< Ayyukan Manzanni 1 >

1 A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
My first account, O Theophilus, dealt with all that Jesus began doing and teaching from the beginning down to the day when,
2 har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
after giving instructions through the Spirit to the apostles whom he had chosen, he was taken up to heaven.
3 Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
After his sufferings he had also shown himself alive to them in many convincing manifestations, revealing himself to them during forty days, and speaking of the kingdom of God.
4 A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
And once when he was eating with them he charged them not to depart from Jerusalem, but to wait for the promise of the Father. "Of this," he said, "you have heard from me.
5 Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
"For John indeed baptized in water, but you shall be baptized in the Holy Spirit not many days hence."
6 Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
So, when they came together, they began to ask him, "Master, are you at this time about to restore the kingdom of Israel?"
7 Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
He answered. "It is not for you to know times and occasions which the Father has fixed in his own authority;
8 Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
"yet you will receive power when the Holy Spirit comes upon you, and you are to be my witnesses both in Jerusalem and in all Judea, and in Samaria, and to the very ends of the earth."
9 Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
When he had said this, and while they were looking at him, he was lifted up, and a cloud received him up out of their sight.
10 Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
While they were gazing into the sky as he was going up, suddenly there were two men in white garments standing by them,
11 Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
and they said. "Men of Galilee, why do you stand gazing into the sky? This same Jesus who has been taken up from you into the sky will come back in just the same way as you have seen him going into the sky."
12 Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
Then they returned to Jerusalem from the mountain called Olivet, which is near Jerusalem, about a Sabbath Day’s journey distant.
13 Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
On entering the city they went to the upper room where they were accustomed to meet. They were Peter and John and James and Andrew, Philip and Thomas, Bartholomew and Matthew, James, son of Alphaeus, and Simon the Zealot, and Judas the son of James.
14 Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
These all with one mind gave their constant attention to prayer, together with some women, and with Mary the mother of Jesus, and his brothers.
15 A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
It was during these days that Peter stood up among the brothers - the whole number of persons present was about one hundred and twenty - and said.
16 ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
"Men and brothers, it was necessary for the Scripture to be fulfilled which the Holy Spirit uttered beforehand by the lips of David in regard to Judas who acted as guide to those who arrested Jesus.
17 dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
"For he was numbered among us, and he did get his allotted share of this ministry.
18 (Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
"Now this man bought a plot of ground with the price of his treachery, and falling there headlong he burst asunder and all his bowels gushed out.
19 Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
"This fact became known to the people of Jerusalem so that the place was called in their language, Acheldamach, The Field of Blood.
20 Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
"For it is written in the Book of Psalms, Let his dwelling-place be desolate; Let no man dwell there, also, Let another take his work.
21 Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
"It is necessary then that, of the men who have been associated with us during the whole time in which the Lord Jesus went in and out among us,
22 farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
from his baptism by John down to the day on which he was taken up from us, one should join us a witness to his resurrection."
23 Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
So they placed two in nomination, Joseph called Bar-Sabbas (surnamed Justas) and Matthias;
24 Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
and they prayed, saying. "Thou, O Lord, who knowest the hearts of all men, show clearly which of these two men thou hast chosen to fill the place
25 ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
"in this ministry of this apostles from which Judas went out to go to his own place."
26 Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.
Then they cast lots for them, and the lot fell upon Matthias, and he was numbered with the eleven apostles.

< Ayyukan Manzanni 1 >