иисусове, и вопрошаху сынове Израилевы Господа, глаголюще: кто взыдет нам к Хананею воевода, ратовати на них?
2 Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
И рече Господь: Иуда взыдет: се, дах землю в руку его.
3 Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
И рече Иуда к Симеону брату своему: взыди со мною в жребий мой, и ополчимся на Хананеа: и пойду и аз с тобою в жребий твой. И пойде с ним Симеон.
4 Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
И взыде Иуда, и предаде Господь Хананеа и Ферезеа в руце их: и избиша их в Везеце до десяти тысящ мужей.
5 A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
И обретоша Адонивезека в Везеце, и секошася с ним: и избиша Хананеа и Ферезеа.
6 Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
И побеже Адонивезек: и гнаша вслед его, и яша его, и отсекоша краи рук его и краи ног его.
7 Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
И рече Адонивезек: седмидесяти царем обсекох краи рук их и краи ног их, и быша собирающе (от крупиц) под трапезою моею: якоже убо сотворих, тако воздаде ми Бог. И приведоша его во Иерусалим, и умре тамо.
8 Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
И воеваша сынове Иудины на Иерусалим, и взяша его, и поразиша его острием меча, и град сожгоша огнем.
9 Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
И по сих снидоша сынове Иудины воевати на Хананеа живущаго в горней к югу и в равней.
10 Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
И пойде Иуда на Хананеа живущаго в Хевроне. И изыде Хеврон со страны: имя же бе Хеврону прежде Кариафарвок-Сефер: и убиша Сесина и Ахимана и Фолмиа, роды Енаковы.
11 Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
И взыдоша оттуду к живущым в Давире: имя же Давиру бе прежде Кариафсефер, Град Писмен.
12 Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
И рече Халев: иже аще поразит Град Писмен и возмет его, дам ему Асхань дщерь мою в жену.
13 Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
И взя его Гофониил сын Кенеза брата Халевова юнейший, и даде ему Халев Асхань дщерь свою в жену.
14 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
И бысть внегда отходити ей, и подвиже ю Гофониил просити у отца своего села, и ропташе (седящи) на осляти, и вопияше со осляти: на землю южную отдал мя еси. И рече ей Халев: что ти есть?
15 Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
И рече ему Асхань: даждь ми благословение: яко на землю южную отдал еси мя, да даси мне и исходища водная. И даде ей Халев по сердцу ея исходища вышних и исходища нижних.
16 Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
И сынове Иофора Кинеева, ужика Моисеова, взыдоша от града Финическа к сыном Иудиным в пустыню сущую на юг Иуды ко исходу Аредову, и поидоша, и вселишася с людьми.
17 Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
И пойде Иуда с Симеоном братом своим, и изби Хананеа живущаго в Сефефе, и потребиша его: и прозваша имя граду Потребление.
18 Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
И взя Иуда Газу и предел ея, и Аскалона и предел его, и Аккарон и предел его, и Азот и окрестная его.
19 Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
И бяше Господь со Иудою. И взя гору, яко не возмогоша потребити живущих во юдоли, зане Рихав противоста им, и колесницы железныя бяху там.
20 Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
И даша Халеву Хеврон, якоже глагола Моисей: и наследствова тамо три грады сынов Енаковых, и изгна оттуду три сыны Енаковы.
21 Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
И Иевусеа живущаго во Иерусалиме не изгнаша сынове Вениаминовы, и живяше Иевусей с сынми Вениамини во Иерусалиме даже до сего дне.
22 To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
И взыдоша сынове Иосифли и сии в Вефиль: и Господь бяше с ними.
23 Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
И ополчишася, и соглядаша (сынове Иосифовы) Вефиль: имя же бе прежде граду Луза.
24 ’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
И видеша стрегущии мужа исходящаго из града, и яша его и рекоша ему: покажи нам вход во град, и сотворим с тобою милость.
25 Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
И показа им вход градный: и поразиша град острием меча, мужа же и сродство его отпустиша.
26 Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
И отиде муж в землю Хеттиим, и созда тамо град, и прозва имя ему Луза: сие имя ему даже до дне сего.
27 Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
И не разори Манассий Вефсана, иже есть Скифский град, ниже дщерей его, ниже окрестных (предел) его, ниже Фанаха, ниже дщерей его, ниже живущих в Доре, ниже дщерей его, ниже живущих во Иевламе, ниже окрестных его, ниже дщерей его, и живущих в Магеддоне, ниже окрестных его и дщерей его. И нача Хананей жити на земли сей.
28 Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
И бысть егда укрепися Израиль, и сотвори Хананеа данника: изгнанием же не изгна его.
29 Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
И Ефрем не изгна Хананеа живущаго в Газере: и живяше Хананей среде его в Газере, и бысть ему в данника.
30 Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
И Завулон не изгна живущих в Хевроне и живущих во Аммане: и вселися Хананей посреде их и бысть ему данник.
31 Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
И Асир не изгна живущих во Акхоре, (и бысть ему данник, ) ни живущих в Доре, ни живущих в Сидоне, ни живущих в Далафе и во Ахазиве, и во Елве и во Афеке и в Роове.
32 kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
И вселися Асир посреде Хананеа живущаго на земли (той), зане не возможе изгнати его.
33 Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
И Неффалим не изгна живущих в Вефсамисе, ниже живущих в Вефанахе: и вселися Неффалим среде Хананеа живущаго на земли (сей): живущии же в Вефсамисе и в Вефанахе быша ему данницы.
34 Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
И утесни Аморрей сыны Дановы в горе, яко не попусти им низходити во юдоль.
35 Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
И нача Аморрей жити в горе Чрепней, идеже медведи и лисицы, в Мирсиноне и в Салавине: и отяготе рука дому Иосифля на Аморреа, и бысть ему данник.
36 Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.
И предел Аморрейский идумей от восхода Акравиня, от Камене и выше.

< Mahukunta 1 >