< Rut 1 >

1 A kwanakin da mahukunta suke mulki an yi yunwa a ƙasar, sai wani mutum daga Betlehem a Yahuda tare da matarsa da’ya’yansu maza biyu, suka tafi su yi zama na ɗan lokaci a ƙasar Mowab.
And it came to pass, in the days when the Judges administered justice, that there was a famine in the land, —and so a certain man went his way, out of Bethlehem-judah to sojourn in the country of Moab, he, and his wife, and his two sons.
2 Sunan mutumin, Elimelek ne, sunan matarsa Na’omi; sunayen’ya’yan nan nasu biyu, su ne Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Betlehem ta Yahuda. Suka kuwa tafi Mowab suka zauna a can.
And, the name of the man, was Elimelech, and, the name of his wife, Naomi, and, the name of his two sons, Mahlon and Chilion—Ephrathites out of Bethlehem-judah, —so they came into the country of Moab, and remained there.
3 To, Elimelek mijin Na’omi ya rasu, aka bar ta da’ya’yanta maza biyu.
And Elimelech, husband of Naomi, died, —and she was left, she and her two sons.
4 Suka auri mata Mowabawa, sunan ɗaya Orfa ɗayan kuma Rut. Bayan sun zauna a can kamar shekara goma,
And they took them wives, of the women of Moab, the name of the one, was Orpah, and, the name of the other, Ruth, —and they dwelt there, about ten years.
5 sai Malon da Kiliyon suka mutu su ma, aka kuma bar Na’omi babu’ya’yanta maza biyu da kuma mijinta.
And, they also, both, died, Mahlon and Chilion, —so the woman was bereft of her two sons, and of her husband.
6 Sa’ad da ta ji a Mowab cewa Ubangiji ya zo don yă taimaki mutanensa ta wurin tanada musu da abinci, sai Na’omi tare da surukanta suka shirya su koma gida daga can.
Then she arose, she and her daughters-in-law, and returned out of the country of Moab, —for she had heard, in the country of Moab, how that Yahweh had visited his people, in giving unto them, bread.
7 Tare da surukanta biyu suka bar inda suka zauna suka kuma kama hanya da za tă komar da su zuwa ƙasar Yahuda.
So she went forth out of the dwelling-place where she had remained, and her two daughters-in-law with her, —and they went on the way, to return unto the land of Judah.
8 Sai Na’omi ta ce wa surukanta biyu, “Ku koma, kowannenku, zuwa gidan mahaifiyarta. Bari Ubangiji yă nuna muku alheri yadda kuka nuna wa matattun nan da kuma gare ni.
Then said Naomi to her two daughters-in-law: Go return, each one to the house of her mother, —Yahweh deal with you in lovingkindness, as ye have dealt with the dead, and with me.
9 Bari Ubangiji yă sa kowannenku ta sami hutu a gidan wani miji.” Sa’an nan ta sumbace su suka kuma yi kuka da ƙarfi
Yahweh grant you, that ye may find a place of rest, each one in the house of her husband, —And she kissed them, and they lifted up their voice, and wept.
10 suka ce mata, “Za mu tafi tare da ke zuwa ga mutanenki.”
And they said to her, —With thee, will we return, unto thy people.
11 Amma Na’omi ta ce, “Ku koma gida,’ya’yana mata. Don me za ku tafi tare da ni? Zan ƙara samun waɗansu’ya’ya maza da za su zama mazanku ne?
Then said Naomi—Go back, my daughters! wherefore should ye journey with me? Have I, yet, sons in my womb, that they should become your, husbands?
12 Ku koma gida’ya’yana mata; na tsufa ainun da zan sāke samun wani miji. Ko ma na yi tsammani har yanzu ina da bege, ko ma na sami miji a wannan dare na kuma haifi’ya’ya maza,
Go back, my daughters, go your way, for I am too old to have a husband, —If I should say, I have, hope, if I should, even to-night have a husband, and should, even bear sons,
13 za ku jira sai sun yi girma? Za ku ci gaba da kasance babu aure saboda su? A’a,’ya’yana mata. Ina da baƙin ciki ƙwarai fiye da ku, domin hannun Ubangiji ya yi gāba da ni!”
would ye, therefore, tarry until they were grown? would ye, therefore, shut yourselves up from having husbands? Nay! my daughters, for it is far more bitter for me than for you, that forth hath gone against me, the hand of Yahweh.
14 A kan wannan suka sāke ɓarke da kuka. Sa’an nan Orfa ta sumbaci surukarta ta yi bankwana, amma Rut ta manne mata.
And they lifted up their voice and wept, yet more. Then Orpah kissed her mother-in- law, but, Ruth, clave unto her.
15 Sai Na’omi ta ce, “Duba,’yar’uwanki ta koma zuwa ga mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da ita.”
And she said—Lo! thy sister-in-law hath gone back, unto her people, and unto her gods, —go thou back, after thy sister-in-law.
16 Rut Amma Rut ta amsa, “Kada ki roƙe ni in bar ki ko in koma daga gare ki. Inda za ki, zan tafi, kuma inda za ki zauna, zan zauna. Mutanenki, za su zama mutanena kuma Allahnki, zai zama Allahna.
And Ruth said—Do not urge me to leave thee, to go back from following thee, —for, whither thou goest, I will go, and, where thou lodgest, I will lodge, thy people, shall be my people, and, thy God, my God;
17 Inda za ki mutu zan mutu, zan mutu a can kuma za a binne ni. Bari Ubangiji ya hukunta ni da tsanani sosai, in wani abu in ba mutuwa ce ta raba ke da ni ba.”
where thou diest, I will die, and, there, will I be buried: So, let Yahweh do to me, and, so, let him add, if, death itself, part me and thee.
18 Sa’ad da Na’omi ta gane cewa Rut ta ƙudura tă tafi tare da ita, sai ta daina nema tă koma.
And, when she saw that, bravely determined, was she to go with her, she ceased entreating her.
19 Saboda haka matan biyu suka ci gaba da tafiya sai da suka isa Betlehem. Da suka isa Betlehem, sai dukan garin ya ruɗe saboda su, matan kuwa suka ce, “Na’omi ce wannan kuwa?”
So, they two, went their way, until they entered Bethlehem. And it came to pass, when they entered Bethlehem, that all the city was moved concerning them, and the women said—Is this Naomi?
20 Ta ce musu, “Kada ku kira ni Na’omi. Ku kira ni Mara gama Maɗaukaki ya sa raina ya yi ɗaci sosai.
And she said unto them, Do not call me Naomi ["Sweet"], —call me Mara ["Bitter"], for the Almighty hath dealt very bitterly with me:
21 In tafi cikakke, amma Ubangiji ya dawo da ni ba kome. Don me kuke kirana Na’omi? Ubangiji ya wahalshe ni, Maɗaukaki ya kawo mini masifa.”
I was full when I departed, but, empty, am I brought back of Yahweh, —wherefore should ye call me Naomi, when, Yahweh, hath given answer against me, and, the Almighty, hath crushed me?
22 Na’omi fa ta koma daga Mowab tare da Rut mutuniyar Mowab, surukarta, suka kai Betlehem a lokacin da ake fara girbin sha’ir.
So Naomi returned, and Ruth the Moabitess, her daughter-in-law, with her, who returned out of the country of Moab, —and, they, entered Bethlehem in the beginning of barley harvest.

< Rut 1 >