< Rut 2 >

1 To, fa, Na’omi tana da dangi a gefen mijinta da iyalin Elimelek, mutum mai martaba, mai suna Bowaz.
Now, Naomi, had an acquaintance of her husband’s, a man of great integrity, of the family of Elimelech, —whose name, was Boaz.
2 Sai Rut mutuniyar Mowab ta ce wa Na’omi, “Bari in tafi gonaki in yi kala raguwar hatsi a bayan duk wanda na sami tagomashi daga gare shi.” Na’omi ta ce mata, “Ki je,’yata.”
And Ruth the Moabitess said unto Naomi—Let me go, I pray thee, to the field, and glean ears of corn after him in whose eyes I may find favour. And she said to her—Go, my daughter.
3 Saboda haka ta tafi ta fara kala a gonaki a bayan masu girbi. Sai ya zamana, ta sami kanta tana aiki a gonar da take ta Bowaz, wanda yake daga dangin Elimelek.
So she went her way, and came, and gleaned in the field, after the reapers, —and it happened to her, to light upon the portion of field-land belonging to Boaz, who was of the family of Elimelech.
4 Sai ga Bowaz ya iso daga Betlehem ya gai da masu girbi, “Ubangiji yă kasance tare da ku!” Sai suka amsa, “Ubangiji yă albarkace ka!”
And lo! Boaz coming from Bethlehem, and he said to the reapers, Yahweh, be with you! and they said to him, Yahweh bless thee!
5 Sai Bowaz ya tambayi shugaban masu girbinsa, “Wace yarinya ce wannan?”
Then said Boaz to his young man, that was set over the reapers, —Whose is this maiden?
6 Shugaban ya amsa, “Ita ce mutuniyar Mowab da ta zo daga Mowab tare da Na’omi.
And the young man that was set over the reapers answered and said, —The Moabitish maiden, is she who came back with Naomi, out of the country of Moab;
7 Ta ce, ‘Ina roƙo a bar ni in bi bayan masu girbin in yi kala.’ Haka ta shiga cikin gonar ta kuwa yi aiki tun da safe har zuwa yanzu, sai ɗan hutun da ta yi kaɗan.”
and she said—Let me glean, I pray thee, and gather among the sheaves, after the reapers; so she came in, and hath continued from that time, all the morning until just now, and hath not rested in the house, for a little.
8 Saboda haka Bowaz ya ce wa Rut, “’Yata, ki saurare ni. Kada ki tafi ki yi kala a wani gona, kada kuma ki tafi daga nan. Ki tsaya nan tare da’yan matana bayi.
And Boaz said unto Ruth—Hearest thou not, my daughter? Do not go to glean in any other field, neither indeed shalt thou pass on, from hence, —but, here, shalt thou keep fast by my maidens:
9 Ki lura da gonar da mutanena suke girbi, ki bi su tare da’yan matana. Na riga na faɗa wa mazan kada su taɓa ke. Kuma duk sa’ad da kika ji ƙishirwa, ki tafi ki ɗebo ruwa daga tulunan da mazan suka cika.”
thine eyes, be on the field which they shall reap, and go thou after them, Have I not commanded the young men, that they touch thee not? And, when thou art athirst, then go unto the vessels, and drink of what the young men shall draw.
10 Jin haka, sai ta rusuna da fuskata har ƙasa ta ce, “Me ya sa na sami irin wannan tagomashi a idanunka da har ka lura da ni, ni da nake baƙuwa?”
Then she fell upon her face, and bowed herself to the ground, —and said unto him—Wherefore have I found favour in thine eyes, that thou shouldest take notice of me, seeing that, I, am, a stranger?
11 Bowaz ya amsa, “An faɗa mini duka game da abin kika yi domin surukarki tun mutuwar mijinki, yadda kika bar mahaifinki da mahaifiyarki da kuma ƙasarki kika zo ki yi zama da mutanen da ba ki taɓa sani ba.
And Boaz answered, and said to her, It hath been, told, me—all that thou hast done unto thy mother-in-law, since the death of thy husband, —and how thou hast left thy father and thy mother, and the land of thy nativity, and come unto a people whom thou knewest not, aforetime.
12 Bari Ubangiji yă sāka maka saboda abin da ka yi. Bari Ubangiji, Allah na Isra’ila yă sāka maka a yalwace, a ƙarƙashin fikafikan da ka sami mafaka.”
Yahweh recompense thy deed, —and let thy reward be full from Yahweh, the God of Israel, unto whom thou hast come to take refuge under his wings.
13 Ta ce, “Bari in ci gaba da samun tagomashi a idanunka ranka yă daɗe. Ka ta’azantar da ni ka kuma yi wa baranyarka magana mai alheri ko da yake ban kai matsayi ɗaya daga cikin bayinka’yan mata ba.”
And she said—Let me find favour in thine eyes, my lord, for that thou hast comforted me, and for that thou hast spoken unto the heart of thy handmaid, —though, I, be not as, one of thine own handmaidens.
14 A lokacin cin abinci Bowaz ya ce mata, “Zo nan. Ki ɗebo burodi ki tsoma cikin ruwan inabi.” Da ta zauna tare da masu girbin, sai ya ba ta gasasshe hatsi. Ta ci duk abin da take so har ta bar ragowa.
And Boaz said to her at mealtime—Draw nigh hither, and eat of the bread, and dip thy morsel in the vinegar. So she sat beside the reapers, and there was reached to her parched corn, and she did eat and was satisfied, and left thereof remaining.
15 Da ta tashi don tă yi kala, sai Bowaz ya yi umarni wa samarinsa cewa, “Ko ta tara daga cikin dammuna, kada ku wulaƙanta ta.
And, when she rose up to glean, Boaz commanded his young men, saying—Even between the sheaves, let her glean, and reproach her not;
16 Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.”
yea moreover, draw out, for her, from the bundles, —and leave behind that she may glean it, and rebuke her not.
17 Saboda haka Rut ta yi kala a gonar har yamma. Sa’an nan ta sussuka hatsin sha’ir da ta kalata ta sami kamar efa.
So she gleaned in the field, until the evening, —and beat out that which she had gleaned, and there was about an ephah of barley.
18 Ta ɗauka ta koma gari sai surukarta ta ga yawan abin da ta kalato. Rut kuma ta fitar da ragowar abin da ta ci bayan ta ƙoshi ta ba ta.
And she took it up, and came into the city, and, when her mother-in-law had seen what she had gleaned, she brought forth and gave her what had been left remaining, after that she was satisfied.
19 Surukarta ta tambaye ta, “Ina kika yi kala a yau? Ina kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga mutumin nan ta ya lura da ke!” Sai Rut ta faɗa wa surukarta game da wurin wanda ta yi ta aiki. Ta ce, “Sunan mutumin da na yi aiki da shi a yau Bowaz ne.”
And her mother-in-law said to her—In what place hast thou gleaned, today? and where hast thou wrought? May he that took notice of thee, be blessed! So she told her mother-in-law, with whom she had wrought, and said—The name of the man with whom I wrought today, is Boaz.
20 Sai Na’omi ta ce wa surukarta, “Ubangiji yă yi masa albarka! Bai daina nuna alheri ga masu rai da matattu ba.” Ta ƙara da cewa, “Wannan mutum danginmu ne na kusa; shi ɗaya daga cikin danginmu mai fansa.”
Then said Naomi, to her daughter-in-law—Blessed, be he of Yahweh, who hath not left off his lovingkindness to the living, and to the dead. And Naomi said to her—Near to us, is the man, of our own kinsmen, is he!
21 Sa’an nan Rut mutuniyar Mowab ta ce, “Ya ma ce mini, ‘Ki riƙa bin ma’aikatana sai sun ƙare yin girbin dukan hatsina.’”
And Ruth the Moabitess said, —Yea for he said unto me—By my young men, shalt thou keep fast, until they have ended all my harvest.
22 Na’omi ta ce wa Rut surukarta, “Zai fi miki kyau,’yata ki riƙa tafiya da’yan matansa, domin a gonar wani dabam mai yiwuwa a yi miki lahani.”
And Naomi said unto Ruth her daughter-in-law, —Good, is it, my daughter, that thou go forth with his maidens, and that they meet thee not, in any other field.
23 Saboda haka Rut ta tsaya kusa da bayi mata na Bowaz don tă yi kala sai da girbin sha’ir da na alkama suka ƙare. Ta kuwa zauna tare da surukarta.
So she kept fast by the maidens of Boaz, to glean, until the end of the barley harvest, and the wheat harvest, —and dwelt with her mother-in-law.

< Rut 2 >