< Romawa 5 >
1 Saboda haka, da yake an same mu marasa laifi ta wurin bangaskiya, muna da salama tare da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi,
Since we stand justified as the result of faith, let us continue to enjoy the peace we have with God through our Lord Jesus Christ.
2 ta wurinsa ne muka sami shiga wannan alherin da muke tsaye yanzu, ta wurin bangaskiya. Muna kuma farin ciki a begen ɗaukakar Allah.
Through him also we have had our access into this grace in which we have taken our stand, and are exulting in hope of the glory of God.
3 Ba haka kawai ba, amma muna kuma da farin ciki cikin shan wuyanmu, gama mun san cewa shan wuyan nan takan haifi jimiri;
And not only so, but we are actually exulting also even in our troubles; for we know that trouble works fortitude,
4 jimiri kuma yakan kawo hali mai kyau; hali mai kyau kuma yakan sa bege.
and fortitude character, and character, hope -
5 Bege kuwa ba ya ba mu kunya, domin Allah ya zuba ƙaunarsa a zukatanmu ta wurin Ruhu Mai Tsarkin da ya ba mu.
a hope which never disappoints us. For through the Holy Spirit who has given to us, the "brimming river of the love of God" has overflowed in our hearts.
6 Kun ga, a daidai lokaci, yayinda muke marasa ƙarfi, Kiristi ya mutu saboda waɗanda ba su san Allah ba.
For while we were still without strength, Christ died in due time for the ungodly.
7 Da ƙyar wani yă mutu saboda mai adalci, ko da yake saboda mutumin kirki wani zai iya ƙarfin hali yă mutu.
Why, a man will hardly give his life for another, even for a righteous man, though perchance for a good man one might even take it upon himself to die.
8 Amma Allah ya nuna mana ƙaunarsa a wannan. Tun muna masu zunubi tukuna, Kiristi ya mutu dominmu.
But God gives proof of his love to us by the fact that while we were still sinners, Christ died for us.
9 Da yake yanzu mun sami zama marasa laifi ta wurin jininsa, ashe kuwa za a cece mu daga fushin Allah ta wurinsa!
By how much more, then, being now justified in his blood, shall we be saved through him from the wrath of God.
10 Gama in kuwa, sa’ad da muke abokan gāban Allah, aka sulhunta mu da shi ta wurin mutuwar Ɗansa, ashe, da yake an sulhunta mu, za mu sami ceto ta wurin ransa!
For if, when we were God’s enemies, we were reconciled to him through the death of his Son, how much more, now that we are reconciled, shall we be saved in his life.
11 Ba ma haka yake kawai ba, har muna farin ciki da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa yanzu muka sami sulhu.
And not only that, but we exult in God through our Lord Jesus Christ, through whom we have now obtained our reconciliation.
12 Saboda haka, kamar yadda zunubi ya shigo duniya ta wurin mutum ɗaya, mutuwa kuma ta wurin zunubi, ta haka kuwa mutuwa ta shafi dukan mutane, domin dukan mutane sun yi zunubi.
Thus, then, sin came into the world through one man, and through sin came death and so death spread to all men, because all had sinned.
13 Gama kafin a ba da doka, zunubi yana nan a duniya. Amma ba a lissafin zunubi inda babu doka.
For prior to the Law, sin actually existed in the world, but sin was not set down to man’s account when there was no law.
14 Duk da haka, mutuwa ta yi mulki tun Adamu har yă zuwa Musa, ta yi mulki har ma a kan waɗanda ba su yi zunubi ta wurin taka umarni kamar yadda Adamu ya yi ba. A wata hanya dai Adamu shi ne kwatancin wani mutumin nan mai zuwa.
Nevertheless, from Adam to Moses death reigned as king, even over those who had not sinned after the likeness of Adam’s transgression. Now Adam is a type of Him who was to come.
15 Amma kyautan nan dabam take da laifin nan. Gama in mutane da yawa sun mutu saboda laifin mutum ɗayan nan, to, ai, alherin Allah da kuma kyautan nan mai zuwa ta wurin alherin mutum ɗayan nan, Yesu Kiristi, ya shafi mutane da yawa!
But the free gift is not like the transgression; for if through the transgression of that one man the rest on men died, much more did the grace of God and the gift given in his grace in the one Man, Jesus Christ, overflow unto the rest of men.
16 Kyautar Allah kuwa ba kamar sakamakon da ya bi zunubin mutum gudan nan ba ne, Hukuncin ya bi zunubin mutum gudan nan, ya kuma kawo hallaka, amma kyautar ta bi laifofin masu yawa ta kuma sa Allah ya gan mu a matsayin marasa laifi.
And it is not with the free gift as it was through the one that sinned; for the judgment came from one transgression unto condemnation; but the free gift came from many transgressions unto acquittal.
17 Gama in, ta wurin laifin mutum ɗaya, mutuwa ta yi mulki ta wurin mutum ɗayan nan, ashe, waɗanda suka sami kyautar alherin Allah a yalwace da kuma kyautar adalci za su yi mulki a wannan rayuwa ta wurin mutum ɗayan nan, Yesu Kiristi.
For if through the transgression of the one, death reigned as king through the one, much more shall those who receive the overflowing grace and gift of righteousness reign as kings in life through One, through Jesus Christ.
18 Saboda haka, kamar yadda sakamakon laifin mutum guda ya jawo hallaka ga dukan mutane, haka ma sakamakon aikin adalci guda ya sa Allah ya same mu marasa laifi, wannan kuwa kawo rai ga dukan mutane.
It follows then, as through the transgression of one man came condemnation unto all men, even so through the act of righteousness of One came acquittal and life to all men.
19 Gama kamar yadda ta wurin rashin biyayyar mutum guda, mutane masu yawa suka zama masu zunubi, haka kuma ta wurin biyayyar mutum guda, mutane da yawa za su zama masu adalci.
For just as through the disobedience of one man the rest were made sinners; even so by the obedience of One shall all the rest be made righteous.
20 An ba da dokar don mu ga yadda laifi yake da girma. Amma da zunubi ya ƙaru, sai alheri ya ƙaru sosai,
Now law was brought in so that transgression might abound; but where sin abounded, grace super-abounded;
21 domin, kamar yadda zunubi ya yi mulki cikin mutuwa, haka ma alheri yă yi mulki ta wurin adalci yă kuwa kawo rai madawwami ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu. (aiōnios )
in order that as sin has ruled as king in death, so also grace might rule as king in righteousness which issues in eternal life, through Jesus Christ our Lord, - ours! (aiōnios )